Karamchi Tv

Karamchi Tv Karamchi TV Jarida ce dake watsa labarai a harshen Hausa, da su ka shafi kowane fanni na rayuwar Ɗan Adam.

Zaku iya tuntuɓarmu ta waɗannan hanyoyi domin bada talla:

Lambar waya/WhatsApp: 09044426890
Adireshin Email: [email protected].

Gaza: Falasɗinawa Sun Fara Samun Kayan Agaji Bayan Watanni 6Daga { Abubakar Bashir Adam Yakasai} Bayan kusan watanni shi...
27/07/2025

Gaza: Falasɗinawa Sun Fara Samun Kayan Agaji Bayan Watanni 6

Daga { Abubakar Bashir Adam Yakasai}

Bayan kusan watanni shida da dakatar da kai kayan agaji zuwa Gaza, rahotanni sun tabbatar da cewa an fara shiga da kayan tallafi zuwa yankin a yau Lahadi.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da al’ummar Falasɗinu ke ci gaba da fama da mummunar matsalar jin ƙai sakamakon rikicin da ke gudana tsakanin Isra’ila da Hamas, wanda ya janyo tsananin karancin abinci, magunguna da sauran kayan bukatu.

Majiyoyi daga yankin sun bayyana cewa motoci dauke da kayan abinci da magunguna sun samu damar shiga wasu sassan Gaza, lamarin da ya tayar da ƙwarin gwiwa ga dubban fararen hula da s**a shafe watanni cikin tsananin bukata.

Tun bayan da rikicin ya kazance a watan Oktoba, an dakatar da yawancin hanyoyin kai agaji, musamman daga iyakar Rafah, lamarin da ya janyo s**a daga kungiyoyin agaji da na kare hakkin bil’adama.

Har yanzu dai akwai bukatar karin kayan agaji domin biyan bukatun dimbin mutane da ke cikin halin matsi a Gaza. Kungiyoyin jin kai na duniya sun ce matakin bude hanya na yau babban cigaba ne, amma suna kira da a bude dukkan hanyoyin agaji gaba ɗaya ba tare da wani jinkiri ba.

Uwar Najeriya ta lashe gasar cin kofin Afirka ta mata Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya ta zama zakaran Afirka, ...
27/07/2025

Uwar Najeriya ta lashe gasar cin kofin Afirka ta mata

Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Najeriya ta zama zakaran Afirka, bayan da ta samu nasarar lashe gasar cin kofin Nahiyar da aka kammala a kwanakin nan.

Wannan nasara ta ƙara daga matsayin Najeriya a fagen wasanni, musamman ma wajen wakiltar ƙasa a matakin kasa da kasa. 'Yan wasan sun nuna bajinta da ƙwarewa a dukkanin wasannin da s**a fafata, lamarin da ya jawo yabo daga bangarori daban-daban na ƙasa.

An shirya gasar ce domin bai wa mata damar nuna basira da baiwar da Allah Ya h**e musu a fagen kwallon kafa, tare da girmama al’adunsu da fahimtar addininsu.

Ministan wasanni da sauran jami'an gwamnati sun taya tawagar murna tare da yabawa kwazon da s**a nuna, inda s**a ce wannan nasara alama ce ta cewa Najeriya na da tarin baiwa a tsakanin mata, muddin aka basu dama.

Yanzu Shinkafa Ta Wadatu a Nijeriya a Zamanin Gwamnatin Tinubu – Inji Daniel BwalaMai ba shugaban ƙasa shawara ta musamm...
27/07/2025

Yanzu Shinkafa Ta Wadatu a Nijeriya a Zamanin Gwamnatin Tinubu – Inji Daniel Bwala

Mai ba shugaban ƙasa shawara ta musamman kan harkokin sadarwa, Daniel Bwala, ya bayyana cewa a halin yanzu shinkafa ta wadatu a fadin ƙasar, sakamakon wasu tsare-tsare na musamman da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar.

Bwala ya ce wadannan manufofi sun haɗa da tallafawa manoma da kuma saukaka hanyoyin samar da kayan abinci a cikin gida, wanda hakan ya rage dogaro da shigo da kaya daga ƙasashen waje.

"A yau, babu wanda zai ce ana fama da karancin shinkafa a kasuwa, saboda tsarin da wannan gwamnati ta saka na inganta noman cikin gida," in ji Bwala a wata hira da ya yi da manema labarai.

Ya ƙara da cewa gwamnati na ci gaba da ɗaukar matakai domin tabbatar da cewa kayan abinci sun yi arha kuma sun wadatu ga kowa da kowa, musamman a wannan lokaci da ake fama da matsin tattalin arziƙi.

