Gargai TV

Gargai TV Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Gargai TV, Media/News Company, Kano.

Cikin Hotuna: Yadda Engr. Dr. Rabiʼu Musa Kwankwaso Jagora Jam'iyyar NNPP na Ƙasa ya sauka a Filin Jirgin Sama na tunawa...
01/01/2026

Cikin Hotuna:

Yadda Engr. Dr. Rabiʼu Musa Kwankwaso Jagora Jam'iyyar NNPP na Ƙasa ya sauka a Filin Jirgin Sama na tunawa da Marigayi Malam Aminu Kano yayin da ya dawo daga Birnin Ikoye

Hotuna: Saifullahi Hassan

LABARI: ’Yan sanda sun dakatar da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu bisa umarnin kotu.Rundunar ’Yan Sandan...
01/01/2026

LABARI: ’Yan sanda sun dakatar da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu bisa umarnin kotu.

Rundunar ’Yan Sandan Najeriya (NPF) ta dakatar da aiwatar da dokar samun lasisin gilashin mota mai duhu, bisa bin umarnin kotu.

An shirya fara aiwatar da dokar ne a ranar 2 ga Janairu, 2026.

Wannan mata akwai tsoron cin haram, ta tsinci N330m a account dinta na banki, ta mayar ma banki su a nemi mai suWannan i...
01/01/2026

Wannan mata akwai tsoron cin haram, ta tsinci N330m a account dinta na banki, ta mayar ma banki su a nemi mai su

Wannan ita ce Aisha Isah Yelwa, ‘yar asalin Jihar Neja daga Ƙaramar Hukumar Lapai, wadda ta nuna gagarumar gaskiya da amana bayan da ta mayar wa wani banki Naira miliyan 330 da aka yi kuskuren turawa zuwa asusun ajiyarta.

Rahotanni sun bayyana cewa, bayan Aisha ta samu saƙon shigowar kuɗin, ba ta sanar da kowa ba, sai dai nan take ta tashi zuwa reshen First Bank da ke garin Lapai domin sanar da su kuskuren da aka yi.

Bayan tabbatar da lamarin, bankin ya karɓi kuɗin gaba ɗaya daga hannunta.

Matakin da Aisha Isah Yelwa ta ɗauka ya ja hankalin jama’a, inda da dama ke yabawa da jinjina mata bisa gaskiya, rikon amana da tsoron Allah da ta nuna.

Yadda Wata Ibo Ta Bude Makarantun Koyan Al'qur'ani Ga Wanda S**a Musulunta a Yankin Kudu Maso Gabas."Wannan mafarki ba n...
31/12/2025

Yadda Wata Ibo Ta Bude Makarantun Koyan Al'qur'ani Ga Wanda S**a Musulunta a Yankin Kudu Maso Gabas.

"Wannan mafarki ba na jin daɗi bane ko neman suna — amma mafarki ne mai girma da nauyi.

Mafarki ne na samun filin ƙasa kaɗan inda za a gina ajujuwa guda 5 ko 6 — makaranta mai sauƙi da tsarki, inda ake karatun Al-Qur’ani cikin salama, kuma yara su ji daɗin koyon Kalmar Allah cikin tsari da tausayi.

Na fara da ’ya’yana biyu kacal. Ba tare da kudi ba, ba tare da taimako ko goyon baya ba — sai dai niyya da tawakkali.

Yau, da rahamar Allah, wannan karamin mataki ya haifar da ɗalibai sama da 90, kuma 11 daga cikinsu sun kammala mataki na farko na Qur’ani.

Kowane harafi da suke karantawa, kowace aya da suke haddacewa, kyauta ce daga Allah, ba nasara ta kaina ba. Alhamdulillah kullum.

Akwai kalubale. Ba ni da yalwar kudi. Akwai ranakun da nauyin wannan amanar ke damuna sosai. Amma ina tuna kaina da dalilin da ya sa na fara — da kuma Wanda nake yi donSa.

Allah Ya ce:
"In kun ba Allah bashi mai kyau, zai ninka muku, kuma Ya gafarta muku."

Ya kuma yi alkawari:
In kun taimaki Allah, zai taimake ku kuma Ya tsayar da kafafunku da ƙarfi."*

Annabi (SAW) ya ce:
"Sadaka ba ta rage dukiya ba."

HOTUNA: Yadda Sojojin rundunar Operation Hadin Kai s**a k**a wani mutum ɗauke da kayan haɗa bam a babban Masallacin Juma...
31/12/2025

HOTUNA: Yadda Sojojin rundunar Operation Hadin Kai s**a k**a wani mutum ɗauke da kayan haɗa bam a babban Masallacin Juma’a na garin Banki da ke ƙaramar hukumar Bama a Jihar Borno.

HOTUNA: Kotu Ta Tura Tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami Da Matarsa Da Dansa Zuwa Gidan Yari Bisa Zargin Babakere D...
30/12/2025

HOTUNA: Kotu Ta Tura Tsohon Ministan Shari'a, Abubakar Malami Da Matarsa Da Dansa Zuwa Gidan Yari Bisa Zargin Babakere Da Dukiyar Kasa

Me za ku ce?

ALLAH SARKI: Yadda Shahararrun Mutanen Ingila S**a Gamu Da Hàdari A NijeriyaDaga Sa'adatu Baba Ahmad, Daga IngilaYanzu k...
30/12/2025

ALLAH SARKI: Yadda Shahararrun Mutanen Ingila S**a Gamu Da Hàdari A Nijeriya

Daga Sa'adatu Baba Ahmad, Daga Ingila

Yanzu kusan dai wannan labarin na hatsarin fitaccen ɗan damben Britaniya a Najeriya, shi ne labari ma fi shahara a manyan gidajen jaridun ƙetare, yanayin dai yadda aka fito da shi daga motar ne dai ba ambulance, ba kurar ɗaukar mara lafiya da ma’aikatan lafiya da sauransu ya fi ɗagawa mutane hankali a nan Ingila.

Sannan zarge-zarge sun yi nisa ana cewa ragowar biyun ma da s**a rasu ba su sami kulawar gaggawa ba ne.

Duk da kulawar jaje da shugaban shugaban ƙasar Najeriya Asiwaju ya fitar da gaggawa da wasu shahararrun mutane k**ar Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da sauransu wannan bai sanyaya zuciyar ƙasashen waje ba.

Dukka matasan uku ‘yan ƙasar Ingila ne, sai dai ko wannensu yana da tushe daga wasu ƙasashe.

Anthony Joshua haifaffen Wartford ne a yankin Hertfordshire ta ƙasar Ingila, uwassa Yeta ‘yar Najeriya ce, Babansa Robert ruwa biyu ne ɗan yankin Ireland ne da kuma Nigeria. Ya yi matuƙar sabawa da Nigeria da mutanen Nijeriya domin wasu rahotanni sun ce ya taɓa zama na tsawon lokaci a Najeriya kafin afkuwar wannan hatsarin na yau. Shi dai yanzu ya bubbugu tare da wasu raunika ne, yanzu yana asibiti, Allah Ya ba shi lafiya.

Ragowar mutane biyu da s**a rasu a yayin hatsarin akwai Sina Ghami ya kasance mai horar da ƙarfi da juriya na Joshua tsawon fiye da shekaru 10. Hakanan yana daga cikin masu kafa Evolve Gym a London.

Ghami kwararre ne a fannin kiwon lafiya da motsa jiki wanda ya ƙware a fannin raunukan ƙashi da motsa jiki na gyara. Ya yi aiki tare da 'yan wasan kwaikwayo da manyan shahararru a cikin National Football League (NFL), National Basketball Association (NBA), da kuma kungiyar kwallon ƙafa ta Michigan State University.

Abdullatef Latif "Latz" Ayodele ƙwararre ne wajen wasan motsa jiki, shi ne mai horar da Joshua na ƙashin kai. Sha'awarsa ga motsa jiki ta bayyana a shafukan sa na sada zumunta, haka nan kuma sadaukarwarsa ga addinin Musulunci. Ya karɓi Musulunci a shekarar 2012 ya kasance mai bayar da gudummowa ga matasa da aiyukan Sadaqatul-Jariya iri-iri daban-daban a wurare daban-daban. Yana yawaita cewa ‘babbar albarkata ita ce shiga musulunci “ wannan shi ne abinda ya rubuta a cikin wani sakon da ya maƙala a shafinsa tun shekarar 2020.
Asali, Kevin Ayodele, Latif ya buga wasan ƙwallon ƙafa ne, ya buga wasan kwallon ƙafa ne ga Aylesbury United, Tooting & Mitcham United, Hillingdon Borough, AFC Hayes, Chalfont Wasps da Northwood. bayan ya karɓi addinin Musulunci kuma ya koma suna Abdul Latif – wanda aka fi sani da Latz.

Ban samo takamemen a wacce jiha ya gina makaranta ba, sai dai na ga wani bidiyonsa inda yake cewa ya samar da kujeru da tebura na ajujuwa da kuma wajen motsa jiki da duk abinda ake buƙata don bunƙasa ilimi da jin daɗin matasa, kuma ya fara samar da ayyukan jin ƙai manya ga marasa ƙarfi tun a 2019.

Tallafin Lateef na kusan ƙarshe shi ne, ya bayar da kekunan motsa jiki guda ɗari. Allah Ya ji ƙansa.

Wannan hatsari yak**ata ya zama wani darasi ga Najeriya na samar da kayan aikin gaggawa a lokutan hatsari, domin ire-iren waɗannan abubuwa sun sha faruwa da gama-garin mutane ba tare da wani ya damu ba amma yanzu duk ɗaukin da gama garin mutane da jami’an tsaro su ka kai yayin hatsarin, bai hana mutanen ƙasashen waje kuka da ƙorafin wasarere da rayuka ba. Babbar tambayar da wasu ke yi mana anan shi ne wai dama babu ambulance babu stretchers na ɗaukar mara lafiya a Najeriya ne? Amsar dai ko akwai to ba ta yi rana ba gaskiya.

Sa'adatu Baba Ahmad ɗaliba ce mai karatun degree na uku a Jami’ar Bedfordshire da ke Ingila.

Da Dumi Dumi: Efcc Ta Shigar Da Tuhume-tuhume 16 Kan Malami, Ɗansa Da Abokinsa...Hukumar EFCC ta shigar da tuhume-tuhume...
30/12/2025

Da Dumi Dumi: Efcc Ta Shigar Da Tuhume-tuhume 16 Kan Malami, Ɗansa Da Abokinsa...

Hukumar EFCC ta shigar da tuhume-tuhume guda 16 a gaban kotu, tana zargin tsohon Ministan Shari’a kuma Tsohon Lauyan Ƙasa (AGF), Abubakar Malami, tare da ɗansa da wani abokin hulɗarsa, da aikata laifin wanke kuɗaɗe.

A cewar EFCC, ana zargin wanke kuɗi ta asusun bankuna da dama, ta hanyar amfani da harkokin kadarori (gidaje/filaye) wajen ɓoye kuɗaɗe, hada-hadar da ake zargin sun saba wa dokar yaƙi da cin hanci

Shari’ar na ƙara ɗaukar zafi, yayin da jama’a ke jiran shin kotu za ta tabbatar da zargin, ko Malami da sauran waɗanda ake tuhuma za su wanke kansu?

Mikiya dai tana nan tana sanya domin ganin yadda shari'ar zata wakana, kudai kawai ku cigaba da bibiyarmu...

YANZU-YANZU: ‘Yan Majalissun Jihar Kano Ƙarƙashin Jagorancin Shugabansu Rt Hon Jibrin İsmail Falgore sun isa gidan Sanat...
29/12/2025

YANZU-YANZU: ‘Yan Majalissun Jihar Kano Ƙarƙashin Jagorancin Shugabansu Rt Hon Jibrin İsmail Falgore sun isa gidan Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a wannan daren.

📸-Inuwa Kwankwaso

DA DUMI-DUMI: An hango jirgin leƙen asirin Amurka yana ta zagaye dajin Sambisa yanzu haka.
27/12/2025

DA DUMI-DUMI: An hango jirgin leƙen asirin Amurka yana ta zagaye dajin Sambisa yanzu haka.

DA ƊUMI ƊUMI: Jami'an Tsaron Najeriya Na Cigaba Da Bincike Domin Tabbatar Da Harin Amurka Kan Najeriya Wanda Ya Kai Jiha...
26/12/2025

DA ƊUMI ƊUMI: Jami'an Tsaron Najeriya Na Cigaba Da Bincike Domin Tabbatar Da Harin Amurka Kan Najeriya Wanda Ya Kai Jihar Sokoto.

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta k**a fitattun ‘yan ta’adda biyu, Usman Siddi da aka fi sani da Siddi, da Shehu Mo...
26/12/2025

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce ta k**a fitattun ‘yan ta’adda biyu, Usman Siddi da aka fi sani da Siddi, da Shehu Mohammed da aka fi sani da Gide, da ke tada hankali a jihohin Zamfara, Neja da Kwara.

📸: Shafi Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Gargai TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Gargai TV:

Share