30/03/2026
ABIN DUBAWA: Akwai Wani Ɓoyayyen Al'amari Tattare Da Wannan Mutumin
Inba haka ba, waya sanar dashi a dan kankanin lokaci, har ya baro inda yake yazo anguwar Rukuba? Ya akayi, ya riga jami'an tsaro isowa gurin? Suwa s**a kawo shi, har ya samu tsaro yafara yada karya a gurin? Shin ko dai yasan za'a aikata hakan ne, ya iso gurin da wuri har ya riga jami'an tsaron gwamnati isowa? Me yasa yake kiran sunan shugaba Bola Tinubu kai tsaye? Sannan waya gaya mai cewa mabiya addinin kirista kadai abin ya shafa?
Sunan'sa Alex Babir, a daga ɓangare, ance shidin 'ɗan mishan' ne, sannan na ɗaya daga cikin waɗan da, aka sanya domin su gayawa duniya cewa ana yiwa mabiya addinin Kirista kisan gilla a Arewacin Najeriya. Ya wanci, zaka ga hotunan Alex Babir da Rev. Dochomo, ɗaya daga cikin maluman Kirista da ya yadda cewa ana yiwa mabiya addinin kisan gilla.
Alex Babir, yakan ziyarci duk inda wani iftila'i ya fadawa mabiya addinin kirista, yayi bidiyo da hotuna tare da yin ƙokarin tabbatar wa duniya cewa ana kashe mabiya addinin kirista, yaje Jahar Filato, Benue, da sassan wasu jahohi a Arewa maso Tsakiya. Anawa tunanin, akwai wani boyayyen al'amari tattare dashi inhar kayi la'akari da yadda ya iso, anguwan Rukuba jiya, mintina kadan bayan harin da wasu yan ta'adda s**a kai, s**a kashe al'umma Kirista da Musulmi.
Sannan, da isar da wajen, babu binkice, ya hau yada labaran karya tare'da kiran sunan shugaba Tunibu cewa ana kashe Kirista a Najeriya. Don haka, lallai wannan mutumin, akwai alamar cewa, yana/suna shirya wata maqarqashiya ne bayan ƙasa domin kawo rashin jituwa Arewa, a tsakanin mabiya addinai, tare da yin ƙurin bata wa gwamnatin Najeriya suna.
Inba haka ba, waya sanar dashi a dan kankanin lokaci, har ya baro inda yake yazo anguwar Rukuba? Ya akayi, ya riga jami'an tsaro isowa gurin? Suwa s**a kawo shi, har ya samu tsaro yafara yada karya a gurin? Shin ko dai yasan za'a aikata hakan ne, ya iso gurin da wuri har ya riga jami'an tsaron gwamnati isowa? Me yasa yake kiran sunan shugaba Bola Tinubu kai tsaye? Sannan waya gaya mai cewa mabiya addinin kirista kadai abin ya shafa?
Gaskiya, ni ina, zargin cewa yasan wani abu dangane da wannan harin, don haka, yana da kyau, mahukunta su gaiyya ce shi, domin ji daga gareshi yadda yasamu damar zuwa gurin, daga faruwar wannan lamarin. In bahaka, zamu cigaba da zargin shi cewa da hannun sa a wannan aika aikan da akayi wa al'umma domin cimma wata manufa nasu.
Ukasha Rabiu Magama
AREWA INFO TV