Yunwa Na Ci Gaba da Hallaka Rayuka a Gaza Yayin da Isra’ila Ke Ci Gaba da Hana Abinci da MagungunaDaga [ Abubakar Bashir...
27/07/2025

Yunwa Na Ci Gaba da Hallaka Rayuka a Gaza Yayin da Isra’ila Ke Ci Gaba da Hana Abinci da Magunguna

Daga [ Abubakar Bashir Adam Yakasai]

A yayin da hare-haren Isra’ila ke ci gaba da dagula rayuwar al’ummar Gaza, an ƙara tsaurara matakan hana shigowar abinci da magunguna zuwa yankin, lamarin da ke kara tsananta matsalar jin ƙai da ke addabar yankin.

A cikin sa’o’i 24 da s**a gabata, wani jariri mai mako guda mai suna Hud Arafat da kuma Zainab Abu Halib ’yar watanni shida, sun riga mu gidan gaskiya sakamakon matsanancin rashin abinci mai gina jiki da kuma gagara samun madarar jarirai.

Rahotanni daga hukumomin lafiya a Gaza sun bayyana cewa, adadin mutanen da s**a mutu sakamakon yunwa da ƙarancin abinci ya kai mutum 122, ciki har da yara 83. Hakan na faruwa ne a daidai lokacin da tsarin kiwon lafiya na yankin ke gab da rugujewa gaba ɗaya.

A cewar ofishin yaɗa labarai na gwamnatin Gaza a ranar 26 ga watan Yuli, sama da yara 100,000 – ciki har da jarirai 40,000 ’yan ƙasa da shekara ɗaya – na cikin hadarin mutuwa sakamakon rashin abinci mai gina jiki da kuma cikakkun kayan abinci na jarirai.

Al’ummar duniya na ci gaba da kiran a kawo karshen kulle-kullen da ke hana agajin jin ƙai shiga Gaza, domin ceton rayukan waɗanda ba su ji ba su gani ba, musamman mata da ƙananan yara.

Sanata Kwankwaso Ya Caccaki Shugaba Tinubu Kan Rabon Albarkatun ƘasaTsohon gwamnan Kano kuma jigon siyasar Arewa, Sanata...
24/07/2025

Sanata Kwankwaso Ya Caccaki Shugaba Tinubu Kan Rabon Albarkatun Ƙasa

Tsohon gwamnan Kano kuma jigon siyasar Arewa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya soki gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa zargin nuna son kai wajen raba albarkatun ƙasa, yana mai cewa gwamnatin na fifita Kudancin Najeriya fiye da yankin Arewa.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin taron masu ruwa da tsaki na jihar Kano kan sauya fasalin kundin tsarin mulki da za a gudanar a shekarar 2025.

A cewarsa, yankin Arewa na fama da koma baya wajen samun kayan more rayuwa da ci gaba saboda yadda ake ware shi daga rabon dukiyar ƙasa.

“Ina ba da shawara ga gwamnatin tarayya da ta duba yadda ake raba albarkatu. Yanzu ana tara dukiya daga duk faɗin ƙasa, amma ana amfani da ita ne wajen gina wasu yankuna kawai, musamman Kudancin ƙasar nan,” in ji Kwankwaso.

Kwankwaso, wanda ya tsaya takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar NNPP a zaben 2023, ya ce rashin adalci wajen rabon albarkatu na kara jefa yankin Arewa cikin ƙalubale, musamman a fannin ilimi, lafiya da tattalin arziki.

Ya kuma yi kira ga masu ruwa da tsaki a Arewa da su farka daga barci tare da neman mafita daga wannan matsala ta hanyar duba yadda za a samu daidaito da adalci a cikin kasa.

Shugaba Tinubu dai ya gabatar da kasafin kudin 2025 ga Majalisar Tarayya a ranar 18 ga Disamba, 2024, wanda wasu 'yan siyasa ke ganin ya fi karkata ne ga yankin da shugaban ya fito.

‘Yan Jarida a Gaza Na Fuskantar Barazanar Yunwa Mai TsananiDaga [Abubakar Bashir Adam Yakasai]Rahotanni daga sassa daban...
24/07/2025

‘Yan Jarida a Gaza Na Fuskantar Barazanar Yunwa Mai Tsanani

Daga [Abubakar Bashir Adam Yakasai]

Rahotanni daga sassa daban-daban na duniya na nuna cewa ‘yan jarida da ke aiki a Gaza na fuskantar barazanar faɗawa cikin ƙangin yunwa, sakamakon tsauraran matakan kulle da Isra’ila ta saka a yankin.

Ƙungiyoyin yada labarai irinsu AFP, BBC, da Reuters sun bayyana cewa ma’aikatansu da ke Gaza sun shiga cikin mawuyacin hali na rashin abinci, ruwa mai tsafta da magunguna — lamarin da ya jefa ayyukan jarida cikin barazana.

