HARIS HAUSA TV

HARIS HAUSA TV HARIS HAUSA TV Kafar samun Sahihan labarin Abin dake faruwa ciki da wajan kasar mu da duniya baki daya 🌍🌎🌏

Tinubu ya sanya hannu a dokar da ta hana sojoji aikata baɗalaShugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu a kan wani k...
12/01/2025

Tinubu ya sanya hannu a dokar da ta hana sojoji aikata baɗala

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanya hannu a kan wani kundin dokoki da ya hana sojojin Nijeriya aikata dukkan nau'in baɗala da su ka haɗa da luwaɗi, maɗigo, zinace-zinace, lalata da dabbobi, daudu da sauran dangogin su da ake ganin sun saba wa ka’idojin aikin soja.

Hakazalika dokokin sun hana sojojin ƙasar huda jiki, zanen fata, rashin ɗa'a, da kuma buguwa da barasa a yayin aiki ko bayan aiki.

Wannan umarnin na kunshe ne a sashe na 26 na kundin dokokin aikin soja da aka yi wa kwaskwarima, wanda shugaba Bola Tinubu ya sanya wa hannu a ranar 16 ga Disamba, 2024.

A kwafin takardar kundin da wakilan gidan jaridu s**a samu a jiya Asabar, wani bangare na kundin na cewa, “An yi ga jami’in soja ya shiga harkar luwadi, madigo, da kuma lalata da dabba.

"Ba zai kasance cikin, ko shiga ayyukan ƴan madigo, luwadi, zina da daudanci ba, gami da shiga ƙungiyar LGBTQ ba.

“Bai k**ata jami’in soja ya riƙa huda jiki da kuma yi wa wani bangare na jikinsa zane ba. Jami'i ba zai aikata ko wanne nau'i na rashin ɗa'a, fada, ko wani aiki dai zubar masa da mutunci a idon al'umma ba. Kada jami'i ya bugu a kowane lokaci ko a lokacin aiki ko bayan tashi daga aiki."

Hakanan kuma dokokin sun haramta wa ko wanne soja shiga harkar kwartanci ko neman matan ma'aikatan da ke ƙarƙashin ofis ɗin su da sauran su.

Sai dai Rahotanni sunce ba a bayyana hukunce-hukunce ko matakan ladabtarwa ga duk wani ma'aikacin da ya karya dokokin ba.

Ƙudurin dokar haraji zai ƙara jefa Al'umarmu cikin talauci - Gwamnatin jahar KanoGwamnatin jihar Kano ta bayyana hamayya...
01/01/2025

Ƙudurin dokar haraji zai ƙara jefa Al'umarmu cikin talauci - Gwamnatin jahar Kano

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana hamayyarta ga ƙudirin dokar harajin da yanzu haka ke gaban majalisar dokokin Najeriya wanda shugaba Tinubu ya aike wa da majalisar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda mataimakinsa, Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta ne ya bayyana haka a yayin bikin murnar shiga sabuwar shekarar 2025 a dandalin Ma'ahaha da ke birnin Kano.

Wata sanarwa da ke ɗauke da sa-hannun mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba ta ce gwamnan ya ce "wannan kundin dokar harajin ba za ta magance matsalar tattalin arziƙinmu ba. Kano tana hamayya da wannan ƙudiri da zai shafi walwalaw al'umma."

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnatin tarayya ke ci gaba da tankiyya tsakaninta da gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad wanda ya soki kudirin Kai tsaye

Jihar Zamfara za ta iya dogara da kanta ba sai ta jira gwamnatin tarayya ba - Gwamna Dauda LawalGwamnan ya ce idan za ay...
20/12/2024

Jihar Zamfara za ta iya dogara da kanta ba sai ta jira gwamnatin tarayya ba - Gwamna Dauda Lawal
Gwamnan ya ce idan za ayi amfani da albarkatun kasa da Allah Ya baiwa jihar to ba su bukatar dogara ga arzikin kasa don samun kudin shiga.

Yanzu yanzu a cikin a daren nan Rahotanni sun nuna cewa wata tankar man fetur ta k**a da wuta yayin sauke man a gidan ma...
17/12/2024

Yanzu yanzu a cikin a daren nan Rahotanni sun nuna cewa wata tankar man fetur ta k**a da wuta yayin sauke man a gidan mai na NNPC da ke kan titin Ibrahim Taiwo a birnin Kano.
Sai dai majiyoyi sun ce ba wanda wutar ta shafa kuma tuni an shawo kanta.

Allah Ya kiyaye gaba.

