CNN Hausa

CNN Hausa Jaridar CNN Hausa za ta dinga kawo muku labarai ingantattu masu kayatarwa. Muna karbar tallan kasuwanci ko na siyasa. A tuntube mu kira ko whatsapp 08035996090

Ƙarshen Tika-Tika-Tik: An binne tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura~Zinariya
15/07/2025

Ƙarshen Tika-Tika-Tik: An binne tsohon shugaban ƙasar Najeriya Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura

~Zinariya

Yadda ake girmama gawar Shugaba Muhammadu Buhari bayan saukarta Daga jirgi.
15/07/2025

Yadda ake girmama gawar Shugaba Muhammadu Buhari bayan saukarta Daga jirgi.

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – MinistaMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Moha...
11/07/2025

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, yana da cikakken ƙudiri na tabbatar da ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi domin zurfafa dimokiraɗiyya da kuma hanzarta cigaba a matakin ƙasa.

Ministan ya bayyana haka ne a Abuja a ranar Juma’a, lokacin da ya karɓi tawagar Ƙungiyar Tsofaffin Kansiloli ta Ƙasa wadda ta kai masa ziyarar ban-girma a ofishin sa.

Ya ce: “Ƙananan hukumomi su ne mataki na uku na gwamnati kuma su ne s**a fi kusa da jama’a. Shi ya sa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu cikin hikimar sa ya sake duba batun ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi."

Ya tunatar da cewa a bara, Antoni-Janar na Ƙasa kuma Ministan Shari’a ya nemi fassarar doka daga Kotun Ƙoli, inda kotun ta tabbatar da cewa kundin tsarin mulki ya tanadi ’yancin cin gashin kai ga ƙananan hukumomi.

“An samu hukunci daga babbar kotun ƙasa da ke nuna cewa kundin tsarin mulkin mu ya tanadi buƙatar ƙananan hukumomi su samu ’yancin kai – su kasance masu cikakken iko da damar aiki a fannoni daban-daban, ko siyasa ko kuma kuɗi,” inji shi.

A cewar sa, bai wa ƙananan hukumomi dama za ta ƙarfafa dimokiraɗiyya a matakin ƙasa da kuma samar da cigaba a cikin al’umma.

Idris ya nuna damuwa kan yadda tsarin ƙananan hukumomi ya raunana a tsawon lokaci, yana nuni da cewa tsarin ya sha bamban da yadda aka tsara shi tun farko.

“Tsawon shekaru, mun shaida yadda ƙarfin ikon ƙananan hukumomi yake ci gaba da raguwa fiye da yadda kundin tsarin mulki ya tanada,” inji shi.

Ya ƙara da cewa Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda gwani ne wajen kare dimokiraɗiyya, yana da tabbacin cewa ƙarfafa wannan mataki na gwamnati yana da matuƙar muhimmanci domin cigaban dimokiraɗiyya a ƙasar nan.

“Shugaban Ƙasa ɗan dimokiraɗiyya ne na gaske, kuma yana ganin cewa domin dimokiraɗiyyar mu ta kai inda muke fata, dole ne a ƙarfafa wannan mataki na gwamnati,” inji shi.

Ya buƙaci gwamnoni da su mara wa ƙoƙ

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Na Samar da Damarmakin Cigaba — Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai...
10/07/2025

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Na Samar da Damarmakin Cigaba — Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana samar da damarmaki na cigaban ƙasa a fannoni daban-daban na tattalin arzikin Nijeriya.

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a Minna, Jihar Neja, yayin taron Kwamishinonin Yaɗa Labarai daga jihohin da jam’iyyar APC take mulki, wanda Ƙungiyar Gwamnonin APC ta shirya don ƙarfafa dabarun sadarwa da haɗin gwiwa tsakanin matakai daban-daban na gwamnati.

Ya ce: “Shirin Sabunta Fata ya wuce sauye-sauyen tattalin arzikin ƙasa gaba ɗaya. Magana ce ta samar da damarmakin cigaban ƙasa a fannoni daban-daban – ga mutum ɗaya, ga iyalai, da kuma ga al’umma gaba ɗaya.”

