SGG TV

SGG TV This is an official page for SGG TV, It deals with the fact from genuine Source (s). Please join us and stay connected. 🙏

Mallam Aminu Saira, an nuna Sumayya riƙe da ɗan ta suna raka Aliyu lokacin da zai tafi opis da safe. Mun ga tablet a han...
25/10/2025

Mallam Aminu Saira, an nuna Sumayya riƙe da ɗan ta suna raka Aliyu lokacin da zai tafi opis da safe. Mun ga tablet a hannun yaron. Amma da s**a fita harabar gida, sai muka ga yaron yana cin masara.

A lokacin da suke cikin palo, babu wannan masarar a hannun yaron. Ba kuma za ka ce yaran Aliyu (su Jogodo) ne s**a ba shi ba, domin lokacin da aka isa wajen su, su ma suna cin masarar.

Kuma ta yaya za a ɗauki busashshiyar masara da sassafe a ba Prince Ahmad, jikan Sarkin Gabas, ya ci? A'ina ake gasa masara da safe?😃

Mallam Saira, your direction is always top-notch, but please pay more attention to your Script Supervisor; some continuity errors were too clear.

YA KASHE RAI SABODA ZAI KARA AUREMatashi magidanci Mamuda Zakari Ya'au wanda ake yiwa lakabi da Wadata mai shekaru 30 ya...
18/10/2025

YA KASHE RAI SABODA ZAI KARA AURE

Matashi magidanci Mamuda Zakari Ya'au wanda ake yiwa lakabi da Wadata mai shekaru 30 yana da mata biyu, ya aikata kisan kai saboda zai kara mata na uku anan cikin garin Bauchi

Kamar yadda kakakin rundinar 'yan sandan jihar Bauchi CSP Ahmed Muhammad Wakil ya sanar, Shekaran jiya Alhamis da misalin karfe 9 na dare, Mamuda Zakari ya tare wani dan acaba mai suna Basiru Muhammad dan shekara 25 yace ya kaishi unguwar Sulaimanu Adamu Quarters dake kusa da Old Airport Bauchi

Da s**a isa gurin sai Mamuda ya zare wuka ya burma a cikin dan acaban Basiru Muhammad, sai ya dauke mashin dinsa ya fara guduwa, anan dai jama'a s**a kawo dauki, sai Mamuda ya jefar da mashin din ya gudu, a yayin guduwa ya jefar da wayansa

'Yan sanda sun kai dauki, kafin a kai Basiru zuwa Asibiti rai yayi halinsa, amma anyi dace an gano wayar Mamuda, ta nan aka ganoshi aka kamashi, kuma ya amsa laifinsa

Yace dalilin da yasa ya aikata laifin kisan shine yana so ya dauke mashin din ne ya sayar ya kara mata na uku duk da yana sana'ar sayar da kayan marmari

Imbanda Allah Ya sa ya jefar da wayansa da wahala a kamashi, amma alhakki ma ba zai barshi ba, saboda bai san adadin mutanen da suke karkashin ciyarwan dan acaban da ya kashe ba saboda kawai yana son yayi sabon aure yaji dadin jima'i

Yanzu gashi ya rasa amaryan da zai aura, matansa guda biyu suma zai rasa su, shikenan rayuwarsa zata kare a gidan yari, wasu kuma su aure sauran matan nasa guda biyu su yi ta jima'i dasu yana can daure a kurkuku

Jama'a mu ji tsoron Allah, duk abinda ka samu ta hanyar haram inda zakayi hakuri ka tashi ka nema ta hanyar halal Allah Zai baka

Muna fatan Allah Ya tsare mana imaninmu

~Datti Assalafi~

17/10/2025

Celebrating my 5th year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

Ba farko ba karshen!!Hakika mutuwar Wannan bawan Allah jami’in hukumar kwastam A wani hotel a katsina Abar tashin hankal...
17/10/2025

Ba farko ba karshen!!

Hakika mutuwar Wannan bawan Allah jami’in hukumar kwastam A wani hotel a katsina Abar tashin hankali ce kuma Darasi ce ga masu rayuwa

Kamar yanda labari yake ta yawo A kafafen sada zumunta ya rasu bayan tarewa da mata 3 a daki daya

Tun 15 ga Wannan watan da muke ciki wanda yanzu haka gawarsa na mutuware Ana gudanar da bincike kuma duka Matan 3 suna hannu

Rayuwar bariki tana da qalubale irin haka wanda mutum baisan karshen ba

Allah ya gafarta mai kurakuransa Allah yasa karshen mu yayi kyau ya daidaita mana zuciyar mu Ameen

Cewar Saidu Sani.