Yadda zazzafar muhawara ta kaure tsakanin Barau  Ndume a majalisa kan kudurin dokar haraji na Tinubu An samu takaddama m...
27/11/2024

Yadda zazzafar muhawara ta kaure tsakanin Barau Ndume a majalisa kan kudurin dokar haraji na Tinubu

An samu takaddama mai zafi a majalisar dattawa yayin da Sanata Ali Ndume ya yi martani ga Mataimakin Shugaban Majalisar, Barau Jibrin, kan kokarin gayyatar kwararru kan haraji da jami'an gwamnati zuwa zauren majalisa ba tare da sanarwa ba.

Rikicin ya ta'allaka ne kan Dokokin Gyaran Haraji, inda wasu ƴan majalisa daga yankin arewa s**a bayyana rashin amincewarsu.

Rikicin ya fara ne lokacin da Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar, Opeyemi Bamidele, ya sanar da wani ba-zata game da dakatar da ajandar ranar don bai wa kwararrun haraji da jami’ai, ciki har da Shugaban Hukumar FIRS, damar gabatar da jawabi ga 'yan majalisa kan Dokokin Gyaran Haraji da ake takaddama kansu.

Duk da haka, Sanata Abdul Ningi ya nuna adawa da hakan bisa ka’idojin Majalisar Dattijai. Ya ce ka’idojin ba su ba da izini ga kowa ya yi magana a zauren majalisa ba sai tsoffin Shugabannin Kasa, tsoffin Shugabannin Majalisar Wakilai, da tsoffin sanatoci. Ningi ya jaddada cewa irin wannan bayani daga kwararru ya dace a yi shi ne a matakin kwamitocin majalisa, ba a taron majalisar gaba daya ba, kasancewar dokokin majalisar ba su amince da irin wannan ba.

Sanata Barau Jibrin, wanda ke jagorantar zaman majalisa, ya mayar da martani ta hanyar cewa Dokokin Gyaran Haraji suna da muhimmanci ga kasa kuma tuni Majalisar Wakilai ta yi aiki a kansu. Ya yi bayanin cewa bai wa kwararru damar yin magana a zauren majalisar zai taimaka wa 'yan Najeriya su fahimci abinda dokokin s**a kunsa. Daga nan sai ya yi fatali da maganar Ningi.

Sanata Ndume, cikin bacin rai, ya fada wa shugaban zaman majalisar da cewa, “Za ku iya cimma muradinku, amma ni zan yi magana.” Ya kuma kara da cewa, “Za ku iya amfani da guduma, amma ni zan yi amfani da muryata.”

Rikicin ya dada ta’azzara lokacin da Sanata Ndume, cikin takaici, ya jagoranci wasu 'yan majalisa daga arewa wajen ficewa daga zaman majalisar a matsayin alamar rashin jin

Yin Amfani Da Carbi Ba Laifi Ba Ne, Kuma Babu Wani Daga Cikin Magabata Da Ya Haramta Hakan, Inji Sheik Sani Rijiyar Lemo...
20/11/2024

Yin Amfani Da Carbi Ba Laifi Ba Ne, Kuma Babu Wani Daga Cikin Magabata Da Ya Haramta Hakan, Inji Sheik Sani Rijiyar Lemo

Shehin ya kawo hujja da cewa idan mutum ya kasance mai yawan zikiri kuma yana so ya cimma wani adadi na wurudi, ba zai yiwu ya yi da hannu ba, dole sai da carbi.

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya mayar da Auwalu Danladi Sankara mukamin kwamishina bayan kotu ta wanke shi dag...
19/11/2024

Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya mayar da Auwalu Danladi Sankara mukamin kwamishina bayan kotu ta wanke shi daga zargin lalata da matar aure.
A ranar Litinin ne wata babbar kotun Shari'ar Musulunci ta jihar Kano ta wanke Auwalu Sankara daga tuhumar da aka yi masa bayan samun rahoto daga ofishin 'yan sanda da kuma ofishin Kwamishinan Shari'a na jihar Kano.
Kotun ta ce duka rahotannin biyu sun nuna cewa babu gamsassun hujjoji da s**a tabbatar da zargin da aka yi wa Auwalu Danladi Sankaran.

