AREWA INFO TV

AREWA INFO TV Arewa Info Tv Kafa ce da aka Ƙirƙira Domin Yaɗa Sahihan Labarai, Al'adu, Nishaɗi Cikin Harshen Hausa.

ABIN DUBAWA: Akwai Wani Ɓoyayyen Al'amari Tattare Da Wannan MutuminInba haka ba, waya sanar dashi a dan kankanin lokaci,...
30/03/2026

ABIN DUBAWA: Akwai Wani Ɓoyayyen Al'amari Tattare Da Wannan Mutumin

Inba haka ba, waya sanar dashi a dan kankanin lokaci, har ya baro inda yake yazo anguwar Rukuba? Ya akayi, ya riga jami'an tsaro isowa gurin? Suwa s**a kawo shi, har ya samu tsaro yafara yada karya a gurin? Shin ko dai yasan za'a aikata hakan ne, ya iso gurin da wuri har ya riga jami'an tsaron gwamnati isowa? Me yasa yake kiran sunan shugaba Bola Tinubu kai tsaye? Sannan waya gaya mai cewa mabiya addinin kirista kadai abin ya shafa?

Sunan'sa Alex Babir, a daga ɓangare, ance shidin 'ɗan mishan' ne, sannan na ɗaya daga cikin waɗan da, aka sanya domin su gayawa duniya cewa ana yiwa mabiya addinin Kirista kisan gilla a Arewacin Najeriya. Ya wanci, zaka ga hotunan Alex Babir da Rev. Dochomo, ɗaya daga cikin maluman Kirista da ya yadda cewa ana yiwa mabiya addinin kisan gilla.

Alex Babir, yakan ziyarci duk inda wani iftila'i ya fadawa mabiya addinin kirista, yayi bidiyo da hotuna tare da yin ƙokarin tabbatar wa duniya cewa ana kashe mabiya addinin kirista, yaje Jahar Filato, Benue, da sassan wasu jahohi a Arewa maso Tsakiya. Anawa tunanin, akwai wani boyayyen al'amari tattare dashi inhar kayi la'akari da yadda ya iso, anguwan Rukuba jiya, mintina kadan bayan harin da wasu yan ta'adda s**a kai, s**a kashe al'umma Kirista da Musulmi.

Sannan, da isar da wajen, babu binkice, ya hau yada labaran karya tare'da kiran sunan shugaba Tunibu cewa ana kashe Kirista a Najeriya. Don haka, lallai wannan mutumin, akwai alamar cewa, yana/suna shirya wata maqarqashiya ne bayan ƙasa domin kawo rashin jituwa Arewa, a tsakanin mabiya addinai, tare da yin ƙurin bata wa gwamnatin Najeriya suna.

Inba haka ba, waya sanar dashi a dan kankanin lokaci, har ya baro inda yake yazo anguwar Rukuba? Ya akayi, ya riga jami'an tsaro isowa gurin? Suwa s**a kawo shi, har ya samu tsaro yafara yada karya a gurin? Shin ko dai yasan za'a aikata hakan ne, ya iso gurin da wuri har ya riga jami'an tsaron gwamnati isowa? Me yasa yake kiran sunan shugaba Bola Tinubu kai tsaye? Sannan waya gaya mai cewa mabiya addinin kirista kadai abin ya shafa?

Gaskiya, ni ina, zargin cewa yasan wani abu dangane da wannan harin, don haka, yana da kyau, mahukunta su gaiyya ce shi, domin ji daga gareshi yadda yasamu damar zuwa gurin, daga faruwar wannan lamarin. In bahaka, zamu cigaba da zargin shi cewa da hannun sa a wannan aika aikan da akayi wa al'umma domin cimma wata manufa nasu.

