CNN Hausa

CNN Hausa Jaridar CNN Hausa za ta dinga kawo muku labarai ingantattu masu kayatarwa. Muna karbar tallan kasuwanci ko na siyasa.

A tuntube mu a wannan lambar 08035996090 whatsapp kaɗai.

Ƙungiyar Matasan Arewa ta nemi a ɗauki mataki akan Sanata Shehu Buba kan zargin sa da hannu a ta'addanciƘungiyar Ci-gaba...
06/09/2025

Ƙungiyar Matasan Arewa ta nemi a ɗauki mataki akan Sanata Shehu Buba kan zargin sa da hannu a ta'addanci

Ƙungiyar Ci-gaban Matasan Arewa AYM, ta kirayi Sufeto-Janar na ƴan sanda (IGP) da ya gaggauta ɗaukar matakin doka akan Sanatan Bauchi ta Kudu, Shehu Umar Buba, bisa zargin sa da tallafa wa ayyukan ta'addanci a garuruwan Arewacin Nijeriya.

A wata takarda da ke ɗauke da sanya hannun Kakakinta, Kwamared Yahaya Muhammed Garba, AYM ta bayyana kaɗuwarta game da ƙamarin ayyukan ta'addanci da ke ƙoƙarin mamaye shiyyar ganin yadda ake rasa rayukan waɗanda ba su ji ba ba su gani ba a kullum.

Ta ce, ƙalubalen da al'umma ke fuskanta a sanadiyyar ayyukan ƴan bindiga da ɓarayin daji na garkuwa da ta'addanci akan dukiyoyinsu ya zama ruwan dare a sassan jihohin ƙasar, lamarin da ya ɗaiɗaita mutane da dama daga muhallansu da jefa su cikin tsoro.

A cewarta, hakan ya yi mummunan tasiri ga haɗin kan al'umma da tattalin arziƙi, wanda ya jefa iyalai da dama cikin matsi akan matsin da suke fuskanta sakamakon taɓarɓarewar harkokin tattali a ƙasar.

Ta ƙara da cewa, ayyukan garkuwa da mutane da neman a biya kuɗaɗen fansa ya zama babban kasuwanci ga masu aikata manyan laifuka, saboda amfani da hakan wajen harin mutane da ɓangarorin daban-daban wanda ya zama sababin ɗaiɗaita dubunnan mutane da iyalansu.

Har'ilayau AYM ta yi tsokaci da jinjina akan matakan da Gwamnatin Tarayya ke ɗauka wajen ganin tsaro mai ɗorewa ya samu a shiyyar da suka haɗa da ƙara jami'an sojoji da ƴan sanda da sauransu a wuraren da ke fama da rashin tsaro.

Saidai, AYM ta bayyana ayyukan ire-iren Sanata Shehu Buba a matsayin abinda ka iya daƙile ƙoƙarin gwamnati na kawo ƙarshen matsalar.

A kwanan nan aka ga wani faifan bidiyo yana nuna kuɗaɗe da babura da aka tura daga gidan Sanatan zuwa wajen ƴan bindiga a Zamfara, lamarin da ke ƙoƙarin tabbatar da zargi akansa da hannu a ayyukan ta'addanci a shiyyar, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji Gwamnatin Tar...
05/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Jimamin Rasuwar Mutane A Nutsewar Jirgin Ruwa A Borgu, Ta Umurci NEMA Ta Kai Agaji

Gwamnatin Tarayya ta miƙa ta’aziyyar ta ga iyalan waɗanda suka rasa ran su a haɗarin jirgin ruwa da ya faru kwanan nan a yankin Borgu na Jihar Neja, wanda ya yi sanadin mutuwar kimanin mutum 32.

A wata sanarwa da ya fitar a yau, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan lamari a matsayin abin da “ya tayar da hankali.”

Ya ce: “Wannan ibtila’i ya yi matuƙar tayar da hankali, kasancewar ya faru ne cikin ƙasa da watanni huɗu bayan ambaliyar ruwa mai muni da ta afku a Mokwa, shi ma a Jihar Neja.

“Muna miƙa ta’aziyyar mu ta musamman ga iyalan waɗanda abin ya shafa, gwamnatin jihar da kuma al’ummar Neja. Jimamin mu da addu’o’in mu suna tare da duk wanda wannan ibtila’i ya shafa.”

Ministan ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) da ta samar da dukkan tallafi da ake buƙata ga iyalan waɗanda suka mutu da waɗanda suka tsira, tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin Jihar Neja domin tabbatar da gaggawar tallafi da taimako.

Haka kuma, gwamnatin ta umurci Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Ƙasa (NOA) da ta gudanar da babban kamfen na wayar da kai a faɗin ƙasar nan domin ƙara faɗakar da jama’a kan matakan tsaro yayin amfani da hanyoyin ruwa.

Idris ya yaba wa gwamnatin Jihar Neja, ta hannun Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha, bisa gaggawar gudanar da aikin ceto da ya tabbatar an tantance dukkan fasinjojin da ke cikin jirgin da ya yi hatsarin.

Ya ce: “Zan yi amfani da wannan dama in sake tunatar da jama’a da su riƙa bai wa batun tsaro muhimmanci yayin tafiya ta hanyoyin ruwa.

“Musamman, babu wanda ya kamata ya shiga tafiyar jirgin ruwa ba tare da sanya rigar kariya ta musamman ba. Matakan tsaro na iya ceton rayuka.”

Ya yi addu’ar samun rahamar Allah ga rayukan waɗanda suka salwanta tare da yi wa waɗanda suka tsira fatar samun lafiya cikin gaggawa.

