Sharhi

Sharhi An bude Sharhi domin Samun ingantattun Labarai,masu ilimantarwa, nishadantarwa, fadakarwa, gami da shirya shirye masu mahimmancin gaske.

Da dumi'dumi: Kwamarad Lawan Habibu dutse wanda ya tattaki daga jihar Jigawa zuwa kano domin jinjina da nuna goyon baya ...
09/08/2025

Da dumi'dumi: Kwamarad Lawan Habibu dutse wanda ya tattaki daga jihar Jigawa zuwa kano domin jinjina da nuna goyon baya ga Gwamnan jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da zaman dirshan a kofar gidan gwamnatin a yunkurin sa na ganawa da gwamna Abba Kabir Yusuf, tun farko dai Kwamarad ya bayyana Gwamna Abba amatsayin Gwamna mafi Tausayin talakawa da kudanci dasu wanda hakan yasa ya yi tattaki domin jinjina gare shi.

Kwamarad ya bayyana ire Iren soyayyar da yake wa Gwamnan jihar Kano ce tasa ya zauna kuma ba zai tashi ba har sai ya samu ganawa da gwamnan ko da kuwa zai kai shekara guda ba tare da ganin gwamnan ba.

“Zan mutu ne a ranar Lahadi, bayan na halarci coci, na ci sakwarar da nake so, sannan in rabu da duniya ba tare da wani ...
09/08/2025

“Zan mutu ne a ranar Lahadi, bayan na halarci coci, na ci sakwarar da nake so, sannan in rabu da duniya ba tare da wani ciwo ba”. — In ji Babban Malamin Addinin Kirista Fasto Adeboye.

Yanzu_Yanxu: Yan sandan jahar Kaduna sun gano tsaffin bama bamai a hannun Yan jari bola dake jahar.Daga Albishr hausa
09/08/2025

Yanzu_Yanxu: Yan sandan jahar Kaduna sun gano tsaffin bama bamai a hannun Yan jari bola dake jahar.

Daga Albishr hausa

Majalisar Dokokin Jihar Neja Ta Nemi A Haramta bikin Sign-Out A Makarantun jihar Niger.Majalisar Dokokin Jihar Neja ta r...
09/08/2025

Majalisar Dokokin Jihar Neja Ta Nemi A Haramta bikin Sign-Out A Makarantun jihar Niger.

Majalisar Dokokin Jihar Neja ta roƙi Gwamna Umaru Bago da ya haramta shagulgulan “sign-out” da “Markers’ Day” a dukkan makarantu na gwamnati da na kudi a jihar.

Wannan na zuwa ne bayan mamba mai wakiltar Mazabar Tafa, Muhammad Idris, ya gabatar da kudiri inda ya bayyana cewa shagulgulan da aka fara a matsayin na ban kwana da juna yanzu sun rikide zuwa ɗabi’u marasa kyau da rashin kunya, abin da ke barazana ga tarbiyya da ilimi.

‘Yan majalisar sun amince da kudirin baki ɗaya, tare da yin kira ga gwamnati ta hanzarta aiwatar da dokar hana hakan.

Mataimakiyar Kakakin Majalisar, Afiniki Dauda, ta ce za ta yi aiki tare da Gwamna da Ma’aikatar Ilimi don tabbatar da aiwatar da wannan doka cikin gaggawa.

Haka kuma, majalisar ta amince da gyara dokar kafa Minna Institute of Technology and Innovation domin ta dace da bukatun zamani da ci gaban ilimi.

Wata Sabuwa: Wani Fasto ya fito da wata karamar sa, ya sanar da ranar da zai mutu Babban Faston cocin RCCG Enoch Adeboye...
08/08/2025

Wata Sabuwa: Wani Fasto ya fito da wata karamar sa, ya sanar da ranar da zai mutu

Babban Faston cocin RCCG Enoch Adeboye ya yi hasashen ranar da zai mutu, inda yace zai mutu a ranar Lahadi bayan ya ci sakwara.

Adeboye ya yi magana ne a ranar Alhamis a lokacin da yake huɗuba a babban taron cocin kashi na 73.

Da yake gabatar da huɗubar sa, Adeboye ya yi kira gare su da su ci gaba da addu'a akan kada su samu cutar da zasu kasa warkewa, yana mai cewa yanzu ya maida hankali ga yin karatuka akan rayuwa.

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Ya Buƙaci Peter Obi Da Ya Dawo PDP, Don Haɗa Kai Wajen Ciyar Da Ƙasa Gaba.Gwamna Bala...
08/08/2025

Gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad Ya Buƙaci Peter Obi Da Ya Dawo PDP, Don Haɗa Kai Wajen Ciyar Da Ƙasa Gaba.

Gwamna Bala Muhammad ya yi wannan kiran ne ya yin da ya karɓi bakwancin tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar Peter Obi a gidan Gwamnatin jihar, ya yin ziyarar da ya kai yau Juma'a kamar yadda Punch ta ruwaito.

Fadar Shugaban Ƙasa ta yi Allah wadai da bayanan da jaridar Daily Trust ta fitar inda ta bayyana cewa akwai yunwa a Naje...
08/08/2025

Fadar Shugaban Ƙasa ta yi Allah wadai da bayanan da jaridar Daily Trust ta fitar inda ta bayyana cewa akwai yunwa a Najeriya, tana mai bayyana cewa jaridar ta ƙi fito da ƙoƙarin da gwamnati ke yi domin magance wahalhalu da ake fuskanta a ƙasar.

Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan Kafafen yada labarai Sunday Dare ya bayyana cewa bayanan da jaridar ta fitar ba gaskiya bane sannan akwai ƙari a cikin abubuwan da ta bayyana.

Dare yace Fadar Shugaban Ƙasa na murna da caccakar ta daga kafafen yaɗa labarai, amma dole abubuwan da za'a caccake ta ya kasance akwai gaskiya a ciki, bawai son zuciya ba.

An bawa Yan jaridu damar ganawa Da Omoyele Sowore a Shelkwatar Yan sanda Najeriya dake Abuja. Yanzu. Cikakken bayani nan...
08/08/2025

An bawa Yan jaridu damar ganawa Da Omoyele Sowore a Shelkwatar Yan sanda Najeriya dake Abuja. Yanzu. Cikakken bayani nan tafe.

DAGA📸 Abdul Journalist 1

Farfesa Isa Ali Pantami ya ziyarci iyalan Marigayi Muhammadu Buhari a gidansu na Kaduna, domin ganin halin da suke ciki.
08/08/2025

Farfesa Isa Ali Pantami ya ziyarci iyalan Marigayi Muhammadu Buhari a gidansu na Kaduna, domin ganin halin da suke ciki.

Address

No. 12 Zoo Road Kano
Kano
700214

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Sharhi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Sharhi:

Share