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu tana aiwatar da shirye-shirye masu ɗaukar hankali ta hanyar manyan ayyukan gine-gine, shirye-shiryen tallafa wa matasa, da kuma sauye-sauye a fannonin noma, mak**ashi, ilimi da ƙere-ƙere.

Ministan ya bayyana cire tallafin fetur a matsayin ɗaya daga cikin manyan matakan da gwamnatin ta ɗauka domin farfaɗo da tattalin arziki.

Ya ce: “Ɗaya daga cikin manya kuma mafi tasiri daga cikin matakan da wannan gwamnati ta ɗauka shi ne cire tallafin fetur, wanda ko da yake ya kasance mai raɗaɗi, amma sauyi ne da ya zama dole. Bayan ceton tattalin arzikin ƙasa daga rugujewa, wannan mataki ya hana ɓarna da asarar kuɗi sosai a tattalin arzikin mu.”

A cewar sa, kuɗaɗen da aka ceto daga cire tallafin ana amfani da su ne wajen manyan ayyukan raya ƙasa irin su hanyar Legas zuwa Kalaba, hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, shimfiɗa layin dogo na Kaduna zuwa Kano, da sake gina hanyar mota ta Abuja zuwa Kaduna da Kano.

Ya ƙara da cewa akwai cigaba da aka samu wajen saka hannun jari a fannin ayyukan jin daɗi a faɗin ƙasar nan, tare da ƙaruwa a cikin kuɗaɗen da ake tura wa jihohi a kowane wata, wanda ke ba su damar aiwatar da ayyuka masu tasiri a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

Da

DA DUMI-DUMI: Wani bawan Allah da ya sayi buhun masara buhu dubu ɗaya a farashin 67k kowane buhu, ya nemi duk me son kar...
07/07/2025

DA DUMI-DUMI: Wani bawan Allah da ya sayi buhun masara buhu dubu ɗaya a farashin 67k kowane buhu, ya nemi duk me son karɓar bashin masarar ko buhu nawa ne a farashin 70k zai bayar amma akwai sharuɗa da ƙa'idoji. Me so zai iya tuntuɓar Abbas Ismail Yar'adua a nan facebook.

A yanzu haka dai buhun masara farashinsa naira 42k ne a kasuwa. A ƙarshe ya nemi jama'a da su saka shi cikin addu'o'insu.

Wane fata za ku yi masa?

TALLAH: Ku sayi DATA mai inganci a farashi mai sauƙi a kamfanin ASPVTU, muna siyar da katin waya shi ma a farashi mai sauƙi.

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar ASPVTU a PlayStore.
👇🏽👇🏽👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.aspvtu.app

Website
👇🏽👇🏽👇🏽
https://app.aspvtu.com

WhatsApp
👇🏽👇🏽👇🏽
https://wa.me/+2348104234299

Wannan ita ce raudar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Allah ka ba mu ikon ziyararta. Allah ya ƙara mana ƙaunar S...
07/07/2025

Wannan ita ce raudar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Allah ka ba mu ikon ziyararta. Allah ya ƙara mana ƙaunar Shugaba ya sa muna cikin cetonsa a gobe ƙiyama.

Wannan ita ce gonar ɗaya daga cikin sahabban Manzon Allah SAW Salmanul Farisi da ke birnin Madina| Allah ya ƙara wa Anna...
06/07/2025

Wannan ita ce gonar ɗaya daga cikin sahabban Manzon Allah SAW Salmanul Farisi da ke birnin Madina| Allah ya ƙara wa Annabi daraja.

TALLAH: Ku sayi DATA mai inganci a farashi mai sauƙi a kamfanin ASPVTU, muna siyar da katin waya shi ma a farashi mai sauƙi.

