Arewa sky News

Arewa sky News Wannan kafa zata rinka kawo muku labaran gida dana ketare masu inganci gami da ilimantar daku da nishadarwa

An sallaachi gawar Hon.Aminu sa’adu ungoggo a garin ungoggo
24/12/2025

An sallaachi gawar Hon.Aminu sa’adu ungoggo a garin ungoggo

Innalillahi Wa Inna Ilaihirraji'unTashin Hankali a Kano Yan Majalisu Biyu Sun Rasu: Dan Majalisa Hon. Sarki Aliyu Daneji...
24/12/2025

Innalillahi Wa Inna Ilaihirraji'un
Tashin Hankali a Kano Yan Majalisu Biyu Sun Rasu: Dan Majalisa Hon. Sarki Aliyu Daneji Ya Rasuwar bayan Rasuwar Abokinsa Aminu Saad Ungogo

Rahotanni sun tabbatar da rasuwar *Hon. Sarki Aliyu Daneji*, ɗan majalisar wakilai mai wakiltar karamar hukumar *Kano Municipal* a majalisar dokokin Jihar Kano, wanda ya rasu yau – *awa ɗaya kacal* bayan rasuwar abokin aikinsa a majalisar.

Wannan lamari ya girgiza al’umma da dama, musamman mazauna Kano, inda ake fassara lamarin a matsayin *musiba mai girma*.

Ana jiran cikakkun bayanai daga majalisar da iyalan mamacin. Jama’a na ci gaba da yi masa addu’a tare da fatan Allah ya gafarta masa, ya ba shi Aljannah Firdaus.

KUYI following Arewa sky News Don samun labarai

An rantsar da Dr. Ahmad Ajuji a matsayin sabon Shugaban jam'iyyar NNPP na kasa a karo na biyu.
20/12/2025

An rantsar da Dr. Ahmad Ajuji a matsayin sabon Shugaban jam'iyyar NNPP na kasa a karo na biyu.

𝑫𝒂 𝑫𝒖𝒎𝒊-𝑫𝒖𝒎𝒊 !𝑺𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏 𝒉𝒖𝒌𝒖𝒎𝒂𝒓 𝒌𝒖𝒍𝒂 𝒅𝒂 𝒉𝒂𝒓𝒌𝒐𝒌𝒊𝒏 𝒎𝒂𝒏 𝒇𝒆𝒕𝒖𝒓 𝒕𝒂 𝑵𝑴𝑫𝑷𝑹𝑨 𝒂 𝑵𝒂𝒋𝒆𝒓𝒊𝒚𝒂 𝑭𝒂𝒓𝒐𝒖𝒌 𝑨𝒉𝒎𝒆𝒅 𝒕𝒂𝒓𝒆 𝒅𝒂 𝒔𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏 𝒉𝒖𝒌𝒖𝒎𝒂𝒓 𝒌𝒖𝒍...
17/12/2025

𝑫𝒂 𝑫𝒖𝒎𝒊-𝑫𝒖𝒎𝒊 !

𝑺𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏 𝒉𝒖𝒌𝒖𝒎𝒂𝒓 𝒌𝒖𝒍𝒂 𝒅𝒂 𝒉𝒂𝒓𝒌𝒐𝒌𝒊𝒏 𝒎𝒂𝒏 𝒇𝒆𝒕𝒖𝒓 𝒕𝒂 𝑵𝑴𝑫𝑷𝑹𝑨 𝒂 𝑵𝒂𝒋𝒆𝒓𝒊𝒚𝒂 𝑭𝒂𝒓𝒐𝒖𝒌 𝑨𝒉𝒎𝒆𝒅 𝒕𝒂𝒓𝒆 𝒅𝒂 𝒔𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏 𝒉𝒖𝒌𝒖𝒎𝒂𝒓 𝒌𝒖𝒍𝒂 𝒅𝒂 𝒂𝒚𝒚𝒖𝒌𝒂𝒏 𝒉𝒂𝒌𝒐 𝒎𝒂𝒏 𝑭𝒆𝒕𝒖𝒓 𝒅𝒊𝒏 𝒕𝒂 𝑵𝑼𝑷𝑹𝑪 𝑮𝒃𝒆𝒏𝒈𝒂 𝑲𝒐𝒎𝒐𝒍𝒂𝒇𝒆 𝒔𝒖𝒏 𝒔𝒂𝒖𝒌𝒂 𝒅𝒂𝒈𝒂 𝒎𝒖𝒌𝒂𝒎𝒊𝒂𝒏𝒔𝒖.

