Amintacciya Company

Amintacciya Company Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Amintacciya Company, Media/News Company, Kano.

Kun san wani Shehi da aketa hayaniya an k**a shi to naji labarin an k**ashi ne saboda kwanaki an bashi biliyan 1 don yay...
04/01/2026

Kun san wani Shehi da aketa hayaniya an k**a shi to naji labarin an k**ashi ne saboda kwanaki an bashi biliyan 1 don yayi tsafi a yi nasarar yiwa Tinubu juyin Mulki, shine aka k**a shi

inji Malam Lawan Triumph

Malamin Addinin Islama, Sheikh Lawal Triumph ya bayyana cewa Biliyan 1 ce aka baiwa wani Shehi akan ayi tsafi dan a yi nasarar yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu juyin Mulki.

Yace dalili kenan da yasa aka k**ashi.

Malam yace yasan da hakane ta hanyar kiran waya jihar da Abinda ya faru, watau, inda aka bashi wannan labari.

Duk da yake malam bai bayyana sunan malamin da yake nufi ba, da yawa wasu sun fassara cewa, da malam Sheikh Khalifa Sani Zaria yake.

Yace irin wannan abinne ba za’a taba ganin dan Izala a ciki ba, sai dai wasu yan Comment a Videon Malam Lawan Triumph sun zarge shi da yada labarin da bai sani ba kawai dan ya kira waya sai kuma ya yarda

Meye Ra'ayin ku?

GWANIN SHA'AWA: Ana ta Aure kafin December ta wuce musamman yadda sanyi ya fara yin Sallah Shin kana cikin masu burin yi...
02/12/2025

GWANIN SHA'AWA: Ana ta Aure kafin December ta wuce musamman yadda sanyi ya fara yin Sallah

Shin kana cikin masu burin yin Aure a wannan shekarar ?

30/11/2025

24/11/2025

Adam A Zango Ali Nuhu Mohammed Abdallah Amdaz

Lokacin da nake Jami’a (kafun a kore ni) akwai wani abokin Gwagwarmayan mu (bana son inyi tagging din shi amma ze ga wan...
24/11/2025

Lokacin da nake Jami’a (kafun a kore ni) akwai wani abokin Gwagwarmayan mu (bana son inyi tagging din shi amma ze ga wannan rubutun) yayi broke se yake fadawa wani abokin shi bakano yana bukatar Emergency N50,000 ya biya kudin makaranta sannan yayi wani lalura be ma san ta ina ze fara ba, Abokin yace masa shi be san inda zaa samo N50k ba, Amma dai yana da numban wayan Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, bari ya bashi kila ya dace!

Ya karbi lambar kwankwaso ya zauna ya tsara masa Text message cewa shi bakano ne, yana Jami’ar ABU yana neman wani opportunity a wata kasa an kirashi visa interview a Abuja kuma bayi da ko sisi da ze je Abuja, be da masauki b***e guzuri, ya rubuta masa cewa Interview din zaayi nan da sati 3.

Shi dai kawai ya tura text ne ba wai don yana sa rai da wani abu ba!

Kwatsam, bayan kwana 17 yana kwance aka kirashi da sassafe da wata lamba, kai ne wane? Yace eh, kana da jarabawa ranar kaza (har ya ma manta saboda kasan halin karya) be gane mene ake fadi a waya ba, se da me kiran yace masa ba kai ne kayiwa Sen Kwankwaso message ba? Se yayi zumbur ya miqe, yace masa ai ya dauka yan damfara ne!

Aka fada masa anyi masa booking hotel kaza a Abuja na kwana 5, zasu bashi Abinchi kullum sau uku, sannan Sen. Yace a bashi N250,000 yayi kudin mota yazo ya koma, sannan yayi zirga zirga a Abuja, Idan kuma akwai wani matsala ko taimakon da yake bukata, ya kira wannan da ya kirashi! A karshe yace ya koma numban Sen yayi masa Godia kuma ya fada masa yadda s**ayi a text kawai ze gani In sha Allah.

Ya tashi ya tafi Abuja, ya sha barcin shi na kwana 5 a hotel, ya karbo N250k din shi ya biya kudin makaranta, ya siya waya, ya dinka sabbin kaya ya dawo Zaria abun sa!

