Taura Top Tv

Taura Top Tv Muna godiya da ziyarar girmamawa. Ga masu bukatar kulla alaka damu zaku iya tuntubarmu a WhatsApp +2349040485468

(MDD) ta bayyana cewa sama da ‘yan Nijeriya 408,000 ne s**a tsallaka zuwa kasashen Nijar, Kamaru da Chadi, sakamakon tab...
09/01/2026

(MDD) ta bayyana cewa sama da ‘yan Nijeriya 408,000 ne s**a tsallaka zuwa kasashen Nijar, Kamaru da Chadi, sakamakon tabarbarewar al’amuran tsaro a wasu sassan kasar.

Rahoton ya nuna cewa hare-haren ‘yan bindiga da rikicin Boko Haram ne s**a tilasta wa dubban mutane barin muhallansu domin neman tsira da kariya a kasashen dake makwabtaka da Nigeria.

Shin ya kuke kallon wannan lamari?

Post By Tauratoptv

Shugaban ƙasar Uganda ya bayyana cewa ƙasarsa na da ƙarfin soji da jajircewar kare kanta, inda yace Uganda za ta iya fus...
06/01/2026

Shugaban ƙasar Uganda ya bayyana cewa ƙasarsa na da ƙarfin soji da jajircewar kare kanta, inda yace Uganda za ta iya fuskantar Amurka idan faɗa ya koma batun kare ikon ƙasa.

Shugaban ya yi wannan furuci ne a wani jawabi da yayi wa jami’an tsaro da magoya bayansa, inda ya jaddada cewa ’yancin kai da ikon ƙasa basu da abin da za a sasanta kansu da shi, komai girman ƙasar da ake magana a kai.

A cewarsa:
Bama neman faɗa da kowa, amma idan aka tilasta mana faɗan ƙasa, Uganda na da sojoji da za su kare mutuncin ƙasar.

Masu sharhi kan harkokin tsaro na ganin cewa wannan kalamai na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun tashin hankali a dangantakar Uganda da wasu ƙasashen yammacin duniya, musamman kan batutuwan tsaro, siyasa da haƙƙin ɗan Adam.

Post By Tauratoptv

Tsohon gwamnan Kano kuma jigo a siyasar jihar, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce idan har sauya shekar Gwamna Abba Kabir Yus...
06/01/2026

Tsohon gwamnan Kano kuma jigo a siyasar jihar, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce idan har sauya shekar Gwamna Abba Kabir Yusuf za a kira shi da butulci, to a cewarsa Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya fara wannan al’ada tun lokacin da ya bar jam’iyyar PDP zuwa APC.

Shekarau ya bayyana hakan ne a matsayin martani ga cece-kucen siyasa da ke kara daukar zafi a Kano, musamman kan batun dangantakar Gwamna Abba da Kwankwaso da kuma zarge-zargen sauya sheka ko rabuwa da tafiyar Kwankwasiyya.

A cewar Shekarau:
Ba adalci ba ne a rika kiran sauya shekar gwamna Abba da butulci, alhali kuwa Kwankwaso da kansa ya taba barin jam’iyya zuwa wata a lokacin shima yana gwamna.

Sannan Ya kara da cewa sauya sheka:
hakki ne na dan siyasa bisa kundin tsarin mulki,

kuma abu ne da ya zama ruwan dare a siyasar Najeriya, ba wai alamar cin amana ba ce kai tsaye.

Post By Tauratoptv

06/01/2026

Zamu yi addu’a, kowa yace Amin, Marasa lafiya na gida dana asibiti allah ka basu lafiya, Saboda Annabi Muhammad (SAW

05/01/2026

Zamu yi addu’a, kowa yace Amin, Ya Allah ka baiwa kowa sa'a a hanyar nemansa ta Alkhairi , Saboda Annabi Muhammad (SAW

Lauyoyin dake kare tsohon Shugaban Nijar, Mohamed Bazoum, sun bayyana cewa rabonsu da yin magana da shi tun watan Oktoba...
03/01/2026

Lauyoyin dake kare tsohon Shugaban Nijar, Mohamed Bazoum, sun bayyana cewa rabonsu da yin magana da shi tun watan Oktoban 2023, bayan da aka kwace masa wayarsa.

Wannan bayani ya fito ne ta kafar Wadata Radio Niger, wadda ta rawaito cewa lauyoyin sun nuna damuwa kan rashin samun damar tuntuɓar wanda suke karewa, tun bayan juyin mulkin da ya hambarar da gwamnatinsa.

A cewarsu, kwace wayar Bazoum ya sanya basa iya sadarwa kai tsaye da shi, ba sa samun cikakken bayani kan halin da yake ciki, kuma hakan na iya shafar haƙƙinsa na samun kariya ta doka.

Post By Tauratoptv

03/01/2026

Zamu yi addu’a, kowa yace Amin, Ya Allah ka kawo mana zaman lafiya a kasarmu dama duniya baki daya , Saboda Annabi Muhammad (SAW

Address

Kano
700101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taura Top Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share