NNPP kano north

NNPP kano north Burin wannan kafa sanar DA al'umma halin DA ake ciki a tafiyar siyasar kwankwaso ta kano DA kasa baki daya

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana hakan ne a wani saƙon da ya wallafa na jimamin tsohon Shugaban Najeriya, marigayi Muhamma...
17/07/2025

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana hakan ne a wani saƙon da ya wallafa na jimamin tsohon Shugaban Najeriya, marigayi Muhammadu Buhari da aka binne a garin Daura na jihar Katsina a ranar Talata.

Tinubu ya bayyana irin kyawawan halayen marigayin da kuma rawar da ya taka domin ciyar da Najeriya gaba.

Wakilan Malamai da dalibai na Makarantar Muhammad Buhari College for Science and Arabic Studies (wanda ke da Dalibai kus...
16/07/2025

Wakilan Malamai da dalibai na Makarantar Muhammad Buhari College for Science and Arabic Studies (wanda ke da Dalibai kusan 450) da ke Daura makaranta da aka gina sadaqa wanda ba ta hukuma.
Sun kawo ziyarar ta'aziya a gidan Baba Buhari dake Daura.
Allah Ya ba shi gidan Aljannar Firdaus.

16/07/2025

Tsowan shugaban jamm'iyyar APC nakasa ya fice daga APC zuwa jam’iyyar hadaka ta ADC.

16/07/2025

Za'a maida haƙƙoƙi ga masu haƙƙi ranar Lahira har ragon da baida ƙaho zai ramuwa ga ragon da ya buge shi da ƙaho—Inji Manzon Allah

Ni ne matashin da na fara dinka gizinoni a Birget, a shekara ina dinka kaya sama da 365 - jarumin Kannywood, Sahir Abdul
16/07/2025

Ni ne matashin da na fara dinka gizinoni a Birget, a shekara ina dinka kaya sama da 365 - jarumin Kannywood, Sahir Abdul

🚨Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar dalibai biyu na makarantar Sakandaren ...
16/07/2025

🚨Gwamnatin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar dalibai biyu na makarantar Sakandaren kwana ta gwamnati da ke Bichi.

Daliban da s**a rasu, Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa, ana zargin sun mutu ne sakamakon yadda wasu dalibai da ke ajin gaba da su su kabasu horo mai hadari da ake kira ‘Gwale-Gwale’.

Rahotanni sun ce manyan daliban ne s**a aikata wannan laifi inda s**a zargi wadanda aka kashen da aikata wani laifin da ba a bayyana ba inda s**a yanke shawarar hukunta su.

Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar Kano, Balarabe Abdullahi Kiru ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Laraba, 16 ga Yuli, 2025.

Sanarwar ta ce, Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Makoda, ta bakin babban sakataren ma’aikatar, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ya bayar da umarnin a gudanar da cikakken bincike na gaskiya cikin gaggawa domin gano gaskiyar lamarin.

Iyalan mamatan sun roki a yi musu adalci. Malam Ibrahim Yusuf Dungurawa, dan uwa ga Umar Yusuf, ya bayyana yadda wannan labari ya rutsa da dan'uwan sa tare da yin kira ga gwamnati da ta tabbatar da adalci.

Hakazalika, Malam Idris Garba Tofawa, mahaifin marigayi Hamza Idris, a yayin da ya bayyana rashin a matsayin jarabawar Ubangiji, ya bukaci hukumomi da su yi abinda ya dace.

16/07/2025

Maganr gaskiya BA adawa jagora kwankwaso yasamu shaida a gurin magabata Da mutanan yanxu saidai muce MADUGU Ka qara godewa Allah

16/07/2025

Ba a saka Dan Sanda a tsakiyar abun hawa.

Madugu ya buga lissafi daidai yasin😂

🚨Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i sun ziyarci Kabarin marigayi M...
16/07/2025

🚨Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa'i sun ziyarci Kabarin marigayi Muhammadu Buhari a gidansa dake Daura domin yi masa addu'a.

A lokacin jana’izar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, garin Daura ya karɓi baƙuncin ɗumbin mutane daga sassa d...
16/07/2025

A lokacin jana’izar tsohon shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, garin Daura ya karɓi baƙuncin ɗumbin mutane daga sassa daban-daban na Najeriya da kuma Afrika, kamar ‘yan siyasa da sarakuna da kuma masoyan Buharin.

Ga yadda jana’izar ta kasance.

Marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammad Buhari ya kasance guda cikin ƴan siyasar da aka fi nunawa soyayya a Najeriya. Me ...
16/07/2025

Marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammad Buhari ya kasance guda cikin ƴan siyasar da aka fi nunawa soyayya a Najeriya.

Me kuka koya daga wajen shi?

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu yayin da ya ke gaisuwar ƙarshe ga gawar marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammad Buhari k...
16/07/2025

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu yayin da ya ke gaisuwar ƙarshe ga gawar marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammad Buhari kafin binne shi.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NNPP kano north posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share