Su wanene wadannan, kuma a wanne lokacine, sannan a wacce Jamiyyar ne ?
16/10/2025

Su wanene wadannan, kuma a wanne lokacine, sannan a wacce Jamiyyar ne ?

Assalamu Alaikum Jama’aAkan batun abin da ya faru wanda muke zargin an yaudari ‘yan Arewa a cikin wata mu’amala ta crypt...
15/10/2025

Assalamu Alaikum Jama’a

Akan batun abin da ya faru wanda muke zargin an yaudari ‘yan Arewa a cikin wata mu’amala ta crypto, ya zama dole in yi wannan bayani don fayyace komai

Wasu suna ganin ba a yi wa al’ummah rashin adalci ba, amma gaskiya ita ce mutane da yawa sun fada cikin tarko saboda amincewa da wani tsarin da daga baya ya nuna akwai alamar cin amana da zalunci.

Ni kaina saboda tsantsar yarda da na yi da wasu, da kuma goyon bayan da na nuna ga al’ummah, ana zargin cewa inada hannu a cikin lamarin. Amma wallahi ni ma cikin wadanda aka cuta nake, kuma ina tare da masu neman adalci.

Jiya, bayan tattaunawa da wasu daga cikin wadanda abin ya shafa, mun samar da mutane 50 da suke da cikakken hujja cewa an zalunce su. Na nemi taimakon mai gidana, Wani Sanata mai ci, don ya hada mu da hukumar EFCC, domin su ne za su fi tabbatar da gaskiya ta hanyar bincike mai zurfi.

Mun riga mun mika shaidu guda 61 na screenshots da wasu takardu da hujjoji, kuma sashen da zai kula da wannan bincike na iya bukatar karin bayani daga gare mu.

Saboda haka, muna roko da tawali’u ga duk wanda wannan zalunci ya rutsa da shi:
➡️ Ku rubuta adadin asarar da kuka yi a comment section,
➡️ sannan ku tag ɗin hukumar EFCC don ta ga irin wannan koke kai tsaye daga jama’a.

Insha Allah, zan ci gaba da bibiyar wannan lamari har sai an tabbatar da gaskiya ta fito fili.

Ba domin sharri nake ba, amma domin kare ‘yan uwa daga masu zalunci da ke fakewa da sunan taimako suna cutar mutane.

Takardar da muka shigar da sunan mutum 50 page 3 wannan iya page daya na saka

Wannan takardun ba don ɓata suna na sakasu ba, sai dai don nuna cewa an kai ƙorafi ga hukumomi domin neman adalci, Kuma hakan zai kwantar da hankali wanda s**ayi asara

Allah ya taimaki masu gaskiya,
Ya kuma tona asirin azzalumai a cikin wannan harkar crypto.
Amin.

Kada mu yi shiru idan aka zalunce mu. Shiru yana ƙarfafa mai zalunci.
Gaskiya ba ta tsorata da bincike — don haka mu tsaya a kan gaskiya, mu nemi adalci tare da haɗin kai. ✊🏽

Sadiq dalhatu
15/10/2025

Warware Gurguwar Fahimta Kan Sauye-sauyen Harajin Kuɗin Shiga Na Gwamnatin Shugaba TinubuRubutawa: Michael ChibuzoFassar...
04/10/2025

Warware Gurguwar Fahimta Kan Sauye-sauyen Harajin Kuɗin Shiga Na Gwamnatin Shugaba Tinubu

Rubutawa: Michael Chibuzo
Fassarawa zuwa Hausa: Aliyu Samba

Yayin da kwanaki ƙididdigaggu s**a rage mu shiga sabuwar Shekara ta 2026, ranar da sabbin dokokin haraji guda biyu za su fara aiki, labaran ƙarya da gurguwar fahimta game da waɗannan dokoki na haraji sun ƙaru sosai a kafafen sada zumunta. Wasu daga ciki suna bayyana ne sakamakon rashin sani, yayin da wasu da yawa kuma wata manufa ce ta siyasa da neman ɓata sunan Gwamnati. A wannan rubutu, zan yi ƙoƙarin warware wannan gurguwar fahimtar game da harajin kuɗin shiga (income tax) a cikin Dokar Haraji ta Najeriya, 2025.

Manyan Jita-jitan Da Aka Fi Ji:

1. Daga ranar 1 ga Janairu, 2026, ‘yan Najeriya za su fara biyan harajin kuɗin shiga mafi tsada.
2. Gwamnati za ta rika cire haraji kai tsaye daga asusun banki na mutum.
3. Gwamnatin Tarayya na neman ƙarin kuɗin shiga ta hanyar kakabawa ‘yan Najeriya haraji mai nauyi.
4. Sabbin dokokin haraji za su hana kasuwanci da haɓakar tattalin arziki.