A cewar wani rahoto na AFP, wasu daga cikin ma’aikatansu sun ce sun daina iya aiki sakamakon raunin jiki da kuma rashin kuzari da yunwa ke haddasawa. Wasu sun bayyana cewa suna rayuwa ne kawai da ruwa mai gishiri, yayin da dama daga cikinsu ke kokarin ciyar da iyalansu ba tare da samun wani tallafi ba.

Haka kuma, wani rahoto daga Roya Media Group ya nuna cewa wasu daga cikin ma’aikatansu a Gaza sun shiga mawuyacin hali inda s**a ce sun fi so su mutu da mutunci fiye da ci gaba da rayuwa cikin wahala da kunci.

Wani dan jarida ma ya shiga yajin cin abinci domin jawo hankalin duniya kan yadda al’ummar Gaza, musamman masu aikin jarida, ke rayuwa cikin yunwa da rashin mafita, duk da jajircewar su wajen isar da sahihan labarai ga duniya.
A cewar kungiyoyin kare ‘yancin ‘yan jarida, akwai bukatar gaggauta kai agaji da daukar matakan kare lafiyar ma’aikatan kafafen yada labarai a Gaza, domin rage haɗarin rasa rayuka a cikin irin wannan yanayi na tashin hankali da yunwa.

Kotun Tarayya Ta Yanke Hukunci Kan G-Fresh da Hamisu Breaker Kan Cin Mutuncin NairaBabbar Kotun Tarayya da ke Kano ta ya...
24/07/2025

Kotun Tarayya Ta Yanke Hukunci Kan G-Fresh da Hamisu Breaker Kan Cin Mutuncin Naira

Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta yanke hukuncin daurin watanni biyar ko biyan tarar Naira 200,000 ga fitaccen ɗan TikTok, Abubakar Ibrahim (G-Fresh), bayan ya amsa laifin cin mutuncin Naira.

G-Fresh ya gurfana a gaban kotun karkashin jagorancin mai shari’a Mohammed N. Yunusa, bisa tuhumar watsa takardun Naira dubu-dubu a cikin wani shago da ke unguwar Tarauni, yayin da suke gudanar da nishadi tare da wasu.

Bayan karanto masa tuhumar, G-Fresh ya amsa laifin, lamarin da ya sa kotu ta yanke masa hukunci nan take.

A gefe guda, hukumar EFCC ta gurfanar da mawakin nan Hamisu Sa’id Usman, wanda aka fi sani da Hamisu Breaker, a gaban kotun Tarayya da ke Kano bisa zargin watsa kudi a bainar jama’a.

An tuhume shi da watsa takardun Naira dari biyu har zuwa Naira dubu 30 a wani gidan biki da ke Hadeja, Jihar Jigawa. Shi ma ya amsa laifin da ake zarginsa da shi, wanda hakan ya sa kotu ta yanke masa hukuncin daurin wata biyar ko biyan tara ta Naira 200,000.

Hukuncin na zuwa ne a daidai lokacin da hukumomi ke ƙara tsaurara matakai kan take-taken da ke rage kimar Naira, domin kare martabar kudin kasa.

Yunwa na Cigaba da Kashe Rayuka a Gaza: Falasɗinawa 111 sun mutu, miliyoyi na fuskantar bala’iDaga [ Abubakar Bashir Ada...
23/07/2025

Yunwa na Cigaba da Kashe Rayuka a Gaza: Falasɗinawa 111 sun mutu, miliyoyi na fuskantar bala’i

Daga [ Abubakar Bashir Adam Yakasai

Rahotanni daga Zirin Gaza na nuna cewa yunwa na ci gaba da yin kamari, inda mutane 111 s**a mutu sakamakon rashin abinci, a wani yanayi mai raɗaɗi da ke faruwa a hankali.

Ƙarin mutane goma sun riga mu gidan gaskiya cikin awanni 24 da s**a gabata kaɗai, yayin da Isra’ila ke ci gaba da yaƙin kisan kare dangi tare da hana shigar da kayan agaji, musamman abinci da magunguna, zuwa cikin yankin da ya rikide zuwa wani babban dandalin bala’i.

Rahotannin kungiyoyin agaji da Majalisar Ɗinkin Duniya sun bayyana cewa miliyoyin Falasɗinawa na fuskantar hadarin yunwa matuƙa, inda wasu suke kwashe makonni ba tare da samun abinci mai gina jiki ba.

Gwamna Namadi ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Hisbah a JigawaGwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya sanya hannu kan...
23/07/2025

Gwamna Namadi ya sanya hannu kan dokar kafa Hukumar Hisbah a Jigawa

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya sanya hannu kan dokar da ta kafa Hukumar Hisbah a matsayin hukuma ta doka a jihar.

