Arewa sky News

Arewa sky News Wannan kafa zata rinka kawo muku labaran gida dana ketare masu inganci gami da ilimantar daku da nishadarwa

22/05/2025

Ivory Coast.

S0j0ji sun karbe kasar.
Fa-ra-nsa ta sake rasa wata kasa a Africa again.

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Sh...
12/05/2025

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Shugaba Ibrahim Traoré zuwa gida, Burkina Faso, bayan halartar bikin cika shekara 80 da fatattakar N**i a Rasha. Masana tsaro sunyi itifakin cewa waɗannan jiragen yakin suna ɗauke da makaman zamani masu linzami kiran hypersonic. Jama'a yanzu duniya, musamman masu mulkin mallaka da ke da burin mamaye duniya, sun fahimci cewa Rasha na daraja Afirka da al'ummanta, musamman shugabanninta masu nagarta irinsu Ibrahim Traoré. Allah Ubangiji Ka tarwatsa azzalumai masu son dakile nahiyar Afrika. Amin

12/05/2025

Jama'a barkanmu da warhaka. Na kalli kai tsaye, yadda jiragen yakin Rasha guda bakwai na zamani kiran SU-57 s**a raka Shugaba Ibrahim Traoré zuwa gida, Burkina Faso, bayan halartar bikin cika shekara 80 da fatattakar N**i a Rasha. Masana tsaro sunyi itifakin cewa waɗannan jiragen yakin suna ɗauke da makaman zamani masu linzami kiran hypersonic. Jama'a yanzu duniya, musamman masu mulkin mallaka da ke da burin mamaye duniya, sun fahimci cewa Rasha na daraja Afirka da al'ummanta, musamman shugabanninta masu nagarta irinsu Ibrahim Traoré. Allah Ubangiji Ka tarwatsa azzalumai masu son dakile nahiyar Afrika. Amin

Yaƙe yaƙe har uku aka gwabza tsakanin Indiya da Pakistan tun bayan da s**a sami yancin kai a shekarar 1947.  Ga shi kuma...
07/05/2025

Yaƙe yaƙe har uku aka gwabza tsakanin Indiya da Pakistan tun bayan da s**a sami yancin kai a shekarar 1947. Ga shi kuma na hudu na kokarin ballewa.

Kashmir yanki ne da ke tsakanin Indiya da kasar Pakistan wadda kasashen biyu s**a shafe shekaru da dama suna rikici dangane da mallakarsa.

Rikicin da aka dade ana gwabzawa kan yankin Kashmir da ta'addanci a kan iyakokin kasashen biyu, shi ne musabbabin rikici tsakanin kasashen biyu, in ban da yakin Indo-Pakistan na 1971, wanda ya faru ne sakamakon tashin hankalin da ya samo asali daga yakin 'yantar da Bangladesh a tsohuwar Pakistan (yanzu Bangladesh ).

Ga duk me bibiyar rikicin dake faruwa yanzu a kasashen indiya da fakistan, bazai kasa sanin rikicin yankin kashmir tsakanin Indiya da makociyarta Pakistan ba. Rikicin neman mallakar yankin tsakanin kasashen biyu ya janyo asarar dinbin al'umma musamman mabiya Addinin Musulunci. Kowace kasa tsakaninsu nason mallakar yankin da yake da yawan al'umma akalla miliyan 69,07,623. Srinagar ita ce yanki mafi yawan jama'a a kwarin Kashmir, tare da mazauna 1,269,751. sannan yanki ne me dinbin arziki musamman ta bangaren noma da sana'oin hannu, da yawon buɗe ido.

Bisa tarihi kasashe uku ne suke rikici akan mallakar yankin, banda Indiya, Pakistan akwai kasar sin (China). Yankin na Kashmir da ake kira Jammu Kashmir yana karkashin ikon Indiya yanzu haka, amma kuma sauran kasashen biyun su ma suna da iko da wasu wuraren. Indiya nada iko da akalla kaso 70, inda ya kunshi Jammu, Jammu ladakh da kuma Siachenglacier. Ita kuma Pakistan tana da iko da kaso 30 daya kunshi Azad Kashmir da Gliqit Baltisan, yayinda China kuma takeda kaso 15 daya kunshi Shashgam Valley da kuma Aksai chin.

Yankin Jammu Kashmir jiha ce karkashin kasar Indiya, amma kuma tanada kwarya-kwaryar 'yancin cin gashin kai, wanda ya kunshi cewar babu wata doka da 'yan majalisun Indiya zasuyi da zatayi amfani a yankin, sai dokar da 'yan majalisun yankin s**ayi. Sannan yankin ne kadai yake da tutar sa ta kashin kansa, wato

Ta tabbata dai yau za'a daura Auran Rarara da Aisha Humaira a Maiduguri. Wane fata zaku musu?
25/04/2025

Ta tabbata dai yau za'a daura Auran Rarara da Aisha Humaira a Maiduguri. Wane fata zaku musu?

23/04/2025

Gwamnan Jihar Delta dake Najeriya Sheriff Oborevwori ya sanar da sauya shekarsa daga PDP zuwa APC. Gwamnan ya ce ya ɗauki matakin ne saboda ci gaban jiharsa sakamakon doguwar tattaunawar da akayi da masu ruwa da tsaki a jihar. Sheriff Oborevwori ya zama gwamnan Delta ne sakamakon tsayar da shi takarar da Jam'iyyar PDP ta yi a zaben shekarar 2023 domin maye gurbin Ifeanyi Okowa da ya kammala wa'adinsa na biyu. Jihar Delta na daya daga cikin tungar Jam'iyyar PDP a siyasar Najeriya, kuma ko a zaben da ya gabata, tsohon gwamnan jihar ne aka ɗauka a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a Jam'iyyar PDP. Masu sanya ido na danganta wannan sauya sheka da nasarar da shugabannin jam'iyyar APC a ƙarƙashin jagaroncin Abdullahi Ganduje ke samu wajen ganin an sake zaben shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a shekarar 2027.

