Fasihiya

Fasihiya Labaran Hausa Rahotanni, Adabi bunkasa aikin fasaha.

NAHCON Ta Yi Alƙawarin Mayar wa Alhazai Kuɗin Abincinsu Da Ya Lalace tare da ladabtar da masu laifi a MinaDaga Aliyu Sam...
29/05/2026

NAHCON Ta Yi Alƙawarin Mayar wa Alhazai Kuɗin Abincinsu Da Ya Lalace tare da ladabtar da masu laifi a Mina

Daga Aliyu Samba

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta ce za ta tabbatar an mayar wa alhazan Najeriya da s**a fuskanci matsalar rashin ingantaccen abinci da walwala a Mina kudinsu, tare da hukunta duk wadanda aka samu da laifi.

Shugaban hukumar, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai bayan ya kai ziyara sansanonin alhazan Najeriya da ke Mina a yayin aikin Hajjin 2026.

Ya ce hukumar ta riga ta kai koken matsalar ga hukumomin Saudiyya kan yadda wasu kamfanonin abinci s**a gaza samar da ingantaccen abinci ga alhazai.

“Yayin rangadin da na yi yanzu, na gano cewa wasu jihohi ba a ba su abinci yadda ya kamata ba jiya da kuma karin kumallo na yau.

“Tuni muka dauki mataki tare da tuntubar hukumomin Saudiyya, kuma za mu saka kamfanonin da abin ya shafa cikin wadanda zamu dena aiki da su,” in ji shi.

Ambasada Ismail ya bayyana cewa hukumar ta sa an mayar abincin da aka ga bai dace da ci ba, tare da kokarin tabbatar da an biya diyyar asarar da alhazan s**a yi.

“Za mu tabbatar an mayar da kudin abincin da ba a kawo ba ko kuma wanda bai dace ba ga alhazai.

“Idan an samu kudin kafin su bar Saudiyya, za a ba su kai tsaye. Idan kuma ba haka ba, za a mikawa sakatarorin jihohi,” inji shi.

Sai dai shugaban NAHCON ya ce ba abin mamaki ba ne idan wasu alhazai ba su gamsu da dandanon abincin ba, domin akwai bambancin al’adu da salon girki tsakanin kasashe.

“Mun ji koke-koken da ake yi game da abincin, amma idan mutum ya bar kasarsa zuwa wata kasa, dole ne ya saba da al’adun wajen da ya je,”

Ya kara da cewa hukumar na duba yiwuwar dauko masu girki daga Najeriya a aikin Hajjin shekara mai zuwa domin su rika girka abincin da ya dace da alhazan Najeriya.

“Nan gaba, in sha Allah, muna son kawo masu girki daga Najeriya domin su yi wa alhazai girki sannan su koma gida bayan aikin Hajji,” inji shi.

Dangane da koke-koken da s**a shafi cunkoso da wuraren kwana, shugaban hukumar ya ce sun fara gudanar da bincike tare da kirga yawan alhazai a sansanonin jihohi daban-daban.

“Mun fara bincike kuma ni kaina na shiga aikin kirga alhazai a jihohi. Akwai abubuwan da muka gano, kuma idan lokaci ya yi za mu bayyana sakamakon binciken tare da hukunta masu laifi,” in ji shi.

Shugaban NAHCON ya kuma bayyana wasu sauye-sauyen da hukumar ta kawo domin inganta aikin Hajji a Najeriya.

Ya ce yanzu suna amfani da fasaha wajen neman biza, samun masauki da kuma biyan kudade domin rage cin hanci da inganta gaskiya a tsarin gudanarwa.

“Muna kokarin kawar da masu shiga tsakani ta hanyar tuntubar hukumomin Saudiyya kai tsaye domin su ba mu sunayen kamfanoni masu inganci,”

A cewarsa, hakan zai taimaka wajen rage kudin Hajji ga ’yan Najeriya tare da bai wa mutane da dama damar sauke farali.

Ya kuma ce hukumar ta inganta harkokin lafiya ta hanyar rajistar asibitoci tare da samar da isassun likitoci, ma’aikatan jinya da magunguna domin kula da lafiyar alhazai.