Da dumi'dumi: 'Yan Majalisar Wakilai na Arewacin Nageriya sun Goyi bayan Kwankwaso kan chanja fasalin Haraji da Gwamnati...
19/11/2024

Da dumi'dumi: 'Yan Majalisar Wakilai na Arewacin Nageriya sun Goyi bayan Kwankwaso kan chanja fasalin Haraji da Gwamnatin Shugaba Tinubu ke shiryawa Wanda s**a Ce koma baya ne ga Arewa

'Yan majalisar wakilai daga yankin arewacin kasar sun nuna damuwa kan wasu kudirori hudu na sake fasalin haraji da majalisar dokokin kasar ke ci gaba da nazari a kai.

Sun yi wannan jawabi ne a wani zaman tattaunawa da majalisar wakilai ta shirya tare da mambobin kwamitin shugaban kasa kan manufofin kasafin kudi da sake fasalin haraji a ranar Litinin.

Kudurorin, musamman gyaran da ake shirin yi wa rabon harajin haraji (VAT), ya haifar da cece-kuce.

Sauran sun hada da: Dokar Kafa Haraji ta Najeriya, wadda za ta soke dokar Hukumar tara haraji ta kasa (FIRS) da kuma kafa hukumar tattara kudaden shiga ta Najeriya (NRS), da kuma dokar kafa hukumar tattara kudaden shiga, wadda za ta samar da kotun haraji.

idan ba'a manta ba a farko makon nan ne Kwankwaso ya soki Shirin Gwamnatin Tarayya tare da s**a kan cewa Gwamnatin na da wani Shiri na Kai Arewacin Nageriya zuwa kasa.

Shekara 8 kana mulki amma ƴan Kwankwasiyya su ka kwace gwamnati a hannunka - Adeleke ya yi wa Ganduje shagubeGwamnan Jih...
18/11/2024

Shekara 8 kana mulki amma ƴan Kwankwasiyya su ka kwace gwamnati a hannunka - Adeleke ya yi wa Ganduje shagube

Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, ya caccaki Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, kan maganganunsa game da shirin jam’iyyar na kwace ikon jihohin Osun da Oyo bayan nasararta a zaben gwamna na Jihar Ondo.

Jaridar The Nation ta rawaito cewa, bayan Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana Lucky Aiyedatiwa a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a Ondo, Ganduje ya bayyana cewa APC ta fara shirye-shiryen kwace ikon jihohin Oyo da Osun, wadanda a halin yanzu ke karkashin ikon jam’iyyar PDP.

A martaninsa, Adeleke ya ce kalaman na Ganduje wata manufa ce ta tada zaune tsaye a yankin Kudu maso Yamma tare da haddasa rikici.

Ta bakin mai magana da yawunsa, Olawale Rasheed, Adeleke ya bayyana a a yau Litinin cewa maganganun da shugaban APC ya yi sun saɓawa dimokuradiyya da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke ikirarin tsayawa kai.

Adeleke ya yi wa Ganduje shagube, yana mai cewa ya kasa kare Jihar Kano daga hannun kungiyar Kwankwasiyya, wadda ta kayar da jam'iyyar da duk da yana mulkin jihar tsawon shekaru takwas.

“Idan har Ganduje na son Shugaban Kasa da gaske, me ya sa yake kokarin tada hankali a yankin Kudu maso Yamma, inda Shugaban Kasa ya fito, ta hanyar yin barazanar karya dokar zabe da kuma tauye hakkin masu zabe?”

17/11/2024

Labaran Safiyar Lahadi 17/0/11/2024 CE - 15/05/1446AH Ga Takaitattun Labaran.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo, sun ceto wata jaririya ‘yar watanni 14 mai suna Grace Osamagbe, wadda ‘yar aikin gidansu ta sace ta.

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima, ya karɓi baƙuncin tawagar da ke shirya fim ɗin “Mai Martaba” ƙarƙashin jagorancin ministar fasaha da al'adu da yawon shakatawa Hannatu Musawa.

Ana ci gaba da ƙirga ƙuri'un zaɓen gwamnan jihar Ondo.

‘Yan sanda a jihar Legas sun ƙi karɓar cin hancin Naira Miliyan 174 daga hannun wani ɗan damfara mai suna Patrick Akpoguma.

Jami’an SSS sun k**a wani da buhun kuɗi a wurin zaɓe a Akure jihar Ondo.

A zaben jihar Ondo, alamu sun fara nuna ɗan takarar APC Lucky Aiyedatewa na kan gaba.

Biden zai yi ganawar ƙarshe a matsayin shugaban ƙasa da shugaban China.

Masu zanga-zangar ƙin gwamnati a Abkhazia ta Georgia sun mamaye majalisa.

Ƙungiyar likitoci a Sudan tace mutum 17 sun mutu wasu sama da 20 kuma sun ɓace a wani hari da dakarun ƙungiyar RSF s**a kai kan wani ƙauye a kudancin jihar Gezira.

