NNPP kano north

NNPP kano north Burin wannan kafa sanar DA al'umma halin DA ake ciki a tafiyar siyasar kwankwaso ta kano DA kasa baki daya

Kaf Kwankwasiyya a tunani na, akwai mutum biyu da ba za su taɓa rabuwa da Kwankwaso ba, ko tsira ko halaka, Allah Ya shi...
08/09/2025

Kaf Kwankwasiyya a tunani na, akwai mutum biyu da ba za su taɓa rabuwa da Kwankwaso ba, ko tsira ko halaka, Allah Ya shiga lamuranku, domin kuna kan dai-dai.

Allah yashiga lamuran ku, kuna kan dai-dai.
H.E Abba K Yusuf Gida-Gida.
Hon. Ahmad Garban Bichi

Kwankwaso Ba Dan Jihar Katsina Bane Amma Ya Ginawa Dalibai Hostel A Jami'ar Alkalam Dake Katsina.Kwankwaso Ba Dan Sokoto...
07/09/2025

Kwankwaso Ba Dan Jihar Katsina Bane Amma Ya Ginawa Dalibai Hostel A Jami'ar Alkalam Dake Katsina.

Kwankwaso Ba Dan Sokoto Bane Amma Ya Gina Dakin Kwanan Dalibai A Jami'ar Usman Danfodio.

Kwankwaso Ba Dan Jihar Nassarawa Bane Amma Ya Gina Musu Makaranta Domin Koyo Da Koyarwa.

Kwankwaso Ba Dan Jihar Borno Bane Amma ya debo marayu 200 wayanda rikicin boko haram ya dai daita a jihar, ya basu mahalli, ya saka su amakaranta kuma yake daukar dawainiyar su.

Kwankwaso Bai Mulki Nigeria Ba Amma Kowacce Jiha A Nigeria Sai Da Ya Dauki Mutane 4 Tare Da Daukar Nauyin Karatunsu Na Jam'ia Ta Mewar University India 🇮🇳 Dake Abuja.

Ubangiji Allah ya cika maka Burinka Oga
Bishop Isaac Idahosa
Kwankwasiyya Reporters
Kwankwasiyya Ballots Box Representatives Association Kano State

Wannan Shine Gidan Rumfa Burin Kowanne Sarki Dake Amsa Sunan Sarki a Kano Ya Ganshi a Gidan Nan Duk Wanda Baya Cikin Gid...
07/09/2025

Wannan Shine Gidan Rumfa Burin Kowanne Sarki Dake Amsa Sunan Sarki a Kano Ya Ganshi a Gidan Nan Duk Wanda Baya Cikin Gidan Nan Kuma Yake Amsa Sunan Sarkin Kano To Duk a Inda Kuka Ganshi Ku Ringa Ce Masa Sannu Saki.

Nifa Duk Abin Da Kofa Yyy Bazaiyi Mamaki Ba Sabi wallahi lokacin Da Kwankwaso Da Kawu Sumaila da Alasan Rurum s**a Sauka...
07/09/2025

Nifa Duk Abin Da Kofa Yyy Bazaiyi Mamaki Ba Sabi wallahi lokacin Da Kwankwaso Da Kawu Sumaila da Alasan Rurum s**a Sauka a Malam Aminu Kano International Airport A Gabana Kofa ya Wurgar da Farar hularsa a Cikin Mutanan mu wani ya Bashi Jar Hula Yasaka ya bi Rubibi Ya Shiga Kwankwasiyya shi Kuma Jagora da Yake Mutum ne Mai Yafiyar ya Dauki takara ya Bashi Amman Yanzu Gashi wa Gari Ya waya a Daidai Fage Wafa Gurin Masu Siyar Da Mashina wallahi a Nan Kofa Ya Saka Jar Hula Sabi Da Haka Kar kuyi Mamaka Daman Turoshi Akayi Domin Damana Can Yaron Tunubu ne .

Ya Allah Duk Mutumin da zai Zaizo ya Rabu da Madugu domin Biyan Bukatarsa Daga Baya Kuma Yaci Amanar sa Ya Allah Karkakawo mana shi Cikin Tsarin Kwankwasiyya.🤲

Kowa yabar jagora zamu barshi kwankwasiyya zami Babu gashi.✍️
Alhassan

Kwankwasiyya Na Bukatar A Fifita Yan Asalin Kwankwasiyya Kafin Tubabbu 👇   Sau Dayawa ina mamakin Yanda ake wofantar da ...
07/09/2025

Kwankwasiyya Na Bukatar A Fifita Yan Asalin Kwankwasiyya Kafin Tubabbu 👇

Sau Dayawa ina mamakin Yanda ake wofantar da yan Kwankwasiyya masu akida adauki butulaye abasu ragamar tafiyar da Al'umma, Akarshe su zama kaza Ci Kigoge baki

su kuwa yan akidar kwankwaso da Kwankwasiyya saboda tsananin biyayya da kaunar kwankwaso s**arbi faduwar ko nasarar da aka tunkara, irinmu da bamaja da baya sannan muna haska wasu korafe korafe da yan akida keyi akasa, kiranmu Anan

me girma jagora Muna rokonka Dan Allah Dan Annabi mu mabiyanka Dan Allah Muna kira da duk abinda zai faru nasara ko akasinta abawa yan cikin gida suyi takara koda za'a fadi

ina amfanin wanda aka zaba su gudu da hakkin mu kuma gobe su dawo abasu dama su kara maimaita abinda daya faru juya,

Muna kira Abawa yan akidar Kwankwasiyya takara koda basu da kudi ko gata Amman suna da nagarta da akidar Cigaban Al'umma da jahar Kano baki daya

07/09/2025

Daga karshe dai
Alhamdulillah.