Duk da kalubalen da ake fuskanta sakamakon taruwar jama’a masu yawa, shugaban hukumar ya ce NAHCON za ta ci gaba da bai wa jin dadin alhazai fifiko a dukkan ayyukanta.

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Abdulaziz Abdulaziz  na taya Al'ummar Musulmi ...
28/05/2026

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaba Tinubu, Abdulaziz Abdulaziz na taya Al'ummar Musulmi Barka da Bikin Babbar Sallah.

NAHCON Ta Shirya Addu’o’i Na Musamman Ga Najeriya A Filin ArafaDaga Aliyu SambaHukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta shiry...
28/05/2026

NAHCON Ta Shirya Addu’o’i Na Musamman Ga Najeriya A Filin Arafa

Daga Aliyu Samba

Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta shirya zaman addu’o’i na musamman domin neman zaman lafiya, hadin kai da ci gaban Najeriya a wani bangare na ayyukan ranar Arafat a Hajjin shekarar 2026.

An gudanar da addu’o’in ne a ranar Talata a birnin Makkah yayin da miliyoyin alhazai daga sassa daban-daban na duniya s**a hallara a Dutsen Arafat domin gudanar da rukuni mai muhimmanci na aikin Hajji.

Zaman addu’ar ya samu halartar mambobin Kwamitin Malamai na Kasa na NAHCON, wasu ‘yan majalisar tarayya, jami’an hukumar da kuma maniyyata daga Najeriya.

Shugaban Hukumar NAHCON kuma Babban Jami’in gudanarwa, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ya bayyana cewa hukumar ta shirya addu’ar ne saboda halin kalubalen tattalin arziki da zamantakewar da kasar ke ciki.

Ambasada Yusuf wanda Kwamishinan Tsare-tsare, Bincike, Watsa Labarai da Ayyukan Laburare na hukumar, Farfesa Abubakar Yagawal ya wakilta, ya ce irin wadannan kalubale suna bukatar ‘yan Najeriya su koma ga Allah domin neman taimako da mafita.

Ya kuma bukaci maniyyatan Najeriya da su rika sanya kasar cikin addu’o’insu yayin da suke rokon bukatunsu na kashin kai.

Shi ma da yake jawabi, dan majalisar wakilai, Hon. Aliyu Sani Madaki, ya yaba wa shugabancin hukumar NAHCON bisa shirya addu’ar, yana mai cewa hakan ya nuna kishin kasa da kula da makomar al’umma.

An gudanar da addu’o’in ne cikin harsunan Larabci da Turanci tare da wasu harsunan Najeriya da s**a hada da Hausa, Yarbanci, Igbo, Nupe da Afemai.

A wani sako na musamman da ya aikewa maniyyatan Najeriya a ranar Arafat, shugaban NAHCON ya bayyana ranar a matsayin rana mafi girma a aikin Hajji, wadda take cike da rahama, gafara da karbar addu’a.

“Arafat rana ce ta tawali’u da sadaukarwa da kuma komawa ga Allah cikin cikakkiyar biyayya. Lokaci ne na yin nazari a kan rayuwa da kuma sabunta alkawarin bautar Allah da hidima ga bil’adama,” in ji shi.

Ya ce hukumar ta NAHCON na ci gaba da nazarin abubuwan da s**a shafi ayyukan Hajji domin kara inganta jin dadin maniyyata da saukaka musu gudanar da ibadunsu.

“Mun yi nisa daga shekarun baya da alhazai ke daukar lokaci mai tsawo a sansanonin jirgi kafin tashinsu zuwa Saudiyya zuwa yadda ake gudanar da Hajji cikin tsari da sauki a yanzu,” in ji Yusuf.

Sai dai ya ce duk da nasarorin da aka samu, har yanzu akwai bukatar kara gyare-gyare domin inganta ayyukan Hajji a nan gaba.

