Sharhi

Sharhi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sharhi, Media/News Company, No. 12 Zoo Road Kano, Kano.

Sharhi International Limited (RC: 7452688) is a CAC-registered media company in Nigeria, providing radio, TV, and digital content to inform, educate, and entertain audiences with trusted news, culture, and innovation.

Na Bawa Tijjani Gandu Kudi Naira Milyan Goma Ya Rabawa Mawaƙa Da Ƴaan Midiya Ya Cinye, Amma Wai Har Da Shi A Maganar Mas...
01/08/2026

Na Bawa Tijjani Gandu Kudi Naira Milyan Goma Ya Rabawa Mawaƙa Da Ƴaan Midiya Ya Cinye, Amma Wai Har Da Shi A Maganar Masu Amana, Idan Kuma Ya Musanta Ina Da Risit Na Alat Ɗin Kuɗin, Inji Kakakin Gwamnan Kano, Sanusi Bature Dwakin Tofa

Sojoji Sun Dakile Yunkurin Garkuwa Da  Mutane, Sun Ceto Matafiya 31 a BornoDakarun Operation HADIN KAI sun dakile yunƙur...
01/08/2026

Sojoji Sun Dakile Yunkurin Garkuwa Da Mutane, Sun Ceto Matafiya 31 a Borno

Dakarun Operation HADIN KAI sun dakile yunƙurin garkuwa da mutane da mayaƙan Boko Haram/ISWAP s**a yi tare da ceto fararen hula 31 a jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:45 na yammacin ranar 31 ga Yuli, 2026 a kan hanyar Buratai zuwa Kamuya a ƙaramar hukumar Biu. Dakarun rundunar musamman ta 135 Special Forces Battalion sun gano ‘yan ta’addan ta hanyar sa ido kai tsaye yayin da suke tare motoci huɗu na fararen hula suna garkuwa da fasinjojin cikinsu.

Bayan samun bayanan sirri, dakarun sun bi sahun ‘yan ta’addan zuwa yankin Mangari–Dora inda s**a yi musayar wuta da su. Hakan ya tilasta wa ‘yan ta’addan barin mutanen da s**a sace da kuma motocin huɗun kafin su tsere cikin daji.

An ceto dukkan mutane 31 ba tare da wata illa ba, sannan an kwato motocin cikin ƙoshin lafiya. Daga bisani an raka waɗanda aka ceto zuwa Buratai domin ci gaba da tafiyarsu cikin aminci.

Mu Gayawa Kanmu Gaskiya, Kwatanta Malamin Addini Da Mashayin Gìya Saboda Siyasa Wuce Gona Da Iri Ne. Siyasa Ba Hauka Ba ...
31/07/2026

Mu Gayawa Kanmu Gaskiya, Kwatanta Malamin Addini Da Mashayin Gìya Saboda Siyasa Wuce Gona Da Iri Ne. Siyasa Ba Hauka Ba Ce, Inji Rahama Abdulmajid

Ku Dinga Yabawa Jami'an Sojojinmu A Koda Yaushe, Saboda Suna Matuƙara Ƙoƙari, Saƙon Shugaba Tinubu Ga Ƴan Nijeriya
30/07/2026

Ku Dinga Yabawa Jami'an Sojojinmu A Koda Yaushe, Saboda Suna Matuƙara Ƙoƙari, Saƙon Shugaba Tinubu Ga Ƴan Nijeriya

Ƴan Najeriya sun zaɓe ka ne don ka yaƙi ƴan ta'adda ba ƴan adawa ba - ADC ga TinubuJam'iyyar ADC ta bukaci Shugaba Bola ...
30/07/2026

Ƴan Najeriya sun zaɓe ka ne don ka yaƙi ƴan ta'adda ba ƴan adawa ba - ADC ga Tinubu

Jam'iyyar ADC ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya mayar da hankali wajen magance matsalar tsaro da ke addabar Najeriya maimakon fara fafutukar siyasar zaben 2027.

A cikin wata sanarwa da Sakataren yaɗa labarai na jam'iyyar, Bolaji Abdullahi, ya fitar, ADC ta ce an zabi Tinubu ne domin ya yaki 'yan ta'adda, masu garkuwa da mutane da 'yan bindiga, ba domin yakar jam'iyyun adawa ba.

Jam'iyyar ta bayyana haka ne bayan kalaman da shugaban ya yi cewa a shirye yake ya "yi fada har karshe" a siyasa, tana mai cewa k**ata ya yi ya fi mayar da hankali kan matsalar tsaro, musamman bayan harin da ya yi sanadin mutuwar akalla mutum 30 a kauyen Naridon da ke karamar hukumar Kauru ta jihar Kaduna.

ADC ta zargi gwamnatin Tinubu da gaza kare rayuka da dukiyoyin al'umma cikin fiye da shekaru uku da ta shafe kan mulki, tana mai cewa nasarar zabe tana samuwa ne ta hanyar kyakkyawan aiki, ba kalaman siyasa ba.