Ukasha Rabiu Magama
AREWA INFO TV

Kunga idan Gwamnati Batai Gaggawar Daukar Mataki Akan wannan Agent din na Turawan Yamma ba Wallahi Sai Arewa da Yan Arew...
30/03/2026

Kunga idan Gwamnati Batai Gaggawar Daukar Mataki Akan wannan Agent din na Turawan Yamma ba Wallahi Sai Arewa da Yan Arewa Sun Dandada Kudar Su Hatta Yankin Sudan Sai Tafi Yankin Arewa Kyan Gani da Zaman Lafiya

Harin Ta’addanci da Aka Kai Jiya a Garin Jos Wanda Yai Sanadiyar Mutuwar Mutane da Dama Musulmi da Crista Wanda Kana Gani Kasan Shiryawa Akai Domin Tayar da Rikici na Kabilanci Abun Mamaki Ko 5 Mint Ba Ai Ba wannan Mutumin Yazo ya Kafe Camera Yana Bidiyo

Cikin Bidiyon Yana Kiran Cewa Shugaban Kasa Ya Dauki Mataki Akan Kisan Kare dangi da Musulmi Suke Kokarin Yiwa Cristocin Arewa Tambaya ta Farko Yadda Yai Saurin zuwa Wajan Bayan Faruwar Abun Kana Gani Kasan An Tsara Komai Dashi

irin Yadda Yake Action a Cikin Bidiyo da Jinginawa Musulmi Lefin Kisan Kasan Cewa Akwai Abinda Yake Shirin Faruwa Ya Akai ma Yasan Abun Ya Faru da Yariga Kowa zuwa Wajan har Ya Samu Kwarin Guiwar Kafe Camera Ba Tare da tsoro ba Cikin Dare ? Ya K**ata a K**a wannan Baturan Ayi Kyakyawan Buncike Akan sa

Ya K**ata Kuyi Mana Tagg din duk Wata Hukuma a Najeriya Cikin wannn Post din Sannan Kuyi Share Sako Yaje inda Akeso

TIRKASHI: Wannan mutumin sunansa Alex Barbir, ɗan ƙasar Amurka. Mutane sun ce sun gan shi a rikicin da ya faru a unguwar...
30/03/2026

TIRKASHI: Wannan mutumin sunansa Alex Barbir, ɗan ƙasar Amurka. Mutane sun ce sun gan shi a rikicin da ya faru a unguwar Rukuba a garin Jos, wanda ya jawo rasa rayuka. Hakan tasa ake kiraye-kiraye ga hukumar DSS data bincike shi.

Wannan hoton da kuke gani, na yi screenshot ɗinsa ne a wani bidiyonsa da yake jawabi mai cike da harzuka mutane don ɗaukar fànsa. A gefe guda za ku ga ɗàn fàshin banki Fasto Ezekiel Dachomo, ga kuma jami’an tsaro da sauran mutane duk a wajen.

Duk lokacin da aka samu bata gari suna ƙoƙarin rura wutar rikici cikin al’umma, za ka samu wasu suna ankarar da hukumomi domin ɗaukar mataki a kansu kafin abu ya zo ya fi ƙarfin kuwa, a zo ana budget in billion domin shawo kan matsalar da da an ɗauki mataki tun a farko, abin ba zai kai ga haka ba.

Rikicin addini ya fi rikicin Bóko Haram, bàndits da manoma da makiyaya. Wajibi ne hukumomi su saka ido kan wannan ɗan ƙasar Amûrka kafin ya haddasa rikicin addini a arewacin Nigeria ya kuma silale abunsa ya bar mu da masifa, matsalolin da muke fama da su ma sun yi mana yawa.

Allah ya kawo mana zaman lafiya, ameen.

Othman Othman
AREWA INFO TV

Cikin Hotuna, Manyan Nasarorin da wasu kungiyoyin kwallon kafa s**a samu a Gasar cin kofin Zakarun Nahiyar Turai Zagaye ...
19/03/2026

Cikin Hotuna, Manyan Nasarorin da wasu kungiyoyin kwallon kafa s**a samu a Gasar cin kofin Zakarun Nahiyar Turai Zagaye na 16.

Wannan Fin Karfi ne ko yanayin canjin Wasa ne?

AREWA INFO TV

TIRKASHI: An bude taron cinikayyar kayayyakin gashin kanti na kasar Sin.
19/03/2026

TIRKASHI: An bude taron cinikayyar kayayyakin gashin kanti na kasar Sin.

Azumi Nawa Kuke sa Rai Za'a yi Bana? 29 ko 30
18/03/2026

Azumi Nawa Kuke sa Rai Za'a yi Bana?