Shugaban hukumar ya kuma yabawa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa goyon bayan da take bai wa hukumar, wanda ya ce hakan ya taimaka wajen samun nasarorin da aka samu a jigilar maniyyatan bana.

Haka kuma ya gode wa Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, bisa bayar da jagoranci da sa ido kan aiwatar da manufofin da s**a shafi aikin Hajji.

Ya kuma yabawa jami’an hukumar NAHCON da sauran masu ruwa da tsaki saboda jajircewa da sadaukarwa wajen gudanar da aikin Hajjin bana.

Daga karshe, Yusuf ya tabbatar wa maniyyata cewa hukumar ta dauki matakan da s**a dace domin tabbatar da dawowarsu gida cikin tsaro da kwanciyar hankali bayan kammala aikin Hajji.

“Allah Ya karbi ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya hada kanmu tare da ba mu zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

ZAƁEN FIDDA GWANI  TINUBU YA SAMU GOYON BAYA MAI KARFI A SOKOTO.Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu gagarumar nasara...
25/05/2026

ZAƁEN FIDDA GWANI TINUBU YA SAMU GOYON BAYA MAI KARFI A SOKOTO.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu gagarumar nasara a zaɓen fidda gwani na ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar APC da aka gudanar a jihar Sokoto tare da sauran sassan ƙasar nan.

Bayan kammala tattara sakamakon zaɓen, shugaban tawagar gudanar da zaɓen APC a jihar Sokoto, Shine Mai Girma Gwamna Dr. Ahmad Aliyu Sokoto, Inda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya samu kuri’u dubu dari uku da ɗaya (301,001), lamarin da ya nuna cikakken goyon baya daga wakilan jam’iyyar a jihar.

Zaɓen ya gudana cikin lumana da tsari, yayin da magoya bayan jam’iyyar s**a bayyana farin cikinsu kan sakamakon da aka samu.

✍️ Ashir Mai Jama'a Bado
--->Daga Sokoto
--->24 May 2026

SHUGABA TINUBU YA KARBI BAKUNCIN SANATA WAMAKKO A LEGASYadda Mai girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a ranar 22 ga May...
24/05/2026

SHUGABA TINUBU YA KARBI BAKUNCIN SANATA WAMAKKO A LEGAS

Yadda Mai girma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a ranar 22 ga Mayu, 2026 ya karɓi bakuncin jagoran jam’iyyar APC a Jihar Sokoto, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, a gidan zamansa da ke Jihar Legas.

Ziyarar Taron ya mayar da hankali ne kan haɗin kan jam’iyya da kuma cigaban ƙasa a Najeriya.

Ziyarar ta kuma nuna kyakkyawar alaƙa da ke tsakanin Shugaban Ƙasa Tinibu da tsohon Gwamnan Jihar Sokoto, Kuma Jagoran Jam'iyar APC sanata Wamakko.

✍️ Ashir Mai Jama'a Bado
--->Daga Sokoto

Yaren Hausa Da Yarbanci Na Cikin Harsuna 35 Da Za A Fassara Huɗubar Arfa Kai Tsaye A BanaDaga Aliyu SambaMahukuntan Ƙasa...
24/05/2026

Yaren Hausa Da Yarbanci Na Cikin Harsuna 35 Da Za A Fassara Huɗubar Arfa Kai Tsaye A Bana

Daga Aliyu Samba

Mahukuntan Ƙasar Saudiyya sun sanar da cewa za a fassara huɗubar ranar Arfa ta Hajjin shekarar 2026 zuwa harsuna 35 na duniya, ciki har da Hausa da Yarbanci daga Najeriya, domin bai wa miliyoyin Musulmai damar sauraron saƙonnin huɗubar cikin yarukan da s**a fi fahimta.

Shirin, wanda Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Masallacin Harami da Masallacin Annabi ﷺ ke jagoranta, zai kasance kai tsaye ta hanyoyin sadarwa na zamani da tashoshin yaɗa labarai masu alaƙa da aikin Hajji.

Hausa da Yarbanci na daga cikin jerin manyan harsunan da aka amince da su tare da Turanci, Faransanci, Indonesiya, Urdu, Turkanci, Farisanci, Sinanci, Rashanci, Hindi, Swahili da wasu da dama daga sassa daban-daban na duniya.