07/09/2025

A TAƘAICE: Shi Audu Kofa so yayi ya zama dillalin cefanar da Jagora, Gwamna da ilahirin Ƴan Kwankwasiyya a wajen shugaban ƙasa daga ƙarshe idan ciniki ya faɗa sai a bashi kujerar minista a matsayin la'adar dillacinsa.

Ita kuma jam'iyyar NNPP sai take ganin ai ko da akwai wani mutum a duniya ko wasu mutane daya kamata ace sunyi dillacin Ƴan Kwankwasiyya a wani waje bai kamata ace sun wuce Jagora Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ko Gwamna Alhaji Abba K Yusuf ba domin kuwa sune s**a fi kowa dacewar su jagorance a kowacce irin tafiya ba mutumin dake kwadayin iya la'adar da zai samu ba.

Cikin mutuntawa jam'iyya ta kira Audu Kofa ta gaya masa cewa ya tsaya ya nutsu ya bar duk wata rawar ƙafa da sunan zama dillalin da ba'a bashi tallan kaya ba, aka fito ɓaro-ɓaro aka gaya masa cewar duk wanda yake son ƙulla wata alaƙar siyasa da Ƴan Kwankwasiyya to kai tsaye Jagora Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ko Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusuf sune mutanen da zai zauna da su a matsayin wakilai ya tattauna da su ba wani mutum ba.

Da Audu Kofa ya fahimci gargadin da akayi masa sai ya ruga gidan TV na Channel yana sambatu ciki hadda tallata Ɗan jam'iyyar da ba nasa ba.

Ita kuma jam'iyyar NNPP jam'iyya ce mai tsari da bin dokoki ba irin jam'iyyar PDP bace da wani zai zame mata karfen ƙafa har a bashi kwamishina a gwamnatin Ganduje ko a bashi minista a gwamnatin Tinubu amma a rasa yadda za'a yi da shi, kai tsaye jam'iyya uwar kowa tayi waje rod da Audu Kofa.

Saboda haka yanzu za'a sake sabon lale, masu son hadaka da mu yanzu zasu gane cewar sun tsalleke mai kaya sun tafi suna tattaunawa ne da dillali bayan da mai kaya ya gano dillali yana kokarin cutarsa kuma yace kori wannan dillalin saboda haka duk mai son tattauna wata magana da yan Kwankwasiyya to kai tsaye Jagora Kwankwaso ne abin nema ba wani a wani waje ba.

Ina ganin duk wani abu da Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa ke yi a siyasarsa na baya-bayan nan baiyi daidai da dan amana ba, ...
07/09/2025

Ina ganin duk wani abu da Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa ke yi a siyasarsa na baya-bayan nan baiyi daidai da dan amana ba, sannan kuma bai gode ba. Ko da kuwa wasu basu lura da haka ba, ni na lura da hakan.

Duk wanda yake bibiyar al'amuran yau da sannan ya san tarihin Kofa a siyasa, ya san cewa Kwankwaso ne ya dora shi a wannan tafiya. A shekarar 2011, Kwankwaso ne ya tsaya masa, ya ba shi tikitin takarar Majalisar Wakilai, kuma ya sake mara masa baya a 2015.

A 2019 kuwa, duk da yawan kokarin da yayi da kuma ikirarin kusancinsa da shugaba Tinubu, Gwamna Abdullahi Ganduje bai barshi ya sake takara ba. Wannan ne ma ya nuna cewa Kofa ya rasa mafita a siyasa, sai ya koma gefe.

A zaben 2023, Kwankwaso ne ya sake daukar dawainiyar farfado da siyasar Kofa, siyasar da da ta riga ta mutu. Ya bashi tikiti ba tare da wani sharadi ba. Da ba don wannan taimako ba, da tuni tarihin Kofa a siyasa ya kare.

Duk da haka, Kowa ya gane cewa Kofa mutum ne da ke jiran karamin uzuri don ya sauya sheka. Kuma da zarar ya samu wannan damar, sai ya nufi kafafen yada labarai, musamman Channels TV, yana furta kalmomi masu zafi da rashin girmamawa ga mutumin da ya daga shi.

Godiya ga Allah da NNPP ta yi gaggawa, domin wani lokacin, sare kan maciji tun da wuri shi ne kawai hanyar dakatar da cizon da zai sake yi.

Ina goyon bayan dakatarwar da jam'iyyar NNPP ta yi wa Kofa, domin siyasa ba wai kawai cimma buri ba ce, har ila yau tana bukatar mutunci, amana, da godiya.

— Majan Kira
Public Affairs Commentator

07/09/2025

Abba dai sai yayi 8 Insha Allah, idan ya gama a samu Gangariyar Ɗan Kwankwasiyya ya ɗora daga inda ya tsaya.

07/09/2025

"Ciniki na ya riski gaɓar dacewa, ga mai kaya ba zamubi dillali ba"
😂

07/09/2025

Tsintacciyar Mage 👌

07/09/2025

NNPP Tace Ta Kori Kofa Daga Jam’iyyarta.

Wata NNPP Din Ta Mayaudara Sunce Bai Kori Ba Amma Shi Kofan Da Kansa Ya Karbi Korar Da NNPP Me Lasisi Tayi Masa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NNPP kano north posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share