31/05/2026
KA JI RABO: Matashiyar ’yar Najeriya, Hafiza Sumayya, takammala haddace Alƙur’ani mai girma da dukkan riwayoyinsa, tare da manyan littattafan Ilimin Qira’ah kamar Ash-Shatibiyyah, Ad-Durrah da At-Tayyibah.
An yaba da kwarewarta wajen karatu da sauyawa tsakanin qira’o’i daban-daban cikin fasaha da kiyaye ka’idojin tajwidi, lamarin da ya sa mutane da dama ke kallonta a matsayin abin koyi ga masu neman ilimin Alƙur’ani.
Wane irin fata za ku yi musu?