07/09/2025
Ina ganin duk wani abu da Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa ke yi a siyasarsa na baya-bayan nan baiyi daidai da dan amana ba, sannan kuma bai gode ba. Ko da kuwa wasu basu lura da haka ba, ni na lura da hakan.
Duk wanda yake bibiyar al'amuran yau da sannan ya san tarihin Kofa a siyasa, ya san cewa Kwankwaso ne ya dora shi a wannan tafiya. A shekarar 2011, Kwankwaso ne ya tsaya masa, ya ba shi tikitin takarar Majalisar Wakilai, kuma ya sake mara masa baya a 2015.
A 2019 kuwa, duk da yawan kokarin da yayi da kuma ikirarin kusancinsa da shugaba Tinubu, Gwamna Abdullahi Ganduje bai barshi ya sake takara ba. Wannan ne ma ya nuna cewa Kofa ya rasa mafita a siyasa, sai ya koma gefe.
A zaben 2023, Kwankwaso ne ya sake daukar dawainiyar farfado da siyasar Kofa, siyasar da da ta riga ta mutu. Ya bashi tikiti ba tare da wani sharadi ba. Da ba don wannan taimako ba, da tuni tarihin Kofa a siyasa ya kare.
Duk da haka, Kowa ya gane cewa Kofa mutum ne da ke jiran karamin uzuri don ya sauya sheka. Kuma da zarar ya samu wannan damar, sai ya nufi kafafen yada labarai, musamman Channels TV, yana furta kalmomi masu zafi da rashin girmamawa ga mutumin da ya daga shi.
Godiya ga Allah da NNPP ta yi gaggawa, domin wani lokacin, sare kan maciji tun da wuri shi ne kawai hanyar dakatar da cizon da zai sake yi.
Ina goyon bayan dakatarwar da jam'iyyar NNPP ta yi wa Kofa, domin siyasa ba wai kawai cimma buri ba ce, har ila yau tana bukatar mutunci, amana, da godiya.
— Majan Kira
Public Affairs Commentator