Mahukuntan Saudiyya sun ce manufar wannan shiri ita ce tabbatar da cewa saƙonnin addini, nasiha da darussan da ke cikin huɗubar Arfa sun isa ga Musulmai a ko'ina cikin duniya ba tare da tangarɗar harshe ba.

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Harami da Masallacin Annabi ﷺ, Abdulrahman Al-Sudais, ya bayyana cewa aikin fassarar huɗubar Arfa na daga cikin manyan shirye-shiryen da aka gina bisa gogewa da aka tara tsawon shekaru.

Ya ce shirin zai ba Musulman da ba sa jin Larabci damar amfana da saƙonnin ɗabi'a da jinƙai da huɗubar ke ɗauke da su, tare da isar da saƙon Musulunci na zaman lafiya ga duniya baki ɗaya.

Huɗubar Arfa, wadda ake gabatarwa a Dutsen Arafat a lokacin Hajji, na daga cikin mafi muhimmancin huɗubobi a Musulunci, kuma miliyoyin Musulmai a faɗin duniya na bibiyarta a kowace shekara.

A wani ɓangare kuma, mahukuntan Saudiyya sun sake tunatar da ƙasashen da ke halartar Hajji da su tabbatar da wayar da kan alhazansu kan bin ƙa'idojin aikin Hajji domin tabbatar da tsaro da nasarar gudanar da ibadar.

Hukumar Alhazai ta Ƙasa ta Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa tana ci gaba da daidaita ayyukanta da tsarin zamani, inda sashen fasahar sadarwa na hukumar ke aiki kan cikakken tsarin zamani domin inganta ayyukan Hajji daidai da hangen nesa na Saudiyya na shekarar 2030.

Masu lura da harkokin Hajji sun bayyana saka Hausa da Yarbanci cikin harsunan da za a fassara huɗubar Arfa a matsayin wani muhimmin mataki da ke nuna muhimmancin al'ummar Musulman Najeriya a duniya, tare da bai wa miliyoyin masu magana da waɗannan harsuna damar sauraron huɗubar kai tsaye cikin sauƙi da fahimta.

Najeriya da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin ArzikiGwamnatin Tarayya ta bayyana shirinta na yin aiki ...
22/05/2026

Najeriya da Poland Za Su Hada Kai Kan Tsaro da Bunƙasa Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya ta bayyana shirinta na yin aiki kafada da kafada da ƙasar Poland wajen inganta harkokin tsaron cikin gida da bunƙasa tattalin arziki.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan yayin da ya karɓi Mataimakin Firaministan Poland, Krzysztof Gawkowski, a ofishinsa da ke Abuja ranar Alhamis.

Tunji-Ojo ya ce Najeriya na da burin anfani da ƙwarewar Poland wajen kula da iyakoki da kuma dabarun tsaron cikin gida da s**a tabbatar da nasara a ƙasar.

Ya ce gwamnatin Najeriya na sa ran yin haɗin gwiwa da Poland musamman a fannoni kamar horas da jami’ai, amfani da fasaha, tsaron yanar gizo da sauran muhimman fannoni.

“Mun yi imani cewa haɗin kai da koyo daga juna ne hanya mafi dacewa wajen rage rauninmu tare da ƙarfafa bangarorin da muke da ƙwarewa,” in ji shi.

Ministan ya tabbatar wa baƙin cewa ziyarar ba za ta zama ta al’ada kawai ba, domin za ta zama tubalin da za a gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.

Ya kuma bayyana cewa ana shirye-shiryen kai ziyara ƙasar Poland domin ƙara zurfafa tattaunawa da gwamnatin ƙasar da kuma ɓangaren kasuwanci masu alaƙa da ma’aikatar harkokin cikin gida.

Tunji-Ojo ya ƙara da cewa manufofin tattalin arzikin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na nuna cewa gwamnati na fahimtar hanyoyin gina tattalin arziki mai ƙarfi.

