Sharhi

Sharhi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Sharhi, Media/News Company, No. 12 Zoo Road Kano, Kano.

Sharhi International Limited (RC: 7452688) is a CAC-registered media company in Nigeria, providing radio, TV, and digital content to inform, educate, and entertain audiences with trusted news, culture, and innovation.

An Daura Auren Jarumar Kannywood Radiya Jibril A Yau Lahadi
31/05/2026

An Daura Auren Jarumar Kannywood Radiya Jibril A Yau Lahadi

DA ƊUMI-ƊUMI: Ministan Tsaro, IGP, Da NSA Sun Isa Oyo Kan Sace Ɗalibai Da Malamai 46Wata tawaga da Shugaba Bola Ahmed Ti...
31/05/2026

DA ƊUMI-ƊUMI: Ministan Tsaro, IGP, Da NSA Sun Isa Oyo Kan Sace Ɗalibai Da Malamai 46

Wata tawaga da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura zuwa Jihar Oyo ta isa garin Ogbomoso a yankin Kudu maso Yammacin Najeriya, domin kai ziyara zuwa ƙauyukan Esiele da Yawota da ke Ƙaramar Hukumar Oriire, inda wasu mahara ɗauke da makamai s**a kai hari kan makarantu uku tare da yin garkuwa da kusan ɗalibai da malamai 46.

Tawagar ta haɗa da Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro, Nuhu Ribadu; Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila; Ministan Tsaro, Christopher Musa; Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe; Sufeto Janar na 'Yan Sanda, Tunji Disu; da mai taimaka wa Shugaban Ƙasa kan harkokin yaɗa labarai, Sunday Dare.

An ce tawagar za ta tantance halin da ake ciki, ta gana da al'ummomin da lamarin ya shafa, tare da duba matakan tsaro domin tabbatar da ceto waɗanda aka sace da kuma hana sake afkuwar irin wannan hari a yankin.

TCN Ta Sanar Da Katse Wutar Lantarki A Kano, Katsina Da Jigawa A Yau Lahadi Kamfanin Tunkudo Wutar Lantarki na Kasa (TCN...
31/05/2026

TCN Ta Sanar Da Katse Wutar Lantarki A Kano, Katsina Da Jigawa A Yau Lahadi

Kamfanin Tunkudo Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya sanar da cewa za a katse wutar lantarki a wasu jihohin Arewacin Najeriya guda biyar a ranar Lahadi, 31 ga watan Mayun 2026, domin gudanar da aikin gyaran shekara-shekara a wani muhimmin layin tunkudo wutar lantarki.

A cikin wata sanarwa da Babbar Manajar Hulɗa da Jama'a ta kamfanin, Ndidi Mbah, ta fitar ranar Asabar, TCN ta ce aikin zai gudana ne a layin Mando zuwa Kumbotso mai ƙarfin 330kV daga ƙarfe 9:00 na safe zuwa 4:00 na yamma.

Kamfanin ya bayyana cewa aikin gyaran ya zama dole domin sauya wani sashe na wayar lantarki da ya lalace a hasumiyar T187 da ke kan hanyar layin, domin tabbatar da inganci da dorewar samar da wutar lantarki.

TCN ta ce sakamakon aikin, Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) ba zai samu damar karɓar wuta daga cibiyar tunkudo wutar ba a lokacin da ake gudanar da aikin.

Hakan na nufin cewa al'ummomin da ke jihohin Kano, Katsina da Jigawa za su fuskanci katsewar wutar lantarki na wucin gadi, yayin da wasu sassan jihohin Bauchi da Yobe ma za su shiga cikin yankunan da abin zai shafa.

Baya ga haka, garin Gazaoua da ke makwabciyar Jamhuriyar Nijar, wanda ke amfana da wutar lantarki daga Najeriya, shi ma zai fuskanci irin wannan katsewar.

Kamfanin ya bukaci al'umma da su yi haƙuri da wannan matsala ta ɗan lokaci, yana mai jaddada cewa aikin gyaran na da muhimmanci wajen tabbatar da ingantaccen tsarin tunkudo wutar lantarki da rage matsalolin da ka iya tasowa a gaba.

Sai dai TCN bai bayyana takamaiman lokacin da za a dawo da wutar lantarki a yankunan da abin ya shafa bayan kammala aikin ba, sai dai ya ce ana sa ran komai zai koma yadda yake da zarar an kammala gyaran.

Jaridar Arewa

Ba na cikin tawagar Seyi Tinubu inji mawaki DavidoYa yi martani ne ga wata daga cikin masu tofa albarkacin bakinsu bayan...
31/05/2026

Ba na cikin tawagar Seyi Tinubu inji mawaki Davido

Ya yi martani ne ga wata daga cikin masu tofa albarkacin bakinsu bayan wasu kalaman s**ar su kansu mawaka da ya yi, inda ya ce ba sa kyauta wa ƴan Nijeriya saboda rashin fadin halin da kasar ke ciki a wakokin da suke.

DCL Hausa

Shekarun baya da ₦5 million wani babban kuɗi ne, amma yanzu kusan duk wani mai wayar Android yana da ita.Inji Engr Adam ...
31/05/2026

Shekarun baya da ₦5 million wani babban kuɗi ne, amma yanzu kusan duk wani mai wayar Android yana da ita.

Inji Engr Adam Muhammad Mukhtar

Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matarsa A Daidai Gari...
30/05/2026

Ƴan Bindiga Sun Sace Tsohon Kakakin Sojan Kasan Najeriya, Mejo Janar Rabe Abubakar (Mai Ritaya) Da Matarsa A Daidai Garin Matazu Akan Hanyarsa Ta Zuwa Katsina, Yau Asabar

Majiya: Sahara Reporters

An Sauya Alkalin Da Zai Saurari Ƙarar Kalubalantar Shugabancin African Democratic CongressBabban Alkalin Kotun Tarayya y...
30/05/2026

An Sauya Alkalin Da Zai Saurari Ƙarar Kalubalantar Shugabancin African Democratic Congress

Babban Alkalin Kotun Tarayya ya sauya alkalin da zai saurari ƙarar da tsohon Mataimakin Shugaban ADC na ƙasa, Nafiu Bala, ya shigar yana kalubalantar shugabancin jam’iyyar ƙarƙashin David Mark.

An mayar da shari’ar ga Mai Shari’a Peter Lifu domin ci gaba da sauraron ƙarar.

Nafiu Bala na neman kotu ta hana David Mark, Rauf Aregbesola da sauran mambobin kwamitin riƙon ƙwarya na jam’iyyar gudanar da harkokin shugabanci, yana mai cewa nadin nasu ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ADC da kuma dokar zaɓe.

An kuma haɗa da ADC, Independent National Electoral Commission da tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, cikin waɗanda ake ƙara.

Sauyin alkalin ya biyo bayan umarnin da kotun ƙoli ta bayar na a gaggauta sauraron shari’ar. A baya, Mai Shari’a Emeka Nwite ya dage sauraron ƙarar har sai an samu cikakken kwafin hukuncin kotun ƙoli.

Daily news hausa

WATA SABUWA: Wike ya yi barazanar kwace filayen otal-otal da wuraren taro da ke ba haramtattun ƙungiyoyi da jam'iyyu hay...
29/05/2026

WATA SABUWA: Wike ya yi barazanar kwace filayen otal-otal da wuraren taro da ke ba haramtattun ƙungiyoyi da jam'iyyu haya

Na Gama Kashe Kudi Sama Da Naira Milyan Dari Kuma Na Rasa Tikiti, Ina Ba Za Ta Sabu Ba, Inji Wani Dan Majalisa Daga Jiha...
29/05/2026

Na Gama Kashe Kudi Sama Da Naira Milyan Dari Kuma Na Rasa Tikiti, Ina Ba Za Ta Sabu Ba, Inji Wani Dan Majalisa Daga Jihar Imo, Hon Ezechukwu Obinna, Wanda Ya Nuna Fushinsa Ga Jam'iyyar APC.

Uwargidan tsohon shugaban ƙasa, marigayi Buhari, Hajiya Aisha Muhammadu Buhari, tare da ɗanta, Yusuf Buhari, ɗan takarar...
29/05/2026

Uwargidan tsohon shugaban ƙasa, marigayi Buhari, Hajiya Aisha Muhammadu Buhari, tare da ɗanta, Yusuf Buhari, ɗan takarar majalisar tarayya a Jihar Katsina, Jiya Alhamis a Daura.

Address

No. 12 Zoo Road Kano
Kano
700214

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhi:

Share