𝑴𝒖𝒓𝒂𝒃𝒖𝒔 𝒅𝒊𝒏 𝒚𝒂 𝒛𝒐 𝒏𝒆 𝒂 𝒅𝒂𝒊𝒅𝒅𝒂𝒊 𝒍𝒐𝒌𝒂𝒄𝒊𝒏 𝒅𝒂 𝒂𝒌𝒆 𝒕𝒂 𝒔𝒂𝒎𝒖𝒏 𝒕𝒂𝒌𝒂𝒅𝒅𝒂𝒎𝒂 𝒕𝒔𝒂𝒌𝒂𝒏𝒊𝒏𝒔𝒖 𝒅𝒂 𝒉𝒂𝒎𝒔𝒉𝒂𝒌𝒊𝒏 𝒅𝒂𝒏 𝒌𝒂𝒔𝒖𝒘𝒂𝒓 𝒏𝒂𝒏 𝒏𝒂 𝑨𝒇𝒊𝒓𝒌𝒂 𝑨𝒍𝒊𝒌𝒐 𝑫𝒂𝒏𝒈𝒐𝒕𝒆.

𝑻𝒖𝒏𝒊 𝑺𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏 𝑵𝒂𝒋𝒆𝒓𝒊𝒚𝒂 𝑩𝒐𝒍𝒂 𝑨𝒉𝒎𝒆𝒅 𝑻𝒊𝒏𝒖𝒃𝒖 𝒚𝒂 𝒎𝒊𝒌𝒂 𝒃𝒖𝒌𝒂𝒕𝒂 𝒈𝒂 𝑴𝒂𝒋𝒂𝒍𝒊𝒔𝒂𝒓 𝑫𝒂𝒕𝒕𝒂𝒘𝒂 𝒕𝒂 𝒂𝒎𝒊𝒏𝒄𝒆 𝒅𝒂 𝒏𝒂𝒅𝒊𝒏 𝒔𝒂𝒃𝒃𝒊𝒏 𝒔𝒉𝒖𝒈𝒂𝒃𝒂𝒏𝒏𝒊𝒏 𝒎𝒂𝒏𝒚𝒂𝒏 𝒉𝒖𝒌𝒖𝒎𝒐𝒎𝒊𝒏 𝒃𝒊𝒚𝒖 𝒎𝒂𝒔𝒖 𝒌𝒖𝒍𝒂 𝒅𝒂 𝒉𝒂𝒓𝒌𝒂𝒓 𝒎𝒂𝒏 𝒇𝒆𝒕𝒖𝒓 𝒂 𝑵𝒂𝒋𝒆𝒓𝒊𝒚𝒂.

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN 'Yan sanda sun hallaka dan Achaba har lahira da kulki a jihar Gombe, kan laifin ya ...
17/12/2025

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHIR RAJI'UN

'Yan sanda sun hallaka dan Achaba har lahira da kulki a jihar Gombe, kan laifin ya dauki fasinja "3 in 1" a mashin din shi.

Yanzu haka 'yan Achaba sun toshe hanyar titin Union Bank zuwa sabon Layi domin nuna fushinsu da alhinin abinda ya faru.

Wannan shine Engr Faruk Ahmed shugaban NMDPRA, ɗan Asalin Jahar Sokoto da Dangote yace yana biyawa ma yaran sa su 4 kudi...
16/12/2025

Wannan shine Engr Faruk Ahmed shugaban NMDPRA, ɗan Asalin Jahar Sokoto da Dangote yace yana biyawa ma yaran sa su 4 kudin makarantar secondary ba University ba Dala miliyan 5, kimanin sama da Naira Biliyan 7 a ƙasar Switzerland.