A nasa jawabin, Mataimakin Firaministan Poland, wanda kuma shi ne Ministan Harkokin Dijital na ƙasar, Krzysztof Gawkowski, ya ce Najeriya ƙasa ce mai tarin albarkatun tattalin arziki, yawan jama’a da kuma damar ci gaban fasaha.

Ya bayyana Najeriya a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa wajen gina dangantaka mai ɗorewa tsakanin ƙasashen biyu.

Gawkowski ya ce Poland a shirye take ta taimaka wa Najeriya ta hanyar ƙwarewarta a fannoni kamar kirkire-kirkire, fasahar zamani, gina ababen more rayuwa da kuma sabbin dabarun fasaha.

Haka kuma ya bayyana fatan ganin Ministan Harkokin Cikin Gida na Najeriya ya kai ziyara Poland domin ƙara ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu.

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Najeriya Da Soke Shari’a A ArewaFadar Shugaban Kasa ta karyata wani ...
22/05/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Najeriya Da Soke Shari’a A Arewa

Fadar Shugaban Kasa ta karyata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke dokar Shari’a a Arewacin kasar.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar 21 ga watan Mayun 2026, gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin “labarin karya” da wasu ke yadawa domin haddasa rikici da tayar da hankalin jama’a gabanin babban zaben 2027.

Sanarwar ta ce babu wani kudiri da Shugaba Tinubu ke shirin aikewa Majalisar Dokoki ta Kasa mai suna “Project True Federation” kamar yadda ake yadawa.

Fadar shugaban kasar ta zargi masu yada rahoton da kokarin haifar da rabuwar kai da rikicin siyasa a kasar.

“’Yan Najeriya su yi watsi gaba daya da wannan labari saboda masu yada shi makiyan zaman lafiya ne kuma masu neman tayar da tarzoma,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa sauya kundin tsarin mulkin kasa ba abu ne da shugaban kasa ko majalisa za su yi kai tsaye ba, domin akwai matakai masu tsauri da s**a hada da samun amincewar kashi biyu bisa uku na majalisun dokokin kasar da kuma majalisun dokokin jihohi 24.

Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu na mayar da hankali ne wajen aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki da gwamnatin sa ta fara domin inganta rayuwar ’yan Najeriya.

Fadar shugaban kasar ta gargadi jama’a da su rika taka-tsantsan wajen karanta da yada rahotannin karya musamman yayin da harkokin yakin neman zabe ke kara karatowa.

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Farfesa Segun Aina a matsayin sabon Magatakardar Hukumar Shirya Jarabawar Sh...
22/05/2026

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya naɗa Farfesa Segun Aina a matsayin sabon Magatakardar Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu ta Ƙasa (JAMB), inda zai gaji Farfesa Is-haq Oloyede, wanda wa’adinsa na biyu zai ƙare a ranar 31 ga Yuli, 2026.

Hakan na ƙunshe a wata sanarwa da Bayo Onanuga mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan labarai da dabaru ya sanyawa hannu a yau Alhamis 21/5/2026.

Farfesa Aina, wanda zai cika shekara 40 a watan Yuli, fitaccen masani ne kuma ƙwararren masani a fannin tsarin kwamfuta, tare da gogewa mai yawa a tsarin jarabawar ƙasa, gine-ginen fasahar zamani, da gyaran cibiyoyin gwamnati.

Ya samu digirin farko na Injiniyan Tsarin Kwamfuta daga Jami’ar Kent, sannan ya yi digirin MSc a fannin Intanet da Tsaron Sadarwa, da kuma digirin PhD a fannin Sarrafa Sigina na Dijital, duk daga Jami’ar Loughborough da ke Ƙasar Birtaniya. Haka kuma ya kammala Shirin Babban Gudanarwa a Lagos Business School.

A matsayin Farfesan Injiniyan Kwamfuta a Jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ile-Ife, Aina ya fara aiki da JAMB ne lokacin yi wa ƙasa hidima (NYSC), inda ya samu ƙwarewar farko a tsarin shiga jami’o’i na ƙasa da kuma tafiyar da bayanai. Wannan gogewa ce ta taimaka wajen ci gaba da gudummawarsa wajen gyaran tsarin jarabawa da inganta ayyuka.