29 ko 30

ZARGIN TURSASAWA: ICPC Ta Ce In Janye Daga Siyasar 2027 Kafin Ta Sake Ni — El-Rufai Ya Gayawa KotuTsohon Gwamnan Jihar K...
18/03/2026

ZARGIN TURSASAWA: ICPC Ta Ce In Janye Daga Siyasar 2027 Kafin Ta Sake Ni — El-Rufai Ya Gayawa Kotu

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya zargi jami’an Hukumar Yaƙi da Yi wa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa (ICPC) da ƙoƙarin tursasa shi ya fice daga harkokin siyasa a matsayin sharadin sakin sa daga tsarewa.

Me zaku ce akan wannan zargi da yake yi??

18/03/2026

A Azumin Bana Wane Dare ne ya fi Maku K**a da Daren Laylatul Qadri
???

A Duba Watan Shawwal a Yau Laraba 29 ga Watan Ramadhana - Sarkin MusumiSarkin Musulmi a Nijeriya kuma Shugaban Majalisar...
18/03/2026

A Duba Watan Shawwal a Yau Laraba 29 ga Watan Ramadhana - Sarkin Musumi

Sarkin Musulmi a Nijeriya kuma Shugaban Majalisar Ƙoli ta Addinin Musulunci, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar na III ya buƙaci 'yan ƙasar su soma duban watan Shawwal ranar Laraba.
Sarkin Musulmin ya bayyana haka ne ranar Talata a wata sanarwa da Wazirin Sokoto kuma Shugaban Kwamitin Bayar da Shawara kan Harkokin Addinin Musulunci, Sambo Wali Junaidu ya fitar.
Sanarwar ta ce, an keɓe ranar Laraba 18 ga watan Maris, 2026, wadda ta zo daidai da 29 ga watan Ramadan 1447AH, a matsayin ranar soma duban jaririn watan Shawwal.
Ta buƙaci duk wanda ya ga wata ya sanar da mai unguwa ko dagacinsu domin shi kuma ya sanar da Fadar Sarkin Musulmi.
Kazalika an bayar da lambobin waya ga wanda zai iya kiran Fadar Sarkin Musulmi kai-tsaye idan ya ga wata.

AREWA INFO TV

Kashi 99% na mutane ba ku san ma'anar abin da kuke kira makamin Nukiliya (Nuclear Weapon) ba. Domin ku a tunanin ku fash...
04/03/2026

Kashi 99% na mutane ba ku san ma'anar abin da kuke kira makamin Nukiliya (Nuclear Weapon) ba.

Domin ku a tunanin ku fashewa ce kawai irin ta bama-baman da kuka saba ji.

Misali: Idan har aka kuskura aka saki wannan makamin a tsakiyar birnin Kano, to ku sani ba gini ne kawai zai rushe ba, GOBE ce za ta kare tun kafin ma gari ya waye.

A cikin sakan na farko, za ku ga wani irin haske da ya fi hasken ranar da kuka Saba gani zafi; hasken da zai narkar da idon duk wanda ya kalla kafin ma ya yi tunanin runtse idonsa.

A wannan lokacin, mutanen da ke yawo a Kasuwar Kurmi ko Masallacin Juma’a na Jalli ba za su ma sami damar yin ihu ba. Domin Zafin zai mayar da naman jikinsu iska, sannan shi ma bangon gine ginensu zai zama gari. Ba mutuwa za a yi ba; bacewa za a yi daga doron kasa a cikin kifawar ido.

Daga nan wata mahaukaciyar iska zata ta biyo baya, guguwar da za ta kwashe manyan benayen dake kan titin IBB Way da Zoo Road kamar yadda yaro yake iya rushewa gidansa na kasa.

Karfen service da manyan bishiyoyin dake Nassarawa GRA za su karye kamar ashana, motoci su rinka tashi a sama kamar takardu.

Gadar Lado da ta kofar Nassarawa za su narke su zama gari, su hade da jinin mutane su zama abu guda. Duk wani abin da kuke alfahari da shi na ginin zamani, zai zama tarkacen da ba shi da sunan kirki a cikin sakan talatin.

Duk da Hakan fa wannan shi ne farkon masifar. Domin bayan hayaki ya turnuke sararin samaniyar Kano, wani irin bakar kankara zata fara fadowa daga sama, guba ce mai dauke da sinadarin radiation da zai gurbata kowane daki da kowane lungu na cikin birni.