Harin Isra'ila kan makaranta a Gaza ya kashe mutum goma da raunata da dama.

Kotun Afirka ta Kudu ta ba da umarnin ga 'yan sanda na su kawo karshen killace masu hakar ma'adinai.

Mutane 8 ne s**a mutu, 17 sun jikkata, a harin wuka a wata makaranta a China.

An jefa abubuwan fashewa guda biyu kusa da gidan Netanyahu a Caesarea saidai shida iyalan sa basa Gidan lokacin da aka kai harin.

Manchester City na da tabbacin Haaland, zai sanya hannu kan sabuwar yarjejeniya inda zai zama wanda ya fi albashi a gasar Premier.

Ruud van Nistelrooy na neman aikin horar da ƴan wasa a Premier bayan barin Manchester United.

Juventus na diba yiyuwar ɗauko ɗanwasan Man. United Joshua Zirkzee, yayin da makomar ɗan wasan ƙungiyar Dusan Vlahovic, ke cikin rashin tabbas.

Newcastle za ta iya sayar da ɗan wasan ta Alexander Isak, domin amfani da kuɗin domin yin sabon zubi.

UEFA Nations League: Germany ta sami nasara akan Bosnia da ci 7:0 a wasan jiya.

Da Dumi Dumi Zargin tsadar man fetur an hangi ayarin wasu zababbun Yan majalisun jaha na Kano a cikin adaidaita sahu ind...
16/11/2024

Da Dumi Dumi
Zargin tsadar man fetur an hangi ayarin wasu zababbun Yan majalisun jaha na Kano a cikin adaidaita sahu inda s**a ajjiye motocin su a gida yayin gudanar da aiki ga Al'umar su da suke wakilta
An hangi a yarin Yan majalisun makare a cikin adaidaita sahu inda har ake zargin sun karya dokar zaman Babu Mai kafa uku Wanda gwamnatin jahar ta Sanya na Hana zaman gefe da gefe
Hakan ya jawo Cece kuce a kafafan sadarwa inda Al'umma da dama suke tofa albarkacin bakunan su
Sai dai wasu suna ganin tsadar man fatir da ake fama da ita a fadin kasar ita ta Sanya zababbun 'yan majalisun ajjiye motocinsu a gida suyi kudi_kudi domin samun saukin biyan Mai adaidaitan yayin fita ai watar da aiki ga Al'umar su

16/11/2024

Labaran Safiyar Asabar 16/11/2024CE - 14/05/1446AH Ga Takaitattun Labaran.

Shugaba Tinubu ya karrama marigayi Laftanar Janar Lagbaja da lambar CFR.

A jihar Kano, ana ci gaba da ce-ce-ku-ce da musayar ra'ayoyi bayan da gwamnan jihar ya rantsar da sabon shugaban ƙaramar hukumar Kumbotso.

Gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo ya naɗa ƙarin kwamishina ɗaya da shugabannin wasu hukumomin gwamnati.

Sarki Sanusi ya naɗa ɗansa DSP Aminu Lamiɗo a matsayin Ciroman Kano.

ICPC za ta binciki Jami’an INEC kan almundahana a zaben Gwamnan Edo.

INEC ta buƙaci jam’iyyu da ƴan takara su wanzar da zaman lafiya Kan zaɓen Gwamnan Ondo.

Masu ruwa da tsaki kan harkar makarantun tsangaya sun ce ya k**ata a tilasta wa iyayen da ke tura ’ya’yansu karatun allo su rika kai musu kayan abinci.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan'adam sun zargi gwamnatin Azerbaijan da yin amfani da taron COP29 wajen murƙushe masu fafutikar kare muhalli da sauran 'yan adawar siyasa.

Ana zargin shugaban ma'aikatan Netanyahu da sauya bayanai kan yaƙin Gaza.

Jam'iyyar sabon shugaban Sri Lanka ta k**a hanyar lashe zaɓen ƴan majalisa.

Lebanon ta yi watsi da bukatar Amurka kan tsagaita wuta.

UEFA Nations League: Portugal ta sami nasara akan Poland da ci 5:1 a wasan jiya.

UEFA Nations League: Spain ta sami nasara akan Denmark da ci 2:1 a wasan jiya.

UEFA Nations League: Scotland ta sami nasara akan Croatia 1:0 a wasan jiya.