An gudanar da bikin sanya hannun ne a Dutse, babban birnin jihar, tare da halartar Mataimakin Gwamna Aminu Usman, da wasu jiga-jigan majalisar dokoki ta jihar.

Wannan doka za ta bai wa hukumar Hisbah cikakken ikon aiwatar da ayyukanta na ƙarfafa tarbiyya, inganta ɗabi’a da adalci a cikin al’umma.

Gwamna Namadi ya ce kafa hukumar zai taimaka wajen ganin an samu zaman lafiya da daidaiton zamantakewa. Ya bukaci jami’an Hisbah da su gudanar da aikinsu cikin gaskiya, adalci da tsoron Allah.

Wannan mataki na zuwa ne bayan fiye da watanni takwas da aka fara nazarin kudirin dokar tun daga shekarar 2024.

ALLAHU AKBAR: An Bayyana Hoton Cikin Ɗakin Ka’abah – Wani Kallo Mai Cike da Ƙauna da Tsoron Allah"Allah ya ƙara mana ƙau...
23/07/2025

ALLAHU AKBAR: An Bayyana Hoton Cikin Ɗakin Ka’abah – Wani Kallo Mai Cike da Ƙauna da Tsoron Allah

"Allah ya ƙara mana ƙaunar Annabi Muhammadu (SAW) da wannan mafificiyar alfarma."

Barkanmu da Safiya Daga nan Karamchi TV

Yunwa Mai Tsanani: Kashi Ɗaya Cikin Uku Na Al’ummar Gaza Ba Su Ci Abinci Tsawon Kwanaki – WFPDaga { Abubakar Bashir Adam...
22/07/2025

Yunwa Mai Tsanani: Kashi Ɗaya Cikin Uku Na Al’ummar Gaza Ba Su Ci Abinci Tsawon Kwanaki – WFP

Daga { Abubakar Bashir Adam Yakasai}

A cewar sabon rahoton Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (World Food Programme – WFP), kashi ɗaya cikin uku na al’ummar Gaza sun kwashe kwanaki da dama ba tare da samun abinci ba, sakamakon tsananin takunkumi da ya hana kai kayan agaji ga fararen hula.

Daraktan shirye-shiryen gaggawa na hukumar, Ross Smith, ya bayyana cewa wannan matsalar yunwa ta kai wani “mummunan mataki” inda dubban mutane – ciki har da mata da kananan yara – ke fama da yunwar da ke barazana ga rayukansu.

“Mutane da dama ba su ci komai ba tsawon kwanaki da dama. Wannan wani abu ne mai tayar da hankali,” in ji Smith.

Rahoton ya nuna cewa sama da mutum 100,000 – galibinsu yara da mata – na cikin mawuyacin hali na yunwa mai tsanani, inda tallafin abinci ke kasa isa gare su saboda haramtaccen shiga da kuma ci gaba da hare-haren da ake kai wa yankin.

Hukumar WFP ta yi kira ga ƙasashen duniya da su gaggauta ɗaukar mataki domin tabbatar da cewa ana bai wa al’ummar Gaza damar samun abinci da sauran kayan agaji cikin gaggawa.

Ƙasashen Duniya Na Ƙara Matsa Lamba Kan Isra’ila, Na Allah Wadai da Yakin GazaDaga {Abubakar Bashir Adam Yakasai}Duniya ...
22/07/2025

Ƙasashen Duniya Na Ƙara Matsa Lamba Kan Isra’ila, Na Allah Wadai da Yakin Gaza

Daga {Abubakar Bashir Adam Yakasai}

Duniya na ci gaba da matsa wa Isra’ila lamba tare da nuna damuwa kan yadda ake gudanar da yakin Gaza, inda Tarayyar Turai da ƙasashe fiye da 25 – ciki har da Birtaniya, Canada da Japan – s**a yi Allah wadai da yadda Isra’ila ke ci gaba da jefa bama-bamai a Gaza ba tare da la'akari da fararen hula ba.

Kasashen sun bayyana wannan hari a matsayin “marar mutunci”, suna kuma kira da a dakatar da jefa bama-bamai nan take da kuma kare rayukan fararen hula da s**a maƙale cikin rikicin.

Sun bayyana cewa wajibi ne a mutunta dokokin yaƙi da kare hakkin ɗan Adam, tare da buƙatar a samar da hanyar ceto da kai agaji ga waɗanda rikicin ya shafa.

Wannan kira na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun asarar rayuka da dimbin raunuka a tsakanin fararen hula, musamman mata da yara, a sakamakon hare-haren da ake kaiwa a zirin Gaza.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karamchi Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share