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar ASPVTU a PlayStore.
👇🏽👇🏽👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.aspvtu.app

Website
👇🏽👇🏽👇🏽
https://app.aspvtu.com

WhatsApp
👇🏽👇🏽👇🏽
https://wa.me/+2348104234299

ALLAHU AKBAR: Jarumar Finafinan Hollywood Lily Jay ƴar asalin ƙasar Austaraliya daga jihar Queensland ta karɓi addinin M...
05/07/2025

ALLAHU AKBAR: Jarumar Finafinan Hollywood Lily Jay ƴar asalin ƙasar Austaraliya daga jihar Queensland ta karɓi addinin Musulunci. Jarumar ta ce shigarta musulunci ya sauya mata rayuwa, inda ta wallafa wani saƙo a tiktok mai taken" a Shahada experience that changed my life" an gan ta a Tiktok tana furta kalmar shahada tare da bayyana yadda zuciyarta ta cika da farin ciki da ƙwalla.

Allah ya ƙara ɗaukaka musulunci.

TALLAH: Ku sayi DATA mai inganci a farashi mai sauƙi a kamfanin ASPVTU, muna siyar da katin waya shi ma a farashi mai sauƙi.

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar ASPVTU a PlayStore.
👇🏽👇🏽👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.aspvtu.app

Website
👇🏽👇🏽👇🏽
https://app.aspvtu.com

WhatsApp
👇🏽👇🏽👇🏽
https://wa.me/+2348104234299

ALLAHU AKBAR: A daidai wannan wurin da kuke gani Manzon Allah SAW ya ɗaure raƙuminsa ranar da aka yi yaƙin Badar. Allah ...
05/07/2025

ALLAHU AKBAR: A daidai wannan wurin da kuke gani Manzon Allah SAW ya ɗaure raƙuminsa ranar da aka yi yaƙin Badar. Allah ya ƙara mana ƙaunar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami'an Tsaro Sun Kashe 'Yan Ta'adda Sama Da 500 A Daren Jiya Alhamis A Jihar Zamfara, Tare Da Kwato Mak**...
04/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Jami'an Tsaro Sun Kashe 'Yan Ta'adda Sama Da 500 A Daren Jiya Alhamis A Jihar Zamfara, Tare Da Kwato Mak**ansu Da Mashina Sama Da 200

Sojojin Najeriya sun hallaka 'yan bindigan fiye da Dari biyar tare da k**a wasu da rai tsakanin dajin Anka, Bukkuyum da Gummi a jihar Zamfara, tare da karbar baburan da suke kai hare-hare ga al'ummar da ba su ji ba su gani ba.

YANZU-YANZU: Al'ummar Gari Sun Yi Kukan Kura Sun Auka Wa Barayin Waya A Kano.Barayin waya kenan da aka k**a a titin na'i...
04/07/2025

YANZU-YANZU: Al'ummar Gari Sun Yi Kukan Kura Sun Auka Wa Barayin Waya A Kano.

Barayin waya kenan da aka k**a a titin na'ibawa 'yan katako Kano an kone babur dinsu mai kafa biyu su kuma sun sha dúka a wurin jama'ar gari.

TALLAH: Ku sayi DATA mai inganci a farashi mai sauƙi a kamfanin ASPVTU, muna siyar da katin waya shi ma a farashi mai sauƙi.

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar ASPVTU a PlayStore.
👇🏽👇🏽👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.aspvtu.app

Website
👇🏽👇🏽👇🏽
https://app.aspvtu.com

WhatsApp
👇🏽👇🏽👇🏽
https://wa.me/+2348104234299

ALLAHU AKBAR: Wannan wajen da kuke gani mai alamar ja da ke jikin hoton nan, shi ne wajen da Manzon Allah Sallallahu Ala...
04/07/2025

ALLAHU AKBAR: Wannan wajen da kuke gani mai alamar ja da ke jikin hoton nan, shi ne wajen da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam ya yi sallah a cikin Ka'aba yayin da nusulmai s**a karɓi Makkah daga wajen ƙuraishawa. Allah ya ƙara wa Annabi daraja

TALLAH: Ku sayi DATA mai inganci a farashi mai sauƙi a kamfanin ASPVTU, muna siyar da katin waya shi ma a farashi mai sauƙi.

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar ASPVTU a PlayStore.
👇🏽👇🏽👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.aspvtu.app

Website
👇🏽👇🏽👇🏽
https://app.aspvtu.com

WhatsApp
👇🏽👇🏽👇🏽
https://wa.me/+2348104234299

Address


Telephone

+2349122994000

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when CNN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to CNN Hausa:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share