Da fiye da shekaru 15 na gogewa bayan kammala karatu, Farfesa Aina na aiki a haɗuwar fasaha, manufofi, da sauye-sauyen cibiyoyi, inda yake bai wa gwamnatocin tarayya da jihohi shawara kan tsara tsare-tsare, sauya tsarin zuwa na dijital, da gyaran ayyuka.

Yana da shekara 39 lokacin da ya zama ɗaya daga cikin mafi ƙarancin shekaru da s**a zama Farfesan Injiniyan Kwamfuta a Najeriya, kuma yanzu zai kafa tarihi a matsayin mafi ƙarancin shekaru da s**a taɓa zama Magatakardan JAMB.

Ya kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara ga manyan hukumomin shirya jarabawa, ciki har da NECO, NABTEB, da ma’aikatun ilimi na jihohi daban-daban, inda ya bayar da ƙwarewa a tsarin ICT, tabbatar da ingancin jarabawa, da inganta tsarin dijital.

Farfesa Aina memba ne na ƙungiyoyin ƙwararru da dama, ciki har da Council for the Regulation of Engineering in Nigeria (COREN), Nigerian Society of Engineers (NSE), Institute of Electrical and Electronics Engineers (IEEE), da Institution of Engineering and Technology (IET).

Shugaba Tinubu na sa ran Farfesa Aina zai yi amfani da dimbin gogewarsa, iliminsa, da fahimtarsa ta aiki wajen tafiyar da hukumar, domin ɗaga wannan muhimmiyar cibiyar ilimi zuwa matakin da ya fi wanda magabacinsa ya kai.

Yadda Ake Maida Arewacin Najeriya Cibiyar Zuba Jari Ta Hanyar Manufofin Shugaba TinubuDaga Aliyu SambaArewacin Najeriya ...
20/05/2026

Yadda Ake Maida Arewacin Najeriya Cibiyar Zuba Jari Ta Hanyar Manufofin Shugaba Tinubu

Daga Aliyu Samba

Arewacin Najeriya yana fuskantar gagarumin sauyi na tattalin arziki wanda ke mayar da yankin wata babbar cibiya ta zuba jari da kasuwanci a Afirka ta Yamma. Wannan ci gaba ba ya rasa nasaba da tsare-tsare da kudaden shiga na musamman da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke turawa yankin ta karkashin tsarin Renewed Hope Agenda.

Gwamnatin tarayya ta mayar da hankali ga samar da ababen more rayuwa, bunkasa makamashi, da inganta fannin noma domin janyo hankalin masu zuba jari na gida da na waje.

1. Manyan Ayyukan Hanya da Sufuri (Infrastructure)
Ayyukan Hanyoyi na Musamman: Cikin ayyukan guda 260 da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ke aiwatarwa a fadin kasa, yankin Arewa maso Yamma kadai yana da guda 48 da ake gudanarwa a yanzu. Wannan ya hada da hanyar Kaduna Western Bypass da ta shafe shekaru 22 tana mace wadda yanzu ta kusa kammala, da kuma amincewa da gina hanyar Mando zuwa Birnin Gwari ta kilomita 122 akan kudi N178 billion.
Sufurin Jirgin Kasa na Zamani: Aikin layin dogo na Kaduna-Kano-Katsina-Maradi (Jamhuriyar Nijar) wanda ke da tsawon kilomita 203 yana cigaba da gudana. Wannan layin dogo zai hada kasuwannin Arewa kai tsaye da tashar jirgin kasa ta cikin kasa ta Dala Dry Inland Port da ke Kano, lamarin da zai saukaka jigilar kayayyaki zuwa kasashen waje.
Babban T**i na Sokoto-Badagry Super Highway: Wannan babban t**i mai tsawon kilomita 1,068 zai hada Arewa da Kudancin kasar ta fannin kasuwanci da zuba jari.
2. Juyin Juya Hali a Fannin Noma da Ruwa
Domin tabbatar da cewa Arewa ta kasance jagaba wajen samar da abinci da albarkatun masana'antu, gwamnatin Tinubu ta zuba biliyoyin nairori a fannin banruwa da raya karkara.