Ruwan fanfo zai koma sanadin mutuwa, kasar da kuke shuka abinci a kanta za ta koma kabari da babu dama a binne kowa. Wadanda s**a tsira da ransu za su rinka yawo a cikin rugujajjen birnin, idanunsu zasu makance, fatar jikinsu ta daddago, su ta rinka neman neman guraren da babu su.

Daga nan kuma, sai wani shiru ya biyo baya. Ranar da kuke gani za ta bace a bayan wani bakin gajimare na tsawon shekaru, damina za ta tsaya, iska za ta daskare, amfanin gona zai matu. Yunwa za ta kwashe sauran mutanen da wutar ba ta cinye ba, yayin da kasashen duniya za su kalli Kano a matsayin wani Yankin Mutuwa da ba za a iya takawa ba tsawon zamani.

Ko bayan shekaru hamsin, 'ya'yan da za a Haifa a kewayen garin za su zo da nakasa da cututtukan da ba su san asalinsu ba, domin wannan makamin ba birni yake rushewa ba, asalin jinin dan Adam yake lalatawa.

Wannan ba abin tsoratarwa ba ne, gaskiya ce wadda double standard din siyasar duniya take kokarin boyewa.

Idan har kana tunanin makamin nukiliya don kariya ne akayishi, to ka koma ka bude littafin tunaninka ka kara karantawa. Domin An halicce ka ne ka zama Khalifa, ba jahili mai neman hanyar kashe kansa da zuri'arsa ba.

Idan har wannan rubutun ya sa ka ji tsoron yaki kuma ka daraja zaman lafiya, to na cika aiki na.

Tura wa abokanka 3 da kake gani suna wasa da maganar tsaro, watakila su gane cewa babu wanda zai tsira idan nuclear ta tashi.

AREWA INFO TV

DA ƊUMI-ƊUMI: Rana ta Kasu Kashi Biyar a Birnin Jos dake Jihar Filato Lamarin da ya Sanya Mutane Mamaki matuka.AREWA INF...
04/02/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Rana ta Kasu Kashi Biyar a Birnin Jos dake Jihar Filato Lamarin da ya Sanya Mutane Mamaki matuka.

AREWA INFO TV

TIRKASHI: An kawo ƙarshen makircin yahudawa, an karyasu, an ƙwace musu wani babban makami da suke garkuwa dashi(Jeffrey ...
03/02/2026

TIRKASHI: An kawo ƙarshen makircin yahudawa, an karyasu, an ƙwace musu wani babban makami da suke garkuwa dashi

(Jeffrey Epstein) wani shahararren matsafi ne, ɗan luwaɗi, mazinaci dake lalata da ƙananan yara

Jeffrey Epstein yana dagacikin manyan mafiyans dake juya duniya

Jeffrey Epstein yanada bidiyos da hotunan manyan shugabannin duniya, sarakunan duniya, mawaƙan duniya, da attajiran duniya dake lalata da ƙananan yara da tsafi acikin gidansa dake kan wani tsibirin ɓoye.

Yahudawa sun mallaki wannan sirrin, shiyasa suke baiwa shugabannin turai umarni tare da juya ƙasashen turai

Yahudawa na amfani da wanna sirrin wurin baiwa shugabannin amerika umarnin yaƙar ƙasashen larabawa kamar irinsu (Iran, Palestine, Syria, Iraq, Libya, Lebanon da sauransu

Duk wanda ya bayyana adawa da yahudawa, sai suyi barazanar fitarda sirrinsa

Zuwa yanzu an fitarda wannan sirrin, duniya tasan komai, saboda haka yahudawa basuda wani sirrin yiwa duniya barazana, bayarda umarni ko ƙarfin iko.

Mafiyawan manyan duniya yan iska ne

Mafiyawan sarakunan ƙasashen larabawa yan iska ne

Mafiyawan attajiran duniya yan iska ne

Mafiyawan mawaƙan duniya da celebrities yan iska ne

Ansamu laifuka sama da 23,000 acikin katafaren tsibirin wannan matsafin (Jeffrey Epstein)

An samu ƙyallen kiswah na rigar kaaba 🕋 acikin wannan tsibirin, wanda ake zargin an aika masa ne domin aikata wani tsafi.

Ansamu gawarwakin mutane dayawa acikin wannan tsibirin.

AREWA INFO TV

Address

Kano
80026

Telephone

+2348081217123

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA INFO TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AREWA INFO TV:

Share