Har yau, Kwankwaso beyi replying message din sa ba, be san shi ko dan gidan waye bane, kuma be nemi ya sani ba, kawai dai yaga message an ce bakano ne, kuma ana neman kudin makaranta!

Da ace wani dan siyasar ne, abunda zaa fara dubawa shine: sau nawa yake posting Alheri ne, kuma a rana sau nawa yake yabon sa Idan aka gama vetting din sa aka ga he’s clean kuma yana posting kullum , sannan se a tura masa N30,000

Daga Elhassan Kauran Mata

24/11/2025

Shugaban APC na ziyartar sa shugabannin ADC na neman sa, wato Dr Isa Ali Pantami Da alamu dai ADC Naso ya kasance da ita...
28/09/2025

Shugaban APC na ziyartar sa shugabannin ADC na neman sa, wato Dr Isa Ali Pantami

Da alamu dai ADC Naso ya kasance da ita yayi da APC basa so ya barsu

Yanzu dai yanayin ya nuna Malam zai iya yin Takara in bai samu a APC yai a ADC

Shin kuna goyon bayan Sheikh Isa Ali Pantami ya zama Gwamna a jihar Gombe?

ALHAMDULILLAHALHAMDULILLAH ALHAMDULILLAH Yau kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, yake cika shekaru biyu cif-cif da budewa.  ...
16/09/2025

ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
Yau kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD, yake cika shekaru biyu cif-cif da budewa.

Da mutane 3 muka fara bude kamfanin, amma zuwa yau muna da ma'aikatan din-din-din su 17 da suke zaune a babban Ofis din kamfanin dake cikin kwaryar jihar Gombe, wasu daga cikin ma'aikatan sun fito daga sassan jihohin Arewa ne, akwai mutane biyu da basu cikin wa 'yan nan hotunan.

Bayan wa 'yan nan ma'aikatan dake zaune a ofis, muna da ma'aikata su 37 da suke da albashi a kowane watan duniya, da suke aiki daga gida.

Jimillar ma'aikatanmu na kamfani bangaren Data su 54 ne suke da albashi a kowane wata, bayansu akwai ma'aikatan wucin gadi bamu saka su cikin lissafi ba.

Cikin shekaru biyun nan Allah ne kadai yasan irin tarin nasarorin da muka cimmawa. Na dade ina fada ba nida burin da ya wuce naga daruruwan matasa suna aiki a wannan kamfanin nawa da sauran harkokinmu na kasuwanci.

Muna da Data masu yawa kowace da farashinta akwai masu sauki da masu tsada sai wacce mutum ya zaba. Kaya mai kyau baya tsada ABBA PANTAMI DATA LTD suna da customer care da kayi korafi kan wata matsala nan take za'a gyara maka.

Hakika muna matukar godiya ga dukkannin kwastomominmu da s**a taba yi mana cinaki, kuma muna matukar alfahari dasu.

Babu taimakon da zaka yi mana wanda ya wuce kayi mana cinaki ka taimakemu a bangaren kasuwancinmu. Mungode.

CEO ABBA PANTAMI DATA LTD

Abin dariya 😂😂😂
14/09/2025

Abin dariya 😂😂😂

10/09/2025

Allah yasa mu dace

Gwamnatin Jihar Adamawa ta tabbatar da mutuwar mutane takwas (8) sak**akon zargin barkewar Buruli Ulcer a garin Malabu, ...
10/09/2025

Gwamnatin Jihar Adamawa ta tabbatar da mutuwar mutane takwas (8) sak**akon zargin barkewar Buruli Ulcer a garin Malabu, karamar hukumar Fufore.

Wannan cuta ta Buruli ulcer cuta ce da ƙwayar Mycobacterium ulcerans ke jawowa, tana lalata fata da ƙashi idan ba a kula da ita da wuri ba.

Rahoton ya ce hukumomi sun tura ƙungiyar kiwon lafiya domin bincike da tallafa wa al’umma.

An kuma yi kira ga jama’a da su kai rahoton duk wani sabon al’amari ko alamar cutar domin a samu daukar matakin gaggawa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Amintacciya Company posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share