Sharhi

Sharhi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sharhi, Media/News Company, No. 12 Zoo Road Kano, Kano.

Sharhi International Limited (RC: 7452688) is a CAC-registered media company in Nigeria, providing radio, TV, and digital content to inform, educate, and entertain audiences with trusted news, culture, and innovation.

Wata Sabuwa : Yar takarar gwamna na jam’iyyar AAC a Jihar Anambra, Chioma Ifemeludike, ta jawo hankalin jama’a a kafafen...
29/10/2025

Wata Sabuwa : Yar takarar gwamna na jam’iyyar AAC a Jihar Anambra, Chioma Ifemeludike, ta jawo hankalin jama’a a kafafen sada zumunta bayan fitar da sabbin hotunan kamfen ɗinta da s**a janyo ce-ce-ku-ce.

DA ƊUMI-ƊUMI : Shugaba Tinubu Ya Cire Sunan Maryam Sanda Cikin Jerin Sunayen Masu Laifi Da Ya Yiwa AfuwaShugaban Kasar N...
29/10/2025

DA ƊUMI-ƊUMI : Shugaba Tinubu Ya Cire Sunan Maryam Sanda Cikin Jerin Sunayen Masu Laifi Da Ya Yiwa Afuwa

Shugaban Kasar Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya cire sunan Maryam Sanda daga cikin jerin masu laifi da zai yiwa afuwa.

Wannan na cikin wani sabon jerin sunayen mutanen da aka rubuta, wanda shugaba Tinubu zai yi wa afuwa, sai dai babu sunan Maryam Sanda a ciki.

GARGADI: Ya Kamata Masu Birkitawa Min Kwakwalwa Ta Hanyar Zolayata Da Suke Yi Su Daina, Domin Kudin Da Nake Siyan Magani...
29/10/2025

GARGADI: Ya Kamata Masu Birkitawa Min Kwakwalwa Ta Hanyar Zolayata Da Suke Yi Su Daina, Domin Kudin Da Nake Siyan Magani A Dawanau Ya Kai Tiriliyan Uku, Shi Ya Sa Yanzu Ban Cika Shiga Cikin Mutane Ba, Cewar A.A Rufai Bilget

Kotu Ta Yanke Wa Barayin Kebil Hukuncin Shekara 2 Da Wata 10 A Gidan Yari A KanoA wata koton shari`iar musulunci dake un...
29/10/2025

Kotu Ta Yanke Wa Barayin Kebil Hukuncin Shekara 2 Da Wata 10 A Gidan Yari A Kano

A wata koton shari`iar musulunci dake unguwar Danbare a birnin jihar kano ta yankewa wasu matasa biyu hukuncin daurin shekara biyu da wata goma bisa k**asu laifin satar kebil na wutar lantarki daga transfoma,ba tare das zabin tara ba.

Rahotanni sun ce asirin barayin ya tono ne alokacin da barayin suke kokarin raba kudin yayin da jama`a mazauna unguwar naibawa yamma s**am gano su s**a mika su zuwa ga hukuna

Da dumi'dumi: DSS sun k**a mai amfani da kafar sada zumunta da ya kira sojoji su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu. Huku...
29/10/2025

Da dumi'dumi: DSS sun k**a mai amfani da kafar sada zumunta da ya kira sojoji su kifar da gwamnatin Shugaba Tinubu.

Hukumar DSS ta k**a wani matashi mai suna Innocent Chukwuma wanda ya wallafa a dandalin X (Twitter) kira ga rundunar soji da su kifar da gwamnatin Najeriya.

An ce Chukwuma yana zaune ne a Oyigbo, jihar Rivers, inda jami’an tsaro s**a cafke shi. Rundunar soji ta musanta batun cewa ana shirin juyin mulki, tana mai cewa “labari ne na ƙarya.”

Gini Mai Hawa Uku Ya Ruguje a Accra, Ghana — An Ceto Mutane 14Rikici ya ɓarke a Accra bayan wani gini mai hawa uku da ak...
29/10/2025

Gini Mai Hawa Uku Ya Ruguje a Accra, Ghana — An Ceto Mutane 14

Rikici ya ɓarke a Accra bayan wani gini mai hawa uku da ake ci gaba da ginawa ya ruguje, lamarin da ya jefa ma’aikata da mazauna yankin cikin tashin hankali.

Rahotanni sun bayyana cewa ginin na kamfanin Fabrico Builders ne, kuma ya rufta ne yayin da aikin ke gudana. Hukumar kashe gobara ta Ghana ta tabbatar da ceto mutane 14 da s**a makale a cikin tarkon ginin da ya rugume.

