28/05/2026
Amirul Hajj na Kano Ya Jagoranci Taya Alhazai Murnar Sallah a Mina
Amirul Hajj na Jihar Kano kuma Sarkin Gaya, Alhaji Dr. Aliyu Ibrahim Abdulkadir, ya jagoranci tawaga zuwa rumfunan alhazan jihar da ke Mina a kasar Saudiyya domin isar da sakon taya su murnar Sallah.
Tawagar ta hada da mataimakin Amirul Hajj kuma Sarkin Karaye, Alhaji Muhammad Maharaz Karaye, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano tare da wasu mambobin hukumar da kuma Darakta Janar na hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle.
Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da shugaban tawagar yada labarai ta aikin Hajjin Kano na 2026, Mustapha Muhammad, ya fitar.
Da yake jawabi ga alhazan jihar, Amirul Hajj Dr. Aliyu Ibrahim Abdulkadir ya yabawa alhazan bisa yadda suke gudanar da ibadunsu cikin tsari da natsuwa, tare da rokon su da su ci gaba da yi wa Jihar Kano da Najeriya addu’o’in zaman lafiya da ci gaba.
Har ila yau, ya bukaci alhazan da su yi wa gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, addu’ar samun nasara tare da dorewar zaman lafiya, arziki da bunkasar tattalin arziki a jihar.
A wani taro daban kuma, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Kano, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ya sanar da cewa Riyal 200 na kasar Saudiyya da gwamnan jihar ya yi alkawarin bai wa alhazai za a raba musu ta hannun jami’an cibiyoyi bayan sun koma Makkah.
Ya kuma tabbatar wa alhazan cewa hukumar za ta ci gaba da samar da ayyukan jin dadi domin tabbatar da walwalarsu a wuraren ibada masu tsarki.
Tun da farko, manyan malamai uku — Sheikh Aminu Daurawa, Sheikh Tijjani Bala Kalarawi da Sheikh Abubakar Kandahar — sun gabatar da wa’azuzzuka kan muhimmancin aikin Hajji, darussansa da falalolinsa ga alhazai.
Malaman sun kuma yi addu’ar Allah Ya karbi aikin Hajjin alhazan tare da gafarta musu kura-kuransu.