Zan bisu daki-daki domin warwarewa.

1. SHIN ZA A ƘARA NE, KO KUMA RAGE HARAJIN KUƊIN SHIGA?

Gaskiyar magana ita ce, mafi yawan ‘yan Najeriya za a rage musu haraji sakamakon sabbin tanade-tanaden da ke cikin sabuwar dokar haraji ta 2025, inda aka ware mutanen da ke samun N800,000 ko ƙasa da haka a shekara daga biyan kowanne irin haraji. Ma’ana, ma’aikaci mai karɓar albashin mafi ƙaranci ko ƙasa da haka ba zai biya haraji ba kwata-kwata.

Wasu na iya cewa mafi ƙarancin albashin gwamnati yanzu N70,000 ne a wata (N840,000 a shekara), wanda ya fi N800,000 da aka ware. Haka ne, amma abin lura shi ne, ba duka kuɗin shiga ake kira taxable income ba. Akwai abin da ake kira (Taxable Income), wato abin da ya rage bayan an cire rangwamen da aka amince da shi kamar:
• Kudin Inshorar Lafiya NHIS (kimanin 5% na albashi)
• Rangwamen haya (20% na haya da bai wuce N500,000 ba)
• Gudunmawar gidauniyar gidaje ta ƙasa NHF (2.5% na albashi)
• Gudunmawar fansho (8% na albashi)
• Inshorar rayuwa, na ka da iyalin ka.

Misali, ma’aikacin da ke karɓar N70,000 a wata (N840,000 a shekara) kuma yake biyan haya N200,000 a shekara, tare da kudin Inshorar lafiya na NHIS, NHF da fansho, zai sami taxable income na N710,800 kacal. Wannan yana cikin iyakar nan da ta ware masu samun N800,000, hakan ya nuna ba zai biya haraji ba.

Ko wanda ke karɓar N80,000 a wata (N960,000 a shekara) zai iya shiga cikin waɗanda aka ware idan an yi amfani da irin waɗannan tsarin. A taƙaice, talakawa da ƙananan ma’aikata sun samu sauƙi, sai masu kuɗi sosai ne za su ɗan biya fiye da da.

2. SHIN ZA A CIRE HARAJI KAI TSAYE DAGA BANKI?

Amsar ita ce A’A! Ba za a rika cire haraji kai tsaye daga asusun bankin mutum ba.

Abin da dokar Haraji ta 2025 ta tanada shi ne, sashe na 29 ya wajabtawa bankuna su rika ba hukumar haraji rahoton masu asusu waɗanda ke da mu’amalar banki har ta fiye da Naira Miliyan 25 a wata ga mutum ɗaya, da Naira Miliyan 100 ga kamfani. Wannan ba yana nufin su cire haraji bane, bayanan ne kawai suke tattarawa don gano masu kuɗi da ke gujewa biyan haraji.

Mutanen da mu’amalarsu ba ta kai Naira Miliyam 25 a wata ba, ba zai shafe su ba kwata-kwata. Kuma a yanzu, fiye da kaso 90% na ‘yan Najeriya ba su da kuɗaɗen da s**a kai wannan adadi a asusun banki.

3. SHIN GWAMNATIN TARAYYA NA NEMAN KUƊI NE TA HARAJI?

Amsar ita ce A’A!

A haƙiƙa, sabbin dokokin an yi su ne domin rage nauyin haraji ga talakawa. Harajin kuɗin shiga da ake magana akai ma, ba na gwamnatin tarayya ba ne kai tsaye. Sashe na 3(2) na dokar haraji ta ƙasa ya bai wa Jihohi ikon karɓar harajin kuɗin shiga daga mutanen da ke zaune a cikin jihohinsu. Gwamnatin Tarayya kawai tana tattara haraji ne daga ma’aikatan soji, ma’aikatun diflomasiyya na ƙasashen waje, da kuma mutanen waje da ke samun kuɗi daga Najeriya.

Saboda haka, jihohi ne suke cin gajiyar harajin kuɗin shiga, ba gwamnatin tarayya ba. Wannan ke nuna cewa ba wai gwamnati na neman karin kuɗi daga talakawa bane, a’a, ana ƙoƙarin kawo sauƙi ne.

4. SHIN SABON DOKAR HARAJI ZAI HANA TATTALIN ARZIKI CI GABA?

A’a, akasin haka ne. Sabbin dokokin suna nufin taimaka wa ƙananan ƴan kasuwa ne da masu ƙaramin karfi.

