GRTV News

GRTV News GRTV NEWS MURYAR HADA KAN AL'UMMA

Tsohon Kwamishinan Ma'aikatun Lafiya da Muhalli na Jihar Kano, kuma Memba a Kwamitin Gudanarwa na Jami'ar Sufuri ta Tara...
07/06/2026

Tsohon Kwamishinan Ma'aikatun Lafiya da Muhalli na Jihar Kano, kuma Memba a Kwamitin Gudanarwa na Jami'ar Sufuri ta Tarayya da ke Daura, Hon. Dr. Kabiru Ibrahim Getso, ya bayyana matuƙar alhini da jimami bisa rasuwar Alhaji Adamu Ibrahim Getso, tsohon Manajan Darakta na Radio Kano da ARTV.

A cikin wata sanarwa da Mai Taimaka Masa na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama'a, Aliyu Abdul Garo, ya fitar, Dr. Getso ya bayyana rasuwar marigayin a matsayin babban rashi ga al'ummar Getso, Jihar Kano baki ɗaya, da kuma fannin yaɗa labarai.

Ya ce labarin rasuwar Alhaji Adamu Ibrahim Getso ya girgiza shi matuƙa, tare da haifar da babban gibi da zai yi matuƙar wahalar cikewa, la'akari da irin gudunmawar da marigayin ya bayar wajen ci gaban al'umma da hidimomin jama'a a tsawon rayuwarsa.

Dr. Getso ya bayyana marigayin a matsayin jagora nagari, mai ba da shawara, gogaggen mai gudanarwa, kuma uba ga al'ummar Getso, wanda hikimarsa, nagartarsa, da jajircewarsa wajen cigaban al'umma s**a sanya ya samu girmamawa da karramawa daga jama'a daban-daban.

Ya ce, "Na yi matuƙar alhini da jin rasuwar Alhaji Adamu Ibrahim Getso. Wannan babban rashi ne ga al'ummarmu da ma jihar Kano baki ɗaya. Marigayin ba kawai ginshiƙi ne ga iyalansa ba, ya kasance uba, jagora, kuma abin koyi ga al'ummar Getso baki ɗaya. Gudunmawar da ya bayar a fannin yaɗa labarai, cigaban al'umma da gina ɗan Adam za su ci gaba da kasancewa abin tunawa har abada."

A madadinsa, iyalansa, magoya baya da masoyansa, Dr. Getso ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa ga iyalan marigayin, Dagacin Getso Alhaji Bello Ibrahim (San Getso), al'ummar garin Getso, abokai da masu ruwa da tsaki, tare da daukacin al'ummar Jihar Kano bisa wannan babban rashi.

Ya kuma bayyana cewa marigayi Alhaji Adamu Ibrahim Getso ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al'umma hidima, inganta walwalar jama'a, da bunƙasa harkokin yaɗa labarai, inda ya bar kyakkyawan tarihi da za a ci gaba da alfahari da shi tsawon lokaci.

Dr. Getso ya ƙara da cewa, "Babu shakka rasuwar Alhaji Adamu Ibrahim Getso babban rashi ne ga al'ummar Getso da karamar hukumar Gwarzo baki ɗaya. Tarihin rayuwarsa na gaskiya, riƙon amana, shugabanci nagari da hidimtawa jama'a zai ci gaba da zama abin koyi ga masu zuwa bayansa."

Daga ƙarshe, ya yi addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin, Ya yafe masa kura-kuransa, Ya sanya shi a Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa, 'yan'uwansa da daukacin masoyansa haƙurin jure wannan babban rashi.

Aliyu Abdul Garo
07 June 2026
Sunday.

DR. GETSO YA TAYA MUSULMAI MURNAR IDIN BABBAR SALLAH Tsohon Kwamishinan Ma’aikatun Lafiya da Muhalli na Jihar Kano, kuma...
28/05/2026

DR. GETSO YA TAYA MUSULMAI MURNAR IDIN BABBAR SALLAH

Tsohon Kwamishinan Ma’aikatun Lafiya da Muhalli na Jihar Kano, kuma Mamba a Majalisar Gudanarwa ta Jami’ar Sufuri ta Tarayya da ke Daura, Hon. Dr. Kabiru Ibrahim Getso, ya taya al’ummar Musulmin Najeriya da ma duniya baki ɗaya murnar bikin Babbar Sallah.

A cikin wata sanarwa da Mai Taimaka Masa na Musamman kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Aliyu Abdul Garo, ya fitar, Dr. Getso ya bayyana Babbar Sallah a matsayin babban tunatarwa kan imani, sadaukarwa, biyayya da tausayi. Ya buƙaci Musulmai da su yi koyi da darussan Annabi Ibrahim (AS) ta hanyar ƙara kusanci ga Allah tare da tallafa wa junansu, musamman marasa galihu a cikin al’umma.

Dr. Getso ya kuma aike da saƙonnin fatan alheri ga manyan shugabanni ciki har da tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, inda ya yi masa addu’ar samun ƙoshin lafiya, da kwarin guywa wajen ci gaba da hidimtawa al’umma.

