CNN Hausa

CNN Hausa Jaridar CNN Hausa za ta dinga kawo muku labarai ingantattu masu kayatarwa. Muna karbar tallan kasuwanci ko na siyasa.
(1)

A tuntube mu a wannan lambar 08035996090 whatsapp kaɗai.

Wannan shi ne ƙabarin mahaifiyar Manzon Allah SAW Nana Aminatu. Allah ya ƙara mana ƙaunar Manzon Allah SAW.
30/10/2025

Wannan shi ne ƙabarin mahaifiyar Manzon Allah SAW Nana Aminatu. Allah ya ƙara mana ƙaunar Manzon Allah SAW.

YANZU-YANZU: Mun Sakar Muku Shirin KUDIRI EPISODE 6Ku ci gaba da kallon KUDIRI EPISODE 6 yanzu haka  a YouTube channel m...
30/10/2025

YANZU-YANZU: Mun Sakar Muku Shirin KUDIRI EPISODE 6

Ku ci gaba da kallon KUDIRI EPISODE 6 yanzu haka a YouTube channel mai suna "Kannwood Exclusive TV"

Kudiri Labari ne mai dauke da mabambantan darussan rayuwa, wanda idan ka fara kallonsa ba za ka daina ba.

Kar ku bari a baku Labari.

Wannan shi ne ƙabarin Sayyada Aisha matar Manzon Allah SAW. Ƙabarin nata yana maƙabartar baƙi'a da ke birnin Madina. All...
30/10/2025

Wannan shi ne ƙabarin Sayyada Aisha matar Manzon Allah SAW. Ƙabarin nata yana maƙabartar baƙi'a da ke birnin Madina. Allah ya ƙara mata yarda.

ALLAHU AKBAR: Mutane Shida Ƴan Gida Ɗaya Sun Karɓi Addinin Musulunci A Kasar Japan.Allah ya tabbatar da su kan Musulunci...
30/10/2025

ALLAHU AKBAR: Mutane Shida Ƴan Gida Ɗaya Sun Karɓi Addinin Musulunci A Kasar Japan.

Allah ya tabbatar da su kan Musulunci da kuma sunnar Manzon Allah SAW ya albarkaci rayuwarsu.

Babu tauye ƴancin addini a Nijeriya, Cewar  Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNNMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alha...
29/10/2025

Babu tauye ƴancin addini a Nijeriya, Cewar Ministan Yaɗa Labarai a hirar CNN
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana ƙara maida hankali wajen magance matsalolin tsaro a ƙasar nan domin tabbatar da tsaro da walwalar ’yan ƙasa.

Da yake magana a cikin wata hira da gidan talbijin na CNN ya yi da shi a London a daren Talata, Idris ya ƙaryata iƙirarin da wasu jami’an ƙasashen waje suke yi cewa wai ’yan ta’adda a Nijeriya suna kai hare-hare ne kan Kiristoci kawai.

Ya bayyana cewa irin waɗannan iƙirari ba su da tushe kuma ba su bayyana haƙiƙanin yanayin tsaron ƙasar nan, inda ya jaddada cewa ’yancin yin addini yana cikin kundin tsarin mulkin Nijeriya.

Ya ce: “Wasu daga cikin iƙirarin da wasu jami’an Amurka s**a yi sun ta’allaƙa ne kan bayanai marasa inganci da kuma zato cewa yawancin waɗanda ake kai wa hare-hare Kiristoci ne. E, ana kai wa Kiristoci hari, amma waɗannan miyagun ba mabiya addini ɗaya kawai suke kai wa farmaki ba. Suna kai wa Kiristoci hari, suna kuma kai wa Musulmi hari, musamman a arewacin ƙasar.”

Idris ya ce masu yaɗa irin waɗannan labaran ƙaryar suna taimaka wa ’yan ta’addar ne, saboda manufar ’yan ta’adda ita ce su haddasa rikici tsakanin Musulmi da Kiristoci a ƙasar.

Ya ƙara da cewa Nijeriya ƙasa ce da ta yi yarda da bambancin addinai, don haka yaɗa labaran ƙarya na nuna rashin jituwa zai iya haifar da rarrabuwar kai.

Ya ce: “Kiran lamarin da cewa hare-haren kan Kiristoci ne kawai zai iya haifar da rarrabuwar kai a Nijeriya. Miyagun suna son a ɗauka kamar ana faɗa ne tsakanin Musulmi da Kiristoci. Mun shaida akwai hare-hare kan Kiristoci, kuma mun shaida akwai hare-hare kan Musulmi. Amma ba daidai ba ne a ce Nijeriya ƙasa ce da ba ta mutunta ’yancin addini, ko a ce ko'ina babu tsaro a Nijeriya. Nijeriya ƙasa ce mai aminci.”

Ministan ya amince cewa akwai matsalolin tsaro, amma kuma gwamnati tana ɗaukar matakai masu ƙarfi da tsari don magance su.

Ya bayyana cewa gwamnati ta ƙarfafa rundunonin tsaro tare da zuba jari a fannoni kamar noma da ayyukan jinƙai domin ƙarfafa zaman lafiya.

Ya ce: “Ko canje-canjen da aka yi na shugabannin hafsoshin tsaro kwanan nan duk don a ƙarfafa tsarin tsaron ƙasar ne, domin gwamnati ta iya magance kowace irin matsala a kan lokaci.”