Aikin Banruwa na Garko: Gwamnatin ta hanyar asusun kiyaye muhalli (Ecological Fund) ta zuba kudi har Naira Biliyan 27 don samar da dandalin noman rani na zamani.
Taimakon Masu Noma: An kafa cibiyar fasahar noma ta Agricultural Incubation Centre mai fadin hekta 10 ta hanyar hukumar NASENI don koya wa matasa da manoma dabarun kasuwancin noma na zamani.
3. Fadada Fannin Makamashi da Gas (Energy Sector)
Bayan aiwatar da dokar masana'antar man fetur (PIA), gwamnatin Tinubu ta samar da sabbin sauye-sauye don amfani da iskar gas (Natural Gas) wajen gudanar da masana'antun Arewa.

A taron makamashi na Nigeria International Energy Summit (NIES), an bayyana cewa samar da iskar gas a cikin gida ya zarce 2 BSCFD a karon farko, kuma ana amfani da wannan damar wajen samar da wutar lantarki ta hanyar amfani da hasken rana (Solar energy projects) wanda Hukumar Makamashi ta Najeriya (ECN) ke kafawa a sassan Arewa don rage tsadar gudanar da masana'antu.

4. Lafiya da Habaka Jari na Dan Adam (Human Capital)
Zuba jari ba zai dore ba idan babu koshin lafiya da ilimi ga al'umma. Shi ya sa gwamnatin tarayya ta amince da gina manyan asibitoci da cibiyoyin kwarewa:

Abubuwan more rayuwa irin su asibitin kwararru na Bola Ahmed Tinubu Specialist Hospital mai gado 300 a Kaduna, da asibitin koyarwa na Aminu Kano Teaching Hospital (inda ake gina cibiyoyin cututtukan zuciya da na yara), suna tabbatar da cewa ma'aikata da masu zuba jari za su samu kyakkyawan tsarin kiwon lafiya.

Bugu da kari, shirin Renewed Hope Baby Support (RHBS) wanda Hukumar Raya Shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC) ta kaddamar yana taimaka wa mata da yara ta hanyar hada harkar lafiya da rajistar zama dan kasa, wanda ke zama ginshikin gina al'umma mai inganci.

Me Yasa Za A Zuba Jari a Arewacin Najeriya Yanzu?
Kamata ya yi masu zuba jari su gane cewa kudaden shiga da gwamnatin tarayya ke samu bayan cire tallafin mai da gyaran tsarin canjin kudi ana tura su ne kai tsaye zuwa ga ayyukan raya kasa. Kamar yadda gwamnonin yankin (kamar na Kaduna da Jigawa) s**a tabbatar, karuwar kudaden shiga daga gwamnatin tarayya ya ba su damar bude sabbin yankunan masana'antu da hanyoyin karkara.

Yanzu ne mafi kyawun lokaci ga masu zuba jari na gida da na kasashen waje za su karkata akalarsu zuwa Arewacin Najeriya, domin samun moriyar saukin sufuri, yalwar makamashi, da kasuwa mai fadi da gwamnatin Shugaba Tinubu ta shimfida.

Ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji zai ƙara amincewar jama’a da tsarin haraji – Ministan Yaɗa LabaraiGwamnatin Tarayy...
20/05/2026

Ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji zai ƙara amincewar jama’a da tsarin haraji – Ministan Yaɗa Labarai

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyar ta ta gina tsarin gudanar da haraji mai tsare gaskiya, tare da mayar da hankali kan buƙatun ’yan ƙasa, a wani ɓangare na Ajandar Sabunta Fata ta Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan ranar Litinin a Abuja yayin ƙaddamar da gidan yana na hukumar da kuma cibiyar karɓar kiran waya kyauta ta ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji.