Haka zalika, ya taya Gwamnan Jihar Kano Alh. Abba Kabir Yusuf, da Mataimakin Gwamnan Jihar, Alh. Murtala Sule Garo, tare da sauran shugabannin siyasa na jihar murnar wannan biki. Tare da yabawa Gwamnan bisa jajircewarsa wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da ke inganta zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa a jihar.

Sanarwar ta kuma yaba da muhimmiyar rawar da sarakunan gargajiya, malamai da shugabannin addinai ke takawa wajen inganta kyawawan ɗabi’u, zaman lafiya da haɗin kai tsakanin al’umma.

Dr. Getso ya yi kira ga ’yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci na Sallah wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa, rungumar juna da kauce wa duk wani nau’i na rarrabuwar kawuna, tashin hankali da ƙiyayya. Ya jaddada cewa zaman lafiya, mutunta juna da haɗin kai su ne ginshiƙan samun ci gaba mai dorewa da bunƙasa ƙasa.

A ƙarshe, ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi ibadu, sadaukarwa da ayyukan alheri na al’ummar Musulmi, Ya gafarta kura-kurai, Ya Albarkaci jihar Kano, Najeriya da daukacin al’ummar Musulmi na duniya da zaman lafiya, wadata da kwanciyar hankali mai ɗorewa.

Aliyu Abdul Garo
28 ga Mayu, 2026
Alhamis.

Muna zargin Baffa Babba Ɗan'agundu da yiwa Jam'iyyar APC zagon ƙasa.Babu ko shakka maganganun da Baffa Babba yakeyi a wa...
21/05/2026

Muna zargin Baffa Babba Ɗan'agundu da yiwa Jam'iyyar APC zagon ƙasa.

Babu ko shakka maganganun da Baffa Babba yakeyi a wannan gaɓar zagon ƙasa ne da neman rarraba kawunan ƴaƴan jam'iyyar APCn Jihar Kano musamman Shiyyar Kano ta Arewa wacce itace GOLDEN ZONE a gurin dukkanin wani ɗan tsohuwar jam'iyyar APC, Shiyyar da ita kaɗai ce Jam'iyyar APC taci Sanata da Ƴan Majalissu ta kawowa shugaban ƙasa kuri'a tare da ɗan takarar gwamna na wancan lokacin, duk wani me kishin jam'iyyar APC da son tayi nasara a jihar Kano bazai rinƙa yin kalamai na tunzuri da rarraba kawunan ƴaƴan jam'iyyar ta APC ba, musamman ya rinƙa ƙara rura wutar fitina tsakanin Sanata Barau da ATM Gwarzo wanda sun riga sun haɗe zasu yiwa APC aiki tun daga sama har ƙasa, a wannan gaɓar da tafi kowacce gaɓa haɗari, gaɓar da ake taka tsantsan da gudun faɗawa cikin rarrabuwar kawunan ƴaƴan jam'iyya a gaɓar shi Baffa Babba Ɗan'agundu zai fito yana iƙirarin babu sulhu a siyasar wani yanki daba nasa ba.

Duk wani ɗan Jam'iyyar APC dama wanda ba ɗan Jam'iyyar ba idan ka tambaye shi wanne zone ne ko kokwanto basayi zone ɗin Jam'iyyar APC ne kuma ko tantama ba'ayi akan Nasarar jam'iyyar APC a yankin da ɗan Jam'iyyar APC dama wanda ba ɗan Jam'iyyar ba zai ce maka Shiyyar Kano ta Arewa, Shiyyar da kowa yake da tabbaci a kanta, Shiyyar da a 2023 ita kaɗai ce Jam'iyyar APC tai Nasara amma Baffa Babba ya fito yake ƙoƙarin raba kawunan Mutane a Shiyyar, yankin da ba nasa ba.

Baffa Babba Ɗan'agundu Maimakon Kalaman tunzuri da katsalandan a cikin siyasar wani yanki daba naka ba zaifi kyau ka koma ka gyara siyasar yankin ka, tun daga matakin akwatu zuwa mazaɓa har zuwa ƙaramar hukumar ka, ina ganin wannan aiki shine yafi maka ba fitowa kana rura wuta a wani yanki daba naka ba, Jam'iyyar APC a Shiyyar Kano ta Arewa zaune take lafiya kuma muna da tabbacin ruɓanya ƙoƙarin ƴaƴan jam'iyyar ta APC akan samun nasarar cin zaɓe a 2027 tun daga sama har ƙasa.

Muna kira ga uwar Jam'iyyar APC ta Jihar Kano da mai girma Gwamna da dukkanin jagororin Jam'iyyar APC na jiha dama ƙasa dasu tsawatarwa da Baffa Babba Ɗan'agundu kan zagon ƙasa da kalaman tunzuri da yakeyi kan siyasar Shiyyar Kano ta Arewa zone ɗin da duk ɗan Jam'iyyar APC yake kiran sa da (GOLDEN ZONE). Sannan su bashi assignment da yakoma yankinsa musamman ma akwatinsa da ƙaramar hukumar sa kada wannan lokacin ma yabamu kunya ya kasa ciwo mana zaɓen su.