Jam'iyyar ta kara da cewa manyan abokan hamayyar shugaban kasa su ne ta'addanci, garkuwa da mutane da rashin tsaro, tare da yin kira gare shi da ya ba su fifiko maimakon mayar da hankali kan siyasar zaben 2027.

Daily Nigerians Hausa

Nijeriya da Canada na tattaunawa don fara zirga-zirgar jiragen sama kai tsaye tsakanin kasashen biyuDCL Hausa
30/07/2026

Nijeriya da Canada na tattaunawa don fara zirga-zirgar jiragen sama kai tsaye tsakanin kasashen biyu

DCL Hausa

2027: Gwamnan Kaduna Uba Sani ya aiyana Jerry Adams a matsayin mataimakinsa a takaraGwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba San...
28/07/2026

2027: Gwamnan Kaduna Uba Sani ya aiyana Jerry Adams a matsayin mataimakinsa a takara

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya bayyana Shugaban Hukumar Tara Kuɗaɗen Shiga ta Jihar Kaduna (KADIRS), Jerry Adams, a matsayin wanda zai yi takarar mataimakin gwamna tare da shi a zaɓen gwamna na shekarar 2027.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Uba Sani ya ce zaɓin Adams ya yi daidai da manufofin gwamnatinsa na adalci, haɗin kai da kuma bai wa kowa dama ba tare da nuna bambanci ba.

Gwamnan ya bayyana Jerry Adams a matsayin gogaggen jami'in gwamnati kuma ƙwararre a harkar haraji, yana mai cewa ya taka muhimmiyar rawa wajen inganta aikin KADIRS, lamarin da ya ƙara wa jihar kuɗaɗen shiga na cikin gida tare da ba gwamnati damar zuba jari a fannonin ilimi, lafiya, ababen more rayuwa da noma.

Uba Sani ya yi kira ga al'ummar Kaduna da su mara wa tikitin baya, yana mai jaddada cewa a duba wannan zaɓi a matsayin matakin ƙarfafa haɗin kai da ci gaban jihar, ba tare da la'akari da bambancin addini, ƙabila ko yanki ba.

Daily Nigerians Hausa

Ba za mu bari wani ɗan Nijeriya ya kwana da yunwa ba - Oluremi Tinubu Uwargidan Shugaban Nijeriya, Oluremi Tinubu, ta ce...
28/07/2026

Ba za mu bari wani ɗan Nijeriya ya kwana da yunwa ba - Oluremi Tinubu

Uwargidan Shugaban Nijeriya, Oluremi Tinubu, ta ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu za ta ci gaba da ƙara ƙoƙarin magance yunwa da tamowa ga yara ta hanyar kafa rumbunan abinci domin kananan yara a shirye-shiryen rabon abinci karkashin shirin Renewed Hope Initiative (RHI) da gwamnati ta samar.

DCL Hausa

Yadda Aka Hallaka Dalibin Jami'ar Jos Kan Zargin Satar Wayar Iphone 12 Wani matashi mai suna Ibrahim Mbaya, ɗan shekara ...
28/07/2026

Yadda Aka Hallaka Dalibin Jami'ar Jos Kan Zargin Satar Wayar Iphone 12

Wani matashi mai suna Ibrahim Mbaya, ɗan shekara 25, wanda ya kammala karatu a Jami'ar Jos (UNIJOS) kuma fitaccen mai yin tallan kaya (model), ya rasu bayan da ake zargin wasu matasa sun yi masa dukan tsiya kan zargin satar wayar iPhone a birnin Jos, jihar Filato.

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Filato ta tabbatar da k**a mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin. Kakakin rundunar, SP Alfred Alabo, ya ce an kai Mbaya Asibitin Koyarwa na Jami'ar Jos (JUTH), inda likitoci s**a tabbatar da rasuwarsa.

A cewar 'yan sanda, binciken farko ya nuna cewa an yi wa marigayin dukan ne bayan an zarge shi da satar wayar salula, maimakon a miƙa shi ga jami'an tsaro domin gudanar da bincike bisa doka.

An miƙa waɗanda aka k**a zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) domin ci gaba da bincike, yayin da ake ci gaba da neman sauran waɗanda ake zargin sun tsere bayan aukuwar lamarin.

Rundunar 'yan sandan ta yi Allah wadai da abin da ta kira ɗaukar doka a hannu (jungle justice), tare da jan hankalin jama'a da su riƙa kai rahoton duk wanda ake zargi da aikata laifi ga jami'an tsaro maimakon hukunta shi da kansu.

📌 Rundunar ta ce ana ci gaba da bincike kan lamarin.

Rana 24

DA ƊUMI ƊUMI: Dan Gwagwarmaya Omoyele Sowere ya daga jaka me taken “Tinubu Must Go” a safiyar Yau Talata.
28/07/2026

DA ƊUMI ƊUMI: Dan Gwagwarmaya Omoyele Sowere ya daga jaka me taken “Tinubu Must Go” a safiyar Yau Talata.

Address

No. 12 Zoo Road Kano
Kano
700214

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhi:

Shortcuts

Share