Hukumomi sun ce ana ci gaba da bincike domin gano musabbabin rugujewar da kuma tabbatar da cewa babu wani da ya rage a cikin baraguzan.

Sanata Barau I. Jibrin CFr, ya saka solar street lights sama da guda ɗari biyu ako wacce ƙaramar hukumar dake Kano ta'ar...
29/10/2025

Sanata Barau I. Jibrin CFr, ya saka solar street lights sama da guda ɗari biyu ako wacce ƙaramar hukumar dake Kano ta'arewa. A ƙoƙarin na maida Kano ta'arewa birni, da kuma ƙara inganta tsaron rayuka da dukiyoyin su.

Barau Reporters

Yaron Da Ya Dinga Yin Shìgaŕ Kwàilàyè Yanà Dàmfaŕàr Mazà 'Yàn KudadeBayan dubuñ yaron mai suna Dahiru ta cika, inda yake...
28/10/2025

Yaron Da Ya Dinga Yin Shìgaŕ Kwàilàyè Yanà Dàmfaŕàr Mazà 'Yàn Kudade

Bayan dubuñ yaron mai suna Dahiru ta cika, inda yake yin shigar mata da lalle da sarƙar wuya, yana amfani da sunan Surayya, a jawaban sa ya ce ya yi samari da dama, inda ya cutar da wasu don haka yana neman yafiyarsu.

Sannan Dahiru ya kara da cewa rashin kulawa da ake yi masa ne ya sa shi shiga wannan harkar har ya fara yaudarar maza. Domin a cewarsa yanzu haka bai san inda mahaifiyarsa take ba tun bayan da aka ce masa ta yi aure a wani gari da bai sani ba. Kuma mahaifinsa ya rasu.

Wata Sabuwa :Gwamnatin Nijar,Ta kafa kwamiti na musamman afadin kasar domin tantance farashin gidajen haya a kasar.
28/10/2025

Wata Sabuwa :Gwamnatin Nijar,Ta kafa kwamiti na musamman afadin kasar domin tantance farashin gidajen haya a kasar.

Da Dumi Dumi -Tsohon Saurayin Yar Guda Ya Bayyana......Ayayin da aketa cecekuce akan auren yar guda da mai wushirya Sai ...
28/10/2025

Da Dumi Dumi -Tsohon Saurayin Yar Guda Ya Bayyana......

Ayayin da aketa cecekuce akan auren yar guda da mai wushirya Sai ga tsohon saurayin ta ya bayyana inada yace "Tun farko muna soyayya na ce ki zo mu yi aure kika ce ke ba za ki auri jinsinmu ba wai ke sai dogo,"To yanzu ga abinda dogon ya yi miki, sakon Sidi Auwal Ga 'Yar Guda

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya aika da wasika ga majalisar dattawa domin neman amincewar ta da sabbin hafsoshin tsar...
28/10/2025

Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya aika da wasika ga majalisar dattawa domin neman amincewar ta da sabbin hafsoshin tsaron da ya nada kwanan nan.

Majalisar zata fara tantance su nan bada jimawa ba kafin tabbatar da su bisa doka.

A karo na goma,  Hisbah ta sake daƙile yunƙurin safarar ƴan mata a Kano Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake dakile yunk...
28/10/2025

A karo na goma, Hisbah ta sake daƙile yunƙurin safarar ƴan mata a Kano

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta sake dakile yunkurin safar 'yan mata daga jihar zuwa wasu garuruwan da ƙasashe domin aikata badala da abubuwan da basu dace ba.

Mataimakin Babban Kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano Dakta Mujahideen Aminudeen ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya aiko Daily Nigerian Hausa inda ya ce a wannan karon sun k**a wani mai suna Umar Bala da ya yi yunkurin safarar mata 3.

Acewar Mujahideen, wannan ne karo na 10 da hukumar ke dakile safarar 'yan mata.

"Waɗanda muka k**a, sun kai su Guda 3, na hudun shi ne mai safarar su, mai suna Umar Bala mai shekaru 40"

Malamin ya bayyana cewa matan sun fito ne daga jihohin Yobe da Borno da Katsina.

Hukumar ta bayyana cewa bayan bincike tuni ta mika su zuwa ga hukumar NAPTIP.

Sannan ya yi kira ga iyaye da su rike amanar 'ya'yansu ta hanyar kula dasu ba tare da barinsu suna gararanba ba.

Daily nigerian hausa

Address

No. 12 Zoo Road Kano
Kano
700214

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhi:

Share