Nasarar APC itace a gaban mu.

Hon. Abdullahi Abubakar
Ɗan kishin jam'iyyar APC

Majalisar Dokokin Kano ta amince da Murtala Garo a matsayin Mataimakin Gwamna - Kamaludden Sani Shawai
27/04/2026

Majalisar Dokokin Kano ta amince da Murtala Garo a matsayin Mataimakin Gwamna - Kamaludden Sani Shawai

Kungiyar Shugabannin kananan Hukumomi na jahar kano (ALGON )Su 44 Karkashin  Shugabancin Hajiya Sa'adatu Yusha'u Soja , ...
22/04/2026

Kungiyar Shugabannin kananan Hukumomi na jahar kano (ALGON )Su 44 Karkashin Shugabancin Hajiya Sa'adatu Yusha'u Soja , sun saya wa Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf form din Takarar Gwamna a zaben 2027.

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sanar da tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da Iran, ƴan sa’o’i ka...
22/04/2026

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sanar da tsawaita wa’adin yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da Iran, ƴan sa’o’i kaɗan kafin wa’adin farko ya ƙare.

Matakin na zuwa ne yayin da ake ƙoƙarin tsara sabon zagaye na tattaunawar sulhu tsakanin ɓangarorin biyu.

Ana ganin tsawaita yarjejeniyar zai taimaka wajen rage fargabar sake barkewar rikici, wanda a baya ya girgiza kasuwannin makamashi da tattalin arzikin duniya.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Trump ya bayyana cewa duk da tsawaita tsagaita wutar, Amurka za ta ci gaba da takaita zirga-zirgar jiragen ruwan Iran.

A ɓangaren Iran kuwa, har yanzu babu wata sanarwa kai tsaye dangane da wannan tsawaitawa. Sai dai kakakin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar, Esmail Baghaei, ya ce ba a cimma matsaya kan sake komawa teburin tattaunawa da Amurka ba, musamman kan matakin da Amurka ta ɗauka na rufe wasu hanyoyin jiragen ruwansu.

Adelabu na shirin yin murabus daga mukamin Ministan Lantarki bayan ganawa da TinubuMinistan Wutar Lantarki, Adebayo Adel...
22/04/2026

Adelabu na shirin yin murabus daga mukamin Ministan Lantarki bayan ganawa da Tinubu

Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu, na shirin yin murabus daga mukaminsa nan da kwanaki bayan wata ganawa ta musamman da ya yi da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Kamar yadda sanarwar mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Tunji Bolaji, ta bayyana, an tabbatar da wannan mataki ne bayan ganawar sirri da aka yi a ranar Talata.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya aike da sunan Alhaji Murtala Sule Garo ga majalisar dokokin jihar domin tantanc...
22/04/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya aike da sunan Alhaji Murtala Sule Garo ga majalisar dokokin jihar domin tantancewa da amincewa da shi a matsayin mataimakin gwamna.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labaran Gwamnan, Mustapha Muhammad, ya fitar.

Sanarwar ta ce matakin ya yi daidai da sashe na 191(3) na Kundin Tsarin Mulkin 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), wanda ke bai wa gwamna damar nada mataimaki idan mukamin ya zama babu kowa.

Ta kuma tunatar da cewa kujerar mataimakin gwamna ta zama babu kowa ne bayan murabus din tsohon mataimakin gwamna, Abdussalam Gwarzo, a ranar 27 ga Maris, 2026.

Gwamnan ya bayyana cewa nadin ya biyo bayan tuntuba da masu ruwa da tsaki, inda ya bukaci majalisar dokokin jihar ta amince da nadin.

Alhaji Garo mai shekaru 48, gogaggen dan siyasa ne da ya shafe sama da shekaru 20 yana rike mukamai na zabe da na nadin gwamnati. Ya taba zama Sakataren Tsare-tsare na jam’iyyarsa a jihar, mai ba gwamna shawara, da kuma shugaban karamar hukumar Kabo.

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta aika sammaci ga Shugaban Hukumar Ilimin Bai Ɗaya (SUBEB), Yusuf Kabir, domin ya yi bayan...
21/04/2026

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta aika sammaci ga Shugaban Hukumar Ilimin Bai Ɗaya (SUBEB), Yusuf Kabir, domin ya yi bayani kan yadda aka gudanar da daukar sabbin ma’aikatan fannin koyarwa, bayan korafe-korafe da s**a taso kan ɗaukar ma'aikatan.

Shugaba Tinubu ya yi garambawul a tsarin Ministocinsa Inda Wale Edun da Ahmed Dangiwa s**a yi Murabus
21/04/2026

Shugaba Tinubu ya yi garambawul a tsarin Ministocinsa Inda Wale Edun da Ahmed Dangiwa s**a yi Murabus

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GRTV News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share