SGG TV

SGG TV This is an official page for SGG TV, It deals with the fact from genuine Source (s). Please join us and stay connected. 🙏

Tinubu ya naɗa Injiya Ramat a matsayin shugaban NERC da kuma Kwamishinonin hukumar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya na...
07/08/2025

Tinubu ya naɗa Injiya Ramat a matsayin shugaban NERC da kuma Kwamishinonin hukumar

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Injiniya Abdullahi Garba Ramat a matsayin sabon Shugaba kuma Babban Darakta na Hukumar Kula da Lantarki ta Ƙasa (NERC).

Injiniya Ramat, mai shekaru 39, ƙwararren injiniya ne a fannin lantarki kuma gogaggen mai gudanarwa, wanda ke da digiri na uku (PhD) a fannin Gudanarwa ta Dabaru da wasu ƙarin ƙwarewa.

Haka kuma, Shugaba Tinubu ya nada wasu kwamishinoni biyu domin aiki a hukumar NERC. Su ne Abubakar Yusuf a matsayin Kwamishinan Harkokin Masu Amfani da Wuta da Dr. Fouad Olayinka Animashun a matsayin Kwamishinan Kudi da Harkokin Gudanarwa.

Dukkan nade-naden suna jiran tantancewa da amincewar Majalisar Dattawa.

Sai dai, domin guje wa gibin shugabanci a wannan muhimmin bangare na gwamnati, Shugaba Tinubu ya bayar da umarnin cewa Injiniya Ramat ya fara aiki a matsayin mai riƙon ƙwarya kafin tantancewarsa, kamar yadda doka ta tanada.

Sanarwar nada jami’an ta fito ne daga mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga, a ranar Laraba, 7 ga Agusta, 2025.

An gudanar da Jana'izar Mal. Habibu Galadanchi,  Mahaifin Matashin Dan Gwagwarmaya nan Mai Suna Dan Bello Galadanchi.
07/08/2025

An gudanar da Jana'izar Mal. Habibu Galadanchi, Mahaifin Matashin Dan Gwagwarmaya nan Mai Suna Dan Bello Galadanchi.

Allah sarki Sadiq Gentle ya rasu ya koma ga Allah. Amma har yanzu na ga wasu sun kasa daukar darasin rayuwa akan mutuwar...
07/08/2025

Allah sarki Sadiq Gentle ya rasu ya koma ga Allah. Amma har yanzu na ga wasu sun kasa daukar darasin rayuwa akan mutuwar shi... 😭😭

Na sha fadin akwai matakin da zaka kai a social media dole ka zama BOYAYYEN mutum, wato duk wata alaka da zaku kulla da ko ma waye kar ta wuce Online din nan. Amma fa mai hangen nesa ne zai gane me nake nufi.... 😭😢👏

Wallahi tallahi duk kusancinka da mutum ko ma waye, kar kayi tunanin ba zai iya butulci maka ko ya cutar da kai ba. Na rantse da Allah ka saka a ranka iyayenka ne kawai ba zasu taba cin amanarka ba a duniyar nan...

Tabbas ya kamata muna kula da wanda zamu dinga mua'mala dasu wallahi akwaii wanda yana nan yana bibiya naka a kafar nan in kayi Post baya LIKE KO COMMENT amma wallahi jira yake ka ketare iyaka yayi amfani da damarsa ya kulle ka ko kuma yasa a kashe ka itace gaskiyar magana

Dukkan yan gwagwarmaya ya kamata suzauna suyiwa kansu wa'azi domin dukkan wanda muke karewa wallahi wannan rasuwar abokin mu Sadiq Gentle ta kara tona musu asiri chewa batamu suke ba nifa tunda na karye na dawo hayyaci na a harkar nan na gane yaseen majority makiyan mu muke tallatawa shawara ga yan gwagwarmaya itace

Ka kalli IYAYEN KA DA DANGIN KU ka rufawa kanka asiri kasan abinda zaka rubuta domin wallahi wajen kare muhibbar wannan mutanen zaka iya rasa ranka kuma wallahi ko gaisuwa bai zama dole suzo ba

Mutum yasan iyakarsa kayi rubutu daidai iyawar abinda zaka iya dauka domin wajen kare wani sakaraii zaka jawo Iyayen ka su shiga wahala kuma wallahi babu ruwansu kayi siyasa saffa saffa

Kalli daii hoton kasan nan mahaifiyar Sadiq Gentle ce gaban danta kafin allah ya dauki ransa sanadiyar wanda ake zargi dansu akaii masa haka kaga wani kusa dashi answer itace aa to kawai kayiwa kanka kiyamul laili ka rufawa Iyayen ka asiri kasan iyakar ka.

Na rantse inka shiga WAHALA wani ko labarin bazaii so jiba wallahi duk wahalar da muke ba ko wanne HON zai dauki yarsa ya baka a matsayin aure ba domin kallon sakaraii wanda baisan chiwan kansa.