Ministan ya bayyana ƙaddamar da sababbin dandalan a matsayin wani babban mataki na ƙarfafa amincewar jama’a da tsarin haraji a Nijeriya.

Ya ce: “Wannan wani babban mataki ne wajen ƙarfafa amincewar jama’a da inganta samun damar amfani da ayyuka tare da tabbatar da adalci a tsarin gudanar da haraji na Nijeriya.

"Ingantacciyar hanyar sadarwa da haɗin kan jama’a suna da muhimmanci wajen tabbatar da nasarar irin waɗannan sauye-sauyen tattalin arzikin.”

A cewar Idris, gwamnatin Shugaba Tinubu tana ci gaba da aiwatar da muhimman sauye-sauye domin ƙarfafa tara kuɗaɗen shiga, tabbatar da ɗorewar tattalin arziki da kuma bunƙasa cigaban ƙasa.

Ya ce: “Ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, Gwamnatin Tarayya tana ci gaba da jajircewa wajen gina tattalin arziki mai ƙarfi, mai ɗorewa kuma mai wadata ta hanyar muhimman sauye-sauye masu ma’ana.”

Ministan ya ce haraji yana taka muhimmiyar rawa wajen cigaban ƙasa ta hanyar samar wa gwamnati kuɗaɗen da ake amfani da su wajen bunƙasa ababen more rayuwa da kiwon lafiya da ilimi da sufuri da tsaro.

Sai dai ya jaddada cewa tsarin gudanar da haraji ba zai yi nasara ta hanyar tilastawa kawai ba, sai an gina shi bisa amincewar jama’a da gaskiya da adalci.

Ya ce: “Tsarin gudanar da haraji ba zai yi nasara ta hanyar tilastawa kawai ba. Dole ne ya samu goyon bayan jama’a tare da kasancewa bisa gaskiya da adalci da kuma ingantacciyar sadarwa.”

Idris ya bayyana cewa ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji wata muhimmiyar gada ce tsakanin masu biyan haraji da hukumomin haraji, domin tabbatar da cewa ’yan Nijeriya na samun damar gabatar da ƙorafe-ƙorafe cikin gaskiya da ƙwarewa.

Ya yaba da ƙaddamar da cibiyar karɓar kiran waya kyauta da kuma shafin gidan yana na hukumar, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen sauƙaƙa sadarwa da samun bayanai da ayyuka.

“Ƙaddamar da cibiyar karɓar kiran waya kyauta tana nuna aniyar gwamnati ta kawar da matsalolin sadarwa tare da tabbatar da cewa ’yan Nijeriya za su iya neman bayanai da gabatar da tambayoyi da kuma warware ƙorafe-ƙorafen su ba tare da wata wahala ko ƙarin kuɗi ba.”

Ministan ya jaddada muhimmancin wayar da kan jama’a kan haraji domin ƙarfafa biyan haraji da kuma inganta kishin ƙasa.

“Wayar da kai kan haraji ba wai don tara kuɗaɗen shiga kawai ba ne, don gina al’adar haɗin kan ƙasa da ɗaukar alhaki tare ne,” inji shi.

Ya yi gargaɗin cewa yaɗa labaran ƙarya da rashin ingantacciyar sadarwa suna hana sauye-sauyen gwamnati samun karɓuwa tare da haifar da rashin amincewa daga jama’a.

Ya ce: “Yaɗa labaran ƙarya da rashin isasshiyar sadarwa s**an haifar da rashin amincewa da kuma ƙin karɓar sauye-sauye. Wannan yana nuna muhimmancin amfani da kafafen yaɗa labarai yadda ya kamata da kuma ci gaba da wayar da kan jama’a.”

Ministan ya sake tabbatar da cewa Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai za ta ci gaba da tsare aiki tare da Ofishin Tax Ombud da sauran hukumomin da abin ya shafa domin wayar da kan jama’a kan sauye-sauyen haraji da haƙƙin masu biyan haraji da hanyoyin warware ƙorafe-ƙorafe.

Ya ƙara da cewa ingantacciyar sadarwa za ta taimaka wajen fahimtar rawar da haraji ke takawa wajen tallