31/05/2026
TCN Ta Sanar Da Katse Wutar Lantarki A Kano, Katsina Da Jigawa A Yau Lahadi
Kamfanin Tunkudo Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya sanar da cewa za a katse wutar lantarki a wasu jihohin Arewacin Najeriya guda biyar a ranar Lahadi, 31 ga watan Mayun 2026, domin gudanar da aikin gyaran shekara-shekara a wani muhimmin layin tunkudo wutar lantarki.
A cikin wata sanarwa da Babbar Manajar Hulɗa da Jama'a ta kamfanin, Ndidi Mbah, ta fitar ranar Asabar, TCN ta ce aikin zai gudana ne a layin Mando zuwa Kumbotso mai ƙarfin 330kV daga ƙarfe 9:00 na safe zuwa 4:00 na yamma.
Kamfanin ya bayyana cewa aikin gyaran ya zama dole domin sauya wani sashe na wayar lantarki da ya lalace a hasumiyar T187 da ke kan hanyar layin, domin tabbatar da inganci da dorewar samar da wutar lantarki.
TCN ta ce sakamakon aikin, Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) ba zai samu damar karɓar wuta daga cibiyar tunkudo wutar ba a lokacin da ake gudanar da aikin.
Hakan na nufin cewa al'ummomin da ke jihohin Kano, Katsina da Jigawa za su fuskanci katsewar wutar lantarki na wucin gadi, yayin da wasu sassan jihohin Bauchi da Yobe ma za su shiga cikin yankunan da abin zai shafa.
Baya ga haka, garin Gazaoua da ke makwabciyar Jamhuriyar Nijar, wanda ke amfana da wutar lantarki daga Najeriya, shi ma zai fuskanci irin wannan katsewar.
Kamfanin ya bukaci al'umma da su yi haƙuri da wannan matsala ta ɗan lokaci, yana mai jaddada cewa aikin gyaran na da muhimmanci wajen tabbatar da ingantaccen tsarin tunkudo wutar lantarki da rage matsalolin da ka iya tasowa a gaba.
Sai dai TCN bai bayyana takamaiman lokacin da za a dawo da wutar lantarki a yankunan da abin ya shafa bayan kammala aikin ba, sai dai ya ce ana sa ran komai zai koma yadda yake da zarar an kammala gyaran.
Jaridar Arewa