~Abdulmalik Ashiru DanMaje ~

Tsaffin Kansilolin Ganduje Sun Barranta Kansu Da Maganganun Abdullah Abbass Wande Yace Kada Su Yadda Da Abba Akan Biyans...
07/08/2025

Tsaffin Kansilolin Ganduje Sun Barranta Kansu Da Maganganun Abdullah Abbass Wande Yace Kada Su Yadda Da Abba Akan Biyansu Hakkinsu Idan S**a Zo Zasu Biyasu.

~Jikan Oga ~

sune s**a fi kowa Gaskiya a Nigeria.sune masu Tantance me gaskiya Da me ƙarya a Nigeria.su kaɗai ne masoya Nigeria na ga...
07/08/2025

sune s**a fi kowa Gaskiya a Nigeria.

sune masu Tantance me gaskiya Da me ƙarya a Nigeria.

su kaɗai ne masoya Nigeria na gaskiya.

sun fi kowa Gane me lefi a Nigeria.

sun fi kowa sanin matsalar Nigeria.

sun fi kowa kishin Nigeria.

Daga kudu da Arewa babu masani kamar su.

sune wa'yanda basu taɓa cin haƙƙin kowa ba.

sunfi kowa sanin Tattalin Arziƙin Nigeria.

kowa mara Daraja ne sune masu Daraja.

Wannan shine Tunanin su: koma bashi bane shi Ɗin ne.

Da kowa zai Ajje Tunanin sa yabi nasu da yanzu Duk Bama nan sai dai ayi sabon zubi a Nigeria Domin kowa saiya ƙare.

Tunanin da Akayi ya kawo matsala ba shi Akeso wajen warwareta ba: Amma su Tunanin da zarce tunanin matsalar suke kawowa ta yadda ran kowa zai ƙara ɓaci Daga ƙarshe a haɗu a kaure da Rikici.

~Shehu Tijjani~

A dakin ajiyar masu laifi, an Karyawa Sowore hannun sa na dama.
07/08/2025

A dakin ajiyar masu laifi, an Karyawa Sowore hannun sa na dama.

Dakin kwana kyauta ne Sede in Baka Shiga hanun mu ba.~Mahidu Muazu Abubakar ~
07/08/2025

Dakin kwana kyauta ne Sede in Baka Shiga hanun mu ba.

~Mahidu Muazu Abubakar ~

07/08/2025

Shugaban Jamiyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas ya nuna damuwarsa akan yanda Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif ya fara biyan tsofaffin Kansiloli hakkokin su.

Yace su kula kada Dan Gwamna ya biyasu hakkokin su kawai s**e zasu koma tsagin tafiyar Kwankwasiyya.

A karshe Abdullahi Abbas yayi Kira ga yan Social Media na Jamiyyar APC da zagi Uwa da Uban kowanene a bangaren yan adawa, zai tsaya musu babu abinda za'ayi.

Dr. Nasiru Yusif Gawuna da magoya bayansa sun amince da Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin Jagoran jamiyyar APC na ji...
06/08/2025

Dr. Nasiru Yusif Gawuna da magoya bayansa sun amince da Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin Jagoran jamiyyar APC na jihar Kano.

Hakan ya biyo bayan taron masu Ruwa da tsaki na Jamiyyar APC da ya gudana a Jiya a Gidan Ganduje da ke jihar Kano.

Wadansu Yan Jamiyyar APC suna ganin kamata yayi Sanata Barau Jibrin shi ya kamata ya zama Jagoran jamiyyar APC na Kano.

Ana cigaba da bayyana ra'ayoyin tsakanin Bangarorin guda 2.

A hannu guda Kuma Dan Majalissar Tarayya na Bichi Engr. Abba Bichi da Sauran Yan Majalissar Tarayya na APC sun goyi da bayan Ganduje.

Shin wa kuke ganin zasu goyi bayan Sanata Barau Jibrin ?

06/08/2025

Laifina guda daya ne da Yan Kwamiti s**a tuhume ni akanshi, shine na amsar Belin Babban dilan Kwaya a matsayina na Kwamishina ba tare da na sanarwa da Mai girma Gwamna ba.

~Ibrahim Namadi, tsohon Kwamishinan Sufuri na Kano~

Jagoran jamiyyar NNPP na Kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da Zababbun Yan Majalissar jiha na jihar Kano Karkash...
05/08/2025

Jagoran jamiyyar NNPP na Kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya gana da Zababbun Yan Majalissar jiha na jihar Kano Karkashin Jagorancin Shugaban Majalissar, R.T Hon. Jibrin Falgore.

Ya gana da sune akan shirye-Shiryen Zaben cike gurbi da za'a yi a Kujerar Dan Majalissar jiha na Bagwai da Shanono da za'a yi bisa Rasuwar Wanda yake akai.

Wanda ya rasu, Marigayi Hon. Halilu Ibrahim Kundila na Jamiyyar APC ne, kusan tsawon Shekara guda ke nan.

Kwankwaso da magoya bayansa sun lashi Takobin sune zasu lashe Wannan Zabe musamman yanda suke da Gwamnati a jihar ta Kano, Sai dai Kuma Bangaren jamiyyar APC sun shirya tsaf domin Kara samun nasarar Wannan Kujera musamman yanda suke da Manyan Mukamai a Gwamnatin Tarayya.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SGG TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share