Arewa sky News

Arewa sky News Wannan kafa zata rinka kawo muku labaran gida dana ketare masu inganci gami da ilimantar daku da nishadarwa

BA RABO DA GWANI BA: Wasu Daga Cikin Ayyukan Cigaban Kasa Da Marigayi Muhammadu Buhari Ya Wanzar A Mulkinsa     Daga Ali...
14/07/2025

BA RABO DA GWANI BA: Wasu Daga Cikin Ayyukan Cigaban Kasa Da Marigayi Muhammadu Buhari Ya Wanzar A Mulkinsa

Daga Aliyu Ahmad

FANNIN ILlMI
1)- Ya gina Jami'ar da ta shafi aiyukan teku da tukin jirgin ruwa da gyaran-sa mai suna 'Maritime University' a jihar Delta dake shiyar kudu maso kudancin Najeria.

2)- Ya gina Jami'ar Sojoji Mai-suna 'Army University dake garin Biu, jihar Borno shiyar Arewa maso Gabas.

3)- Ya Gina Jami'a ta Harkokin Noma Mai-suns (Agricultural University) dake Garin Zuru, jihar Kebbi shiyar Arewa maso Yamma.

4)- Ya Gina Jami'ar Sufuri a Garin Daura, Mai-suna (Transportation University) Daura jihar Katsina, shiyar Arewa maso yamma.

5)- Samar da kudade sama da Naira Biliyan Dari hudu (400 billon) ga Jami'oin dake kasar nan ta hanyar Hukumar Asusun tallafin Ilmin Mai Zurfi (TETFUND)...

6)- Ya Gina Jami'a ta aikin Sojin Sama a Garin Tafawa Balewa dake Jihar Bauchi. Shiyar Arewa maso Gabas.

7)- Ana Gina Sabbin Kolejojin ilimi guda Shida (6) a Jihohi kamar haka;-

A) Bauchi
B) Benue
C) Ebonyi
D) Osun
E) Sokoto da
F) Edo

G) Ya kafa Kwalejin Kimiyya da Safaha a Garin Daura jihar Katsina.

8 Karin Manyan Jami'oi Na Musamman A kowacce Shiya ta kasarnan.

FANNIN LAFIYA
1) Ginin Babban Asibitin Jinya na Sojin Sama a Garin Daura Jihar Katsina.

2)- Babban Asibin Sojin Sama a Garin Bauchi, dake Jihar Bauchi.

3)- Asibitin Mata da Kananan Yara dake Daura jihar Katsina.

4)- Ya Gina Asibitin Sojioji, dake Garin Kaduna jihar Kaduna.

5)- Ya Gina Cibiyar Kula da masu dauke da Cutar Daji (Cancer) a Birnin Tarayya Abuja.

6)- Ya Gina Cibiyar Kula da masu Dauke da cutar Daji (Cancer) a Babbar Jami'ar koyar wa ta Gwamnatin Tarayya dake Lagos, Jihar Lagos.

7. Ingantawa da gyarawa, bugu da Kari ya samar da kayan Aiki Ga Manyan Asibitocin Gwabnatin Tarayya a kowacce jiha dake fadin Nijeriya.

FANNIN GADOJI
1)- Ya karasa Ginin Babbar Gadar nan data Hada jihohin Delta da Anambra (Second Niger Bridge)

2)- Aikin Babbar Gadar nan dake Kogin Benue, Mai-sun

Da me za ku tuna marigayi tsohon shugaban Najeriya, Janar Muhammadu Buhari?
13/07/2025

Da me za ku tuna marigayi tsohon shugaban Najeriya, Janar Muhammadu Buhari?

LABARI AKAN KASAR AMURKA DA CHINA....A shekarar 2018 kasar Amurka ta aike jiragen ruwan yaki zuwa yankin Hong Kong na ka...
05/07/2025

LABARI AKAN KASAR AMURKA DA CHINA....

A shekarar 2018 kasar Amurka ta aike jiragen ruwan yaki zuwa yankin Hong Kong na kasar China, hakan baiyiwa China daɗi ba ko kadan, amma ba yadda zatayi, jirgin ruwa mai daukar jiragen sama na yaki maisuna USS RONALD REAGAN Amurka ta tura tare da wasu jiragen yaki...

Amurka tayi haka ne wai saboda ta nunawa mutanen Hong Kong cewa tana tare dasu...

Tun bayan faruwar hakan sai China ta mayar da hankali wajen samar da nata jirgin ruwan mai daukar jiragen sama wanda akewa lakabi da Aircraft Carrier, yanzu zancen da ake China ta samu nasarar samar da irin wadannan jirage har guda uku sannan tana aikin samar da wani yanzu haka wanda ake kyautata zaton zaifi kowanne Aircraft Carrier girma da Technology a duniya...

Hatta sabon Aircraft Carrier na kasar China wands ya fara ayyuka a wannan shekara ta 2025 maisuna FUJIAN aircraft carrier an tabbatar da cewa yana dauke da Technology mai ban mamaki wanda kasar China ce kawai dashi...

Amurka ta saba yiwa China wulakanci da izza a baya, amma da yake mutanen China hazikai ne masu kishin kasarsu duk wani kalar wulakanci da Amurka tayi musu to zasu mayar da hankali har sai sun samar da shi irin abun da akayi musu wulakanci akansa, har ma s**an samar da wanda yafi na Amurka....

MASU DUBA AYYUKAN NUKILIYA NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA SUN FICE DAGA KASAR IRAN....Masu duba makaman nukiliya na hukumar ...
05/07/2025

MASU DUBA AYYUKAN NUKILIYA NA MAJALISAR DINKIN DUNIYA SUN FICE DAGA KASAR IRAN....

Masu duba makaman nukiliya na hukumar IAEA ta Majalisar Dinkin Duniya sun bar Iran ranar Juma'a bayan kasar ta dakatar da hadin kai da hukumar, sakamakon rikicin kwanaki 12 da ya faru tsakanin Iran da Isra’ila, wanda ya haifar da harin jiragen sama na Isra’ila da Amurka a wuraren makaman nukiliyar Iran. Wannan ya janyo tashin hankali tsakanin Tehran da hukumar IAEA...

Hukumar ta bayyana cewa tawagar ta fice daga Iran lafiya, suna komawa hedkwatar hukumar a Vienna, bayan sun kasance a Tehran a lokacin rikicin soja. Daraktan IAEA, Rafael Grossi, ya jaddada muhimmancin ci gaba da tattaunawa da Iran domin sake farfado da ayyukan sa ido da tabbatarwa cikin gaggawa...

Iran ta dakatar da hadin kai da IAEA a hukumance ranar Laraba, bayan majalisar kasar ta amince da dokar da ke tabbatar da kare hakkin kasar a karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, musamman ma game da bunkasa sinadarin uranium....

Amurka ta soki wannan mataki na Iran, tana mai cewa ba abin karɓa bane, tare da kira ga Tehran da ta dawo kan teburin tattaunawa da aka katse sakamakon harin soja na Isra’ila a watan Yuni...

A gefe guda, Isra’ila ta yi kira ga kasashen duniya da su dauki matakan da s**a dace don tunkarar Iran, har da dawo da takunkumi kan kasar, yayin da ta yaba da nasarorin da sojojinta s**a samu a yakin kwanaki 12 da s**a gabata, duk da dai a zahiri ita Isra’ila ce tafi ɗanɗana kuɗarta...

A takaice, wannan lamari ya kara tsananta rikicin siyasa da na tsaro a yankin, tare da jefa al’amuran nukiliyar Iran cikin yanayi mai cike da rashin tabbas...

Alh Aminu Alasan Dantata, Allah SWT yasa mutuwa hutuce, yasa Aljannah ce makoma! Allah ya bamu hakurin rashin ka. Ya alb...
28/06/2025

Alh Aminu Alasan Dantata, Allah SWT yasa mutuwa hutuce, yasa Aljannah ce makoma!

Allah ya bamu hakurin rashin ka. Ya albarkaci bayan ka ila yaumul kiyama! 😭😭😭

22/05/2025

Ivory Coast.

S0j0ji sun karbe kasar.
Fa-ra-nsa ta sake rasa wata kasa a Africa again.

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Sh...
12/05/2025

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Shugaba Ibrahim Traoré zuwa gida, Burkina Faso, bayan halartar bikin cika shekara 80 da fatattakar N**i a Rasha. Masana tsaro sunyi itifakin cewa waɗannan jiragen yakin suna ɗauke da makaman zamani masu linzami kiran hypersonic. Jama'a yanzu duniya, musamman masu mulkin mallaka da ke da burin mamaye duniya, sun fahimci cewa Rasha na daraja Afirka da al'ummanta, musamman shugabanninta masu nagarta irinsu Ibrahim Traoré. Allah Ubangiji Ka tarwatsa azzalumai masu son dakile nahiyar Afrika. Amin

12/05/2025

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Shugaba Ibrahim Traoré zuwa gida, Burkina Faso, bayan halartar bikin cika shekara 80 da fatattakar N**i a Rasha. Masana tsaro sunyi itifakin cewa waɗannan jiragen yakin suna ɗauke da makaman zamani masu linzami kiran hypersonic. Jama'a yanzu duniya, musamman masu mulkin mallaka da ke da burin mamaye duniya, sun fahimci cewa Rasha na daraja Afirka da al'ummanta, musamman shugabanninta masu nagarta irinsu Ibrahim Traoré. Allah Ubangiji Ka tarwatsa azzalumai masu son dakile nahiyar Afrika. Amin

Yaƙe yaƙe har uku aka gwabza tsakanin Indiya da Pakistan tun bayan da s**a sami yancin kai a shekarar 1947.  Ga shi kuma...
07/05/2025

Yaƙe yaƙe har uku aka gwabza tsakanin Indiya da Pakistan tun bayan da s**a sami yancin kai a shekarar 1947. Ga shi kuma na hudu na kokarin ballewa.

Kashmir yanki ne da ke tsakanin Indiya da kasar Pakistan wadda kasashen biyu s**a shafe shekaru da dama suna rikici dangane da mallakarsa.

Rikicin da aka dade ana gwabzawa kan yankin Kashmir da ta'addanci a kan iyakokin kasashen biyu, shi ne musabbabin rikici tsakanin kasashen biyu, in ban da yakin Indo-Pakistan na 1971, wanda ya faru ne sakamakon tashin hankalin da ya samo asali daga yakin 'yantar da Bangladesh a tsohuwar Pakistan (yanzu Bangladesh ).

Ga duk me bibiyar rikicin dake faruwa yanzu a kasashen indiya da fakistan, bazai kasa sanin rikicin yankin kashmir tsakanin Indiya da makociyarta Pakistan ba. Rikicin neman mallakar yankin tsakanin kasashen biyu ya janyo asarar dinbin al'umma musamman mabiya Addinin Musulunci. Kowace kasa tsakaninsu nason mallakar yankin da yake da yawan al'umma akalla miliyan 69,07,623. Srinagar ita ce yanki mafi yawan jama'a a kwarin Kashmir, tare da mazauna 1,269,751. sannan yanki ne me dinbin arziki musamman ta bangaren noma da sana'oin hannu, da yawon buɗe ido.

Bisa tarihi kasashe uku ne suke rikici akan mallakar yankin, banda Indiya, Pakistan akwai kasar sin (China). Yankin na Kashmir da ake kira Jammu Kashmir yana karkashin ikon Indiya yanzu haka, amma kuma sauran kasashen biyun su ma suna da iko da wasu wuraren. Indiya nada iko da akalla kaso 70, inda ya kunshi Jammu, Jammu ladakh da kuma Siachenglacier. Ita kuma Pakistan tana da iko da kaso 30 daya kunshi Azad Kashmir da Gliqit Baltisan, yayinda China kuma takeda kaso 15 daya kunshi Shashgam Valley da kuma Aksai chin.

Yankin Jammu Kashmir jiha ce karkashin kasar Indiya, amma kuma tanada kwarya-kwaryar 'yancin cin gashin kai, wanda ya kunshi cewar babu wata doka da 'yan majalisun Indiya zasuyi da zatayi amfani a yankin, sai dokar da 'yan majalisun yankin s**ayi. Sannan yankin ne kadai yake da tutar sa ta kashin kansa, wato

Ta tabbata dai yau za'a daura Auran Rarara da Aisha Humaira a Maiduguri. Wane fata zaku musu?
25/04/2025

Ta tabbata dai yau za'a daura Auran Rarara da Aisha Humaira a Maiduguri. Wane fata zaku musu?