Dangote ya ce Idan ka duba kuɗin shigar sa, ba su dace da irin wannan kuɗin makarantar ba. Ko da ni ne na biya dala miliyan 5 tsawon shekaru shida domin ’ya’yana huɗu, dole ne hukumar haraji ta binciki harajina da nawa nake biya.

Dangote ya ƙara da cewa:
“A Sokoto, inda ya fito, mutane na fama da wahalar biyan kuɗin makaranta na naira 100,000. Yara da dama suna zaune a gida ba sa zuwa makaranta saboda naira 100,000.”

Aliko Dangote ya yi zargin cewa ya dace a binciki Babban Daraktan Hukumar Kula da Harkokin Mai ta Tsakiya da Ta Ƙasa ta Najeriya (NMDPRA), Farouk Ahmed.

ANYI JUYIN MULKIYanzun nan Sojoji a Jamhuriyar Benin mai makwabta da jihar Lagos na Kasar mu Nigeria suke sanar da cewa ...
07/12/2025

ANYI JUYIN MULKI

Yanzun nan Sojoji a Jamhuriyar Benin mai makwabta da jihar Lagos na Kasar mu Nigeria suke sanar da cewa sunyi juyin mulki, sun kifar da Gwamnatin Shugaban Kasa Patrice Talon

Juyin mulkin ya gudana ne karkashin jagorancin Lieutenant Colonel Pascal Tigri wanda ya kwace iko da babbar kafar Television na Kasar, kuma ya sanar da juyin mulkin a yanzu

Tabbas Demokaradiyya na fuskantar barazana a yammacin Afirka

Allah Ka bamu mafita na alheri

Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari a Kano — Sun Sace Mutane 25Daren jiya ya kasance mai firgici a wasu yankuna na jihar Kano,...
01/12/2025

Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari a Kano — Sun Sace Mutane 25

Daren jiya ya kasance mai firgici a wasu yankuna na jihar Kano, bayan da yan bindiga s**a afkawa Unguwar Tsamiya a Faruruwa, da Dabawa — duk a karamar hukumar Shanono.

Mutum 2 sun jikkata, kuma akalla 25 aka yi garkuwa da su.

Abin damuwa kuma shi ne:

▪️ Wannan harin ya faru ne kasa da sa’o’i 24 da irin shi a Yan Kamaye, Tsanyawa, wani gari da ke iyaka da Katsina.
▪️ Al’ummar yankin suna cikin tashin hankali, da rashin tabbas kan abin da ka iya sake faruwa.

29/11/2025

isowar gawar sheikh Dashiru Usman Bauchi wajen da za'abinneshi

YANZU-YANZU: Mataimakin Shugaban Kasar Nigeria, Kashim Shettima, ya isa Jihar Bauchi domin halartar jana'izar marigayi S...
28/11/2025

YANZU-YANZU: Mataimakin Shugaban Kasar Nigeria, Kashim Shettima, ya isa Jihar Bauchi domin halartar jana'izar marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Fitacccen malamin addinin Islama a Najeriya, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya rasu a cikin daren da ya gabata, k**ar yadda ...
27/11/2025

Fitacccen malamin addinin Islama a Najeriya, Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi ya rasu a cikin daren da ya gabata, k**ar yadda wata majiya mai tushe ta tabbatar wa RFI Hausa. Majiyar ta ce za a gudanar da jana'izarsa a gobe Juma'a a garin Bauchi ƙarƙashin jagorancin Sheikh Sharif Ibrahim Saleh. Allah ya yi masa rahama

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka sojoji sunyi juyin mulki a kasar Guinea Bissau, har sojoji sun k**a shugaban kasar.
26/11/2025

DA DUMI-DUMI: Yanzu haka sojoji sunyi juyin mulki a kasar Guinea Bissau, har sojoji sun k**a shugaban kasar.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa sky News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa sky News:

Share