Da dumi'dumi: Gwamnan Abia ya Karrama Kwankwaso kan yadda Ya Gina Al'umma  a rayuwarsa.Gwamna Alex Otti na jihar Abia ya...
09/11/2024

Da dumi'dumi: Gwamnan Abia ya Karrama Kwankwaso kan yadda Ya Gina Al'umma a rayuwarsa.

Gwamna Alex Otti na jihar Abia ya karbi bakuncin Jagoran jam'iyyar NNPP na kasa Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso a gidan gwamnati dake Umuahia.

Tattaunawar tasu ta ta'allaka ne kan siyasar kasa da kuma makomar Najeriya. A wani biki na musamman wanda Gwamna Otti ya karrama Sanata Kwankwaso da lambar yabo kan irin gudunmawar da ya bayar ga al’umma, a zamaninsa na Mulki da kuma bayan Mulki.

📷Saifullahi Hassan

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce a shirye yake ya yi aiki da Donald Trump k**ar yadda s**a yi a baya.Shima firamin...
06/11/2024

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce a shirye yake ya yi aiki da Donald Trump k**ar yadda s**a yi a baya.

Shima firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu ya taya Trump murna bisa sake dawowa da ya yi shugabancin Amurka.

Shugaban gwamnatin Austria Karl Nehammer ya ce za su yi aiki da Donald Trump domin tunkarar ƙalubalan da duniya ke fuskanta.

Shugabanƙasar India Narendra Modi shima ya bi sahun masu taya Trump murnar sake lashe zabe.

A yau babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sallami wasu matasa 71 daga jihar Kano tare da wankesu daga zargin da ake yi m...
05/11/2024

A yau babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sallami wasu matasa 71 daga jihar Kano tare da wankesu daga zargin da ake yi musu na shiga zanga-zangar matsin rayuwa a watan Agustan 2024.

Wadannan matasa da ake zargi da laifin cin amanar kasa bayan an same su da tutocin kasar Rasha, an wanke su daga dukkan tuhume-tuhumen da ake yi musu.

Gwamnan jihar Kano, Alh. Abba Kabir Yusuf, ya jajirce wajen ganin an sako matasan, inda ya sha alwashin bin dukkan hanyoyin da doka ta tanada domin tabbatar da ‘yancinsu.

A cikin wata sanarwa da sakataren yada labarai na Gwaman Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamna Abba Kabir Yusuf ya nuna jin dadinsa kan kokarin hadin gwiwa da masu rajin kare hakkin bil’adama da s**a hada da fitaccen lauya Femi Falana SAN da sauran wadanda s**a yi fafutuka ba tare da gajiyawa ba wajen ganin an sako yaran.

A yau ne mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima zai mika matasan ga gwamna Abba Kabir Yusuf, kafin daga bisani a dawo da su Kano ta jirgin Max Air.

03/11/2024

Yanzu yanzu mawakin jam iyar NNPP kwankwasiya na kasa Tijjani Gandu ya saki Sabuwar Wakar ka kan tsare yaran Arewa da gwamnati tayi dalilin zanga zanga

Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana cewar zaɓen shekarar 2027 mai zuwa zai kasance tsakanin jam'iyar APC ne da '...
03/11/2024

Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana cewar zaɓen shekarar 2027 mai zuwa zai kasance tsakanin jam'iyar APC ne da 'yan Najeriya duba da halin da jam'iyar ta jefa 'yan ƙasar a ciki tun bayan hawa mulki.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ɗakin taron gidan gwamnati na jihar Oyo a yammacin ranar Asabar, yayin gudanar da wani muhimmin taro wanda ya haɗar da manyan jigogi na jam'iyar PDP.

Me zaku ce?

Gwamna Abba ya bayar da umarni ga kwamishinan shari'a domin shiga lamarin Yara Kanana 'yan asalin Jihar Kano dake tsare ...
03/11/2024

Gwamna Abba ya bayar da umarni ga kwamishinan shari'a domin shiga lamarin Yara Kanana 'yan asalin Jihar Kano dake tsare a gidan Yarin kuje Abuja.

Gwamnan Jihar Kano Engr Abba Kabir Yusuf ya wallafa a shafinsa na Facebook Yana Mai cewa Hankalina ya karkata ga bayyanar matasa yara (wasu da ake kyautata zaton ’yan Kano ne) a kotu yau a Abuja.

Na umurci Kwamishinan Shari’a da ya gaggauta daukar mataki kan lamarin. Za mu yi duk mai yiwuwa don dawo da su Jihar Kano, in sha Allahu. - AKY

Address

Hotoro, Tsamiyar Boka
Kano
HARISIYYA01

Telephone

8937992403

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HARIS HAUSA TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share