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN: Allah ya karɓi ranta a wurin haihuwa bayan an yi mata tiyata.Ƴan'uwanta suna buƙata...
29/10/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN: Allah ya karɓi ranta a wurin haihuwa bayan an yi mata tiyata.

Ƴan'uwanta suna buƙatar addu'arku domin Allah ya yi mata rahama.

KYAKKYAWAN ƘARSHE: Wannan jami'in kwastam ɗin mai suna Muhammad Musa ya rasu ne a masallaci a yayin da yake yin sallah.A...
29/10/2025

KYAKKYAWAN ƘARSHE: Wannan jami'in kwastam ɗin mai suna Muhammad Musa ya rasu ne a masallaci a yayin da yake yin sallah.

Allah ya gafarta masa.

BABBAR MAGANA: Wallahi duk wanda ke zagin Shehu Tijjani sai ya yi mummunan ƙarshe kuma ba zai mutu da imani ba, Cewar Im...
29/10/2025

BABBAR MAGANA: Wallahi duk wanda ke zagin Shehu Tijjani sai ya yi mummunan ƙarshe kuma ba zai mutu da imani ba, Cewar Imam Junaidu Bauchi

Shahararren matashin malamin Tijjaniyya Sheikh Junaidu Abubakar Bauchi, ya bayyana cewar duk wanda ke zagin Shehu Tijjani ba zai mutu da imani ba, domin shi da kansa Shehu Tijjani ɗin ya ce duk wanda yake zaginsa kuma bai tuba ba to zai mutu kafiri.

Me za ku ce?

DA ƊUMI-ƊUMI: "Marigayi Buhari dattijon arziki ne, duk inda ake neman mutumin kirki salihi to Buhari ya kai, jajirtacce ...
28/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: "Marigayi Buhari dattijon arziki ne, duk inda ake neman mutumin kirki salihi to Buhari ya kai, jajirtacce ne mai gaskiya, nagarta, dattako da kishin ƙasa." Cewar Proudfessor Isa Ali Pantami "Ga*b*ti"

Masu magana na cewa ruwan da ya dake ka shi ne ruwa. Wannan shi ne Allah ya sa mu dace.

Me za ku ce?

Akwai Ayar Tambaya Kan Maƙudan Kuɗaɗen Da Matasan Ƴan Mata Na Cikinmu Ƴan Fim Ke Samu, Cewar Dattijo Husaini Sule ƘoƙiYa...
28/10/2025

Akwai Ayar Tambaya Kan Maƙudan Kuɗaɗen Da Matasan Ƴan Mata Na Cikinmu Ƴan Fim Ke Samu, Cewar Dattijo Husaini Sule Ƙoƙi

Ya ce: "Mu ne muka gina wannan masana’antar ta shirya finafinan da karfinmu domin isar da sako mai kyau tun lokacin daɓe, tun lokacin wasu ba a haifi iyayensu ba, iya bauta mun yi domin sana’ar ta samu karbuwa a kowanne sassa a faɗin kasar nan.

Amma yau an wayi gari saboda son mata irin na mutanenmu sai yarinya ta shigo masana’antar, gobe ka gan ta ta zama hamshakiya da babbar mota wannann yana mutukar ba ni mamaki ga shi yanzu film ɗin ma sai an ga dama ake saka mu a cikin wasu finafinan."

Me za ku ce?

ALLAHU AKBAR: Pastor ya karɓi addinin Musulunci bayan ya sha kayi a yayin da s**a yi muƙabala da wani Malamin addinin Mu...
27/10/2025

ALLAHU AKBAR: Pastor ya karɓi addinin Musulunci bayan ya sha kayi a yayin da s**a yi muƙabala da wani Malamin addinin Musulunci.

Paston ya sha ruwan hujjoji, da yake yana da buɗaɗɗiyar zuciya ta karɓar gaskiya sai ga shi ya karɓi Musulunci a wurin Malamin da s**a yi muƙabalar.

Allah ya tabbatar da shi kan addinin Musulunci da kuma sunnar Manzon Allah SAW ya albarkaci rayuwarsa.

ALLAHU AKBAR: Matasan Musulmai Ƴan Ƙabilar Igbo Sun Gina Katafaren Masallacin Juma'a A Garin Ibagwah Da Ke Jihar EnuguA ...
27/10/2025

ALLAHU AKBAR: Matasan Musulmai Ƴan Ƙabilar Igbo Sun Gina Katafaren Masallacin Juma'a A Garin Ibagwah Da Ke Jihar Enugu

A shekarar 2010, al’ummar Musulmi a garin ibagwa-Aka wanda ke da ɗaya daga cikin mafi yawan Musulman Igbo, sun fara wani gagarumin aiki don gina sabon babban masallaci. Tsohon masallacin Juma’a da ke yankin ya gaza ɗaukar yawan jama’a da ke ƙaruwa a kullum.

Matasan Musulman Igbo sun nuna sadaukarwa da aiki tukuku. Ya kamata a yaba da irin wannan aiki da al’ummar Musulmi s**a yi a "Ibagwa-Aka, Nsukka" da kewaye. Wannan gini ba kawai masallaci ba ne — alama ce ta haɗin kai, sabo da girmama addini

*Allah Ya saka da alheri, Ya karfafa imaninsu, Ya kuma kara musu ci gaba.

Address

B. U. K Road
Kano
700301

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when CNN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to CNN Hausa:

Share