23/04/2025

Gwamnan Jihar Delta dake Najeriya Sheriff Oborevwori ya sanar da sauya shekarsa daga PDP zuwa APC. Gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne saboda ci gaban jiharsa sakamakon doguwar tattaunawar da akayi da masu ruwa da tsaki a jihar. Sheriff Oborevwori ya zama gwamnan Delta ne sakamakon tsayar da shi takarar da Jam'iyyar PDP ta yi a zaben shekarar 2023 domin maye gurbin Ifeanyi Okowa da ya kammala wa'adinsa na biyu. Jihar Delta na daya daga cikin tungar Jam'iyyar PDP a siyasar Najeriya, kuma ko a zaben da ya gabata, tsohon gwamnan jihar ne aka ɗauka a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a Jam'iyyar PDP. Masu sanya ido na danganta wannan sauya sheka da nasarar da shugabannin jam'iyyar APC a ƙarƙashin jagaroncin Abdullahi Ganduje ke samu wajen ganin an sake zaben shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027.

DA DUMI DUMI: Yariman Barci` Na Saudiyya ya cika Shekaru 36 Bayan Fiye da Shekara 20 a kwance Bai farfaɗo Ba, Yarima Al-...
19/04/2025

DA DUMI DUMI: Yariman Barci` Na Saudiyya ya cika Shekaru 36 Bayan Fiye da Shekara 20 a kwance Bai farfaɗo Ba, Yarima Al-Waleed bin Khaled bin Talal, wanda aka fi sani da “Yariman Barci” a fadin duniya ta Larabawa, ya cika shekaru 36 a ranar Juma’a, 18 ga Afrilu, duk da cewa yana cikin dogon suma da ya kwashe fiye da shekaru 20 a ciki.

Ya samu suma ne a shekarar 2005 bayan mummunan hatsarin mota da ya rutsa da shi a birnin London.

A cikin sa’o’i 24 da s**a gabata, ranar zagayowar haihuwarsa ta janyo hankalin mutane da dama a kafar X (Twitter), inda dubban masu amfani da kafar s**a wallafa addu’o’i, fatan alheri da tunatarwa game da wannan lamari da ya zama wata alama ta bangaskiya da jimiri.

Duk da tsawon lokacin da ya dauka a cikin wannan hali, yariman na ci gaba da samun kulawa ta musamman, yana dogara da na’urorin taimaka masa numfashi da abinci ta bututu. A shekara ta 2019, an bayyana cewa ya nuna wasu karancin motsi kamar daga yatsa ko motsa kai kadan, amma ba su nuna cewar ya farfado gaba ɗaya ba.

Yanzu haka yana karɓar kulawa a Cibiyar Lafiya ta Sarki Abdulaziz da ke Riyadh, karkashin kulawar kwararrun likitoci.

Iyayensa, ciki har da mahaifinsa Yarima Khaled bin Talal da mahaifiyarsa Gimbiya Reema bint Talal, na ci gaba da nuna cikakken fata da bege. A baya, Gimbiya Reema ta bayyana cewa “ransa har yanzu yana nan a jikinsa,” yayin da Yarima Khaled—wanda ya ki cire na’urorin taimako—ke ci gaba da tsayawa da yakinin cewa “Wanda Ya raya ransa tsawon wadannan shekaru, Shi ne Zai iya warkar da shi.”

Babu wani sabon bayani na kiwon lafiya da iyalansa s**a fitar dangane da wannan zagayowar haihuwarsa. Sai dai irin yawan goyon bayan da ya samu a kafafen sada zumunta na nuna yadda labarinsa ya ci gaba da zama abin tausayi da haɗin kai ga mutane a sassan yankin.

Masana sun akwai yiwuwar ya farfado bayan dogon lokaci irin wannan abu ne da ba kasafai yake faruwa ba, sai dai suna ci gaba da fatan sabbin ci gaba a ilimin kwakwalwa da jijiyoyi na iya kawo mafita nan

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa sky News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa sky News:

Share