‎DA DUMI DUMI: Kamfanin Dillacin Labarai na Bukuru TV/Radio na farin cikin sanar da Mutanen Arewacin Nijeriya da cewa ta...
05/09/2025

‎DA DUMI DUMI: Kamfanin Dillacin Labarai na Bukuru TV/Radio na farin cikin sanar da Mutanen Arewacin Nijeriya da cewa ta ci gaba da zaɓar Manyan Mutane a Arewacin Nijeriya don Basu Lambar yabo, a Wannan Karon ta Sake Zabo manyan Mutane uku a Arewacin Najeriya domin Karrama su da Lambar yabo mai Girma Kamar yadda ta Saba, Wadanda aka Zaba don Basu Lambar yabon ta Wannan Karon sun Hada da:

‎1-Prof. Isa Ali Ibrahim Pantami: lambar yabo ta karramawa bisa Gudummawar da ya bayar a fannin Ilimin fasaha da kirkire-kirkire da kuma harkan Da'awa.
‎2-Prof. Khalid Aliyu: Kyautar Nasarar Gagarumin Gudunmawa Akan Taimakon Ilimin Addinin Musulunci da Ilmantar ga Al'uma
‎3-Hon. Gwani Muhammad Adam Alkali: Lambar yabo ta karramawa bisa ga Irin gudunmawar da ya bayar wajen yi wa Al'umma hidima, Jagoranci da ci Gaban Al'umma.

‎Gidan Talabijin da Radiyon ta Bukuru Zai karrama su don Gudummawa sosai da Suka bayar a fannonin daban daban da kuma tasiri ga Rayuwar Al’umma a Arewacin Najeriya da ma Kasa Baki daya. Waɗannan lambobin yabo suna zama shaida ga ƙwazo da Sadaukarwa,


‎Engr.Lawan Lawan Suleiman.
‎Bukuru TV/Radio station
[email protected]

ALLAHU AKBAR: Sawun Annabi Muhammadu Manzon Allah (SAW) Na Daga Cikin Abubuwan Da Ake Girmamawa A Wasu Al’adun Musulunci...
05/09/2025

ALLAHU AKBAR: Sawun Annabi Muhammadu Manzon Allah (SAW) Na Daga Cikin Abubuwan Da Ake Girmamawa A Wasu Al’adun Musulunci, Musamman A Masar, Turkiyya, Da Indonesiya, Duk Da Cewa Addinin Islama Na Orthodox Bai Yarda Da Waɗannan Sawun Ba.

Kamar Irin Wadanda Aka Baje Kolin Kayayyakin Tarihi Na Fadar Topkapi Ko Kuma Masallacin Athar al-Nabi Da Ke Birnin Alkahira, Wasu Sun Yi Imanin Cewa An Samo Su Ne Daga Wani Dutse Da Manzon Allah Ya Taka.

04/09/2025

Azzaluman Shugabannin Nijeriya Sun Fi Abubakar Dan Damisa Sharri, Amma Me Ya Sa Da Suka Mutu Aka Dinga Yi Musu Addu'a Tare Da Fatan Alkhairi?

DA ƊUMI-ƊUMI: Sama Da Jiragen Ruwa 50 Daga Kasashe 44 Na Duniya Sun Tunkari Gaza Don Kai Tallafi. Wasu gungun ƴan gwagwa...
04/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Sama Da Jiragen Ruwa 50 Daga Kasashe 44 Na Duniya Sun Tunkari Gaza Don Kai Tallafi.

Wasu gungun ƴan gwagwarmaya daga sassan duniya, karkashin Gidauniyar Plotilla Global Sumud, wacce ta kunshi jiragen ruwa fiye da 50 daga ƙasashe 44 tare da masu fafutuka, na tunkarar Gaza da abinci, magunguna, da kayan tallafi.

Manufar wannan aiki ita ce don karya takunkumin da Isra’ila ta sanya wa Mutanen Gaza.

04/09/2025

Nagartacce, Jajirtacce, Ƙwararre, Mai Cikakkiyar Halitta Annabi Muhammadu Rasulullah ﷺ.
❤️❤️

SON ANNABI: Yadda aka gudanar da zagayen mauludi fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW) a garin Malam Madori na Jihar Ji...
04/09/2025

SON ANNABI: Yadda aka gudanar da zagayen mauludi fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW) a garin Malam Madori na Jihar Jigawa.

Allah ya ƙara wa Annabi daraja

SOYAYYAR ANNABI: Musulmai a garin Yauri da ke jihar Kebbi sun fito domin gudanar da bikin Maulidin Annabi Muhammad SAW.A...
04/09/2025

SOYAYYAR ANNABI: Musulmai a garin Yauri da ke jihar Kebbi sun fito domin gudanar da bikin Maulidin Annabi Muhammad SAW.

Allah ya ƙara wa Annabi daraja.

NA ANNABI YA CE AMIN: Allah Ya Jikan Shiekh Ja’afar Mahmud Adam Allah Ya Dauwamar Da Haske A Cikin KabarinsaAllah ya gaf...
04/09/2025

NA ANNABI YA CE AMIN: Allah Ya Jikan Shiekh Ja’afar Mahmud Adam Allah Ya Dauwamar Da Haske A Cikin Kabarinsa

Allah ya gafarta masa! Allah ya saka shi a Aljannatul Firdause.

Wato Mal Ja’afar ya bada gagarimin ci gaba a karantarwar Addinin Musulunci a Nijeriya da ma wasu kasashe a duniya.

Shi ne Malamin da za ka fahimce karatunsa duk rashin fahimtar mutum.

Allah ya saka masa ladan gudumuwar da ya bayar ga Addinin Musulunci.

Address

B.U.K Road
Kano
700301

Telephone

+2349122994000

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when CNN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to CNN Hausa:

Share