Misali:
• Dokar haraji ta ƙasa ta ware ƙananan kamfanoni (masu juya kuɗin da bai kai Naira Miliyan 100 ba a shekara) daga biyan harajin riba gaba ɗaya. Wannan ya kai sama da kaso 90 cikin 100 na kamfanoni a Najeriya.
• Manyan kamfanoni kuwa za su ci gaba da biyan kaso 30% na Harajin Kuɗaɗen Shiga na Kamfanoni, amma akwai tanadi a doka cewa za a rage shi zuwa kaso 25% idan Kwamitin Tattalin Arziƙi na ƙasa da Jihohi sun tabbatar hakan ba zai cutar da ribar da ke shiga asusun tarayya ba.

Idan dokokin za su hana ci gaba, za a ƙara Harajin Kuɗaɗen Shiga na Kamfanoni zuwa fiye da kaso 30%,, amma abin da sabuwar doka ta tanada ragewa yake, ba ƙarawa ba.

KAMMALAWA

Daga abin da muka gani, sabbin dokokin haraji, musamman na kuɗin shiga al’amari ne mai sauƙi, domin zai kare talakawa ne, tare da goyon bayan ‘yan kasuwa ƙanana da nufin ƙarfafa ci gaban tattalin arziki.

Jihohi da hukumomin haraji ya kamata su gudanar da wayar da kai sosai domin mutane su fahimci gaskiyar abin da aka tanada, maimakon su saurari jita-jita marasa tushe.

A ƙarshe, dole ne mu gane cewa biyan haraji nauyi ne na ‘yan ƙasa. Duk wanda ya cancanci biyan haraji bai da hujjar guduwa. Wannan sabuwar doka ma ta sanya masu kuɗi da manyan kamfanoni su kasa gujewa biyan haraji. Idan hakan ya tabbata, zai ƙara wa jama’a ƙarfin gwiwa wajen neman bahasi da gaskiya daga shugabanni kan yadda ake amfani da kuɗaɗen jama’a. Wannan kuwa, a ƙarshe, yana nufin ƙarfafa ci gaban ƙasa ne cikin sauri.

Tawagar Shiekh Qaribullah Sheikh Nasiru Kabara, yayin Maukibin Ƙadiriyya karo na 75.
04/10/2025

Tawagar Shiekh Qaribullah Sheikh Nasiru Kabara, yayin Maukibin Ƙadiriyya karo na 75.

03/10/2025

Gwamnan jihar Kano, His Excellency Alh. Abba Kabir Yusuf yayi alkawarin zai kammala biyan Sauran tsofaffin Kansiloli kashi na 3 da Sukayi Mulki da Ganduje hakkokin su a watan Nuwamba mai kamawa.

Ya fadi haka ne a dai-dai lokacin da aka cigaba da biyan tsofaffin Kansiloli kashi na 2 hakkokin su wanda Ganduje ya hanasu ko Naira 1.

Kowanne Tsohon Kansila ya sami Sama da Naira Miliyan 4, Kashi na farko sun Sami kusan Naira Miliyan 2, yanzu wadanda s**a rage sune wadanda s**ayi mulki da Ganduje daga 2021 zuwa zuwa 2024.

Gwamnan Kano, ya umarce Babban akawunta na Kano akan a tabbatar an tana ji Sama da Naira Biliyan 8 domin kammala biyan Sauran Kansiloli hakkokin su.

Wanne fata kuke yiwa Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif ?

03/10/2025

Ashe kuma Atiku haka ta faru, to Allah ya sa karhen wahalar kenan- Garba Kore

Shugaban Jamiyyar APC na Kasa,  Professor Nentawe Yilwatda yana gayyatar al'ummar Nigeria wajen bikin binne Mahaifiyar s...
02/10/2025

Shugaban Jamiyyar APC na Kasa, Professor Nentawe Yilwatda yana gayyatar al'ummar Nigeria wajen bikin binne Mahaifiyar sa da za'a yi a ranar 4/10/2025.

Za'a fara rera wakoki a ranar 3/10/2025.

Ga wadanda basu sami damar zuwa ba, ana bukatar Sorry Sorry Sorry kafa 3 !

Gwamnatin Kano ta dakatar da Lawan Triumph daga yin Wa'azi har sai ya zo ya gurfana gaban Kwamitin Malaman Jihar Kano do...
01/10/2025

Gwamnatin Kano ta dakatar da Lawan Triumph daga yin Wa'azi har sai ya zo ya gurfana gaban Kwamitin Malaman Jihar Kano domin bada hujjoji ga me da Munanan Kalamai na rashin ladabi da ya furta ga fiyayyen halitta Annabi Muhammad Salallahu alaihi Was Sallam.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SGG TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share