DA DUMI DUMI: Yariman Barci` Na Saudiyya ya cika Shekaru 36 Bayan Fiye da Shekara 20 a kwance Bai farfaɗo Ba, Yarima Al-...
19/04/2025

DA DUMI DUMI: Yariman Barci` Na Saudiyya ya cika Shekaru 36 Bayan Fiye da Shekara 20 a kwance Bai farfaɗo Ba, Yarima Al-Waleed bin Khaled bin Talal, wanda aka fi sani da “Yariman Barci” a fadin duniya ta Larabawa, ya cika shekaru 36 a ranar Juma’a, 18 ga Afrilu, duk da cewa yana cikin dogon suma da ya kwashe fiye da shekaru 20 a ciki.

Ya samu suma ne a shekarar 2005 bayan mummunan hatsarin mota da ya rutsa da shi a birnin London.

A cikin sa’o’i 24 da s**a gabata, ranar zagayowar haihuwarsa ta janyo hankalin mutane da dama a kafar X (Twitter), inda dubban masu amfani da kafar s**a wallafa addu’o’i, fatan alheri da tunatarwa game da wannan lamari da ya zama wata alama ta bangaskiya da jimiri.

Duk da tsawon lokacin da ya dauka a cikin wannan hali, yariman na ci gaba da samun kulawa ta musamman, yana dogara da na’urorin taimaka masa numfashi da abinci ta bututu. A shekara ta 2019, an bayyana cewa ya nuna wasu karancin motsi kamar daga yatsa ko motsa kai kadan, amma ba su nuna cewar ya farfado gaba ɗaya ba.

Yanzu haka yana karɓar kulawa a Cibiyar Lafiya ta Sarki Abdulaziz da ke Riyadh, karkashin kulawar kwararrun likitoci.

Iyayensa, ciki har da mahaifinsa Yarima Khaled bin Talal da mahaifiyarsa Gimbiya Reema bint Talal, na ci gaba da nuna cikakken fata da bege. A baya, Gimbiya Reema ta bayyana cewa “ransa har yanzu yana nan a jikinsa,” yayin da Yarima Khaled—wanda ya ki cire na’urorin taimako—ke ci gaba da tsayawa da yakinin cewa “Wanda Ya raya ransa tsawon wadannan shekaru, Shi ne Zai iya warkar da shi.”

Babu wani sabon bayani na kiwon lafiya da iyalansa s**a fitar dangane da wannan zagayowar haihuwarsa. Sai dai irin yawan goyon bayan da ya samu a kafafen sada zumunta na nuna yadda labarinsa ya ci gaba da zama abin tausayi da haɗin kai ga mutane a sassan yankin.

Masana sun akwai yiwuwar ya farfado bayan dogon lokaci irin wannan abu ne da ba kasafai yake faruwa ba, sai dai suna ci gaba da fatan sabbin ci gaba a ilimin kwakwalwa da jijiyoyi na iya kawo mafita nan

YANZU -YANZU: Rundunar Yan sanda Ta Gayyaci Sarkin Kano sunusi lamido sunusi, akan shirya hawan sallah a Kano.
05/04/2025

YANZU -YANZU: Rundunar Yan sanda Ta Gayyaci Sarkin Kano sunusi lamido sunusi, akan shirya hawan sallah a Kano.

dandazon Bayin Allah Wajan Sallah Jana’iza Ta Dr. Idris Abdul-aziz Kenan Yanzu Haka Daka Jihar Bauchi Alama Ta Uku Kenan...
04/04/2025

dandazon Bayin Allah Wajan Sallah Jana’iza Ta Dr. Idris Abdul-aziz Kenan Yanzu Haka Daka Jihar Bauchi

Alama Ta Uku Kenan Ga Mutuwar Mutumin kirki mumini Wanda Ake Kyautatawa Zato ga Rahamar Allah 🙏🏼❤️🙏🏼

Innah lillahi wa innah ilaihi rajeeun, Allah yayiwa Dr idris Dutsen tanshi rasuwa Allah yagarta masa Yasa jinya yazama k...
03/04/2025

Innah lillahi wa innah ilaihi rajeeun, Allah yayiwa Dr idris Dutsen tanshi rasuwa Allah yagarta masa Yasa jinya yazama kaffara.

29/03/2025

Kasar Saudi Arabia ta bayyana ganin sabon watan Shauwaal. Hukumomin kasar sun bayyana gobe Lahadi a matsayin ranar 'karamar Sallah.

Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'unn 🥲 Wannan yaron da kuke gani kishiyar maman shi neh ta ƙulle shi da ankwa har tsawon...
25/03/2025

Innalillahi wa 'inna ilaihi raji'unn 🥲

Wannan yaron da kuke gani kishiyar maman shi neh ta ƙulle shi da ankwa har tsawon shekaru biyu.🥲

Wai Nikam mata ina tausayin naku yake tafiya neh ?

Allah katsaremuna imaninmu baki daya amm wannan wallahi ba kishi bane jahilci ne tsintsa 👌

Zakariya Muhammad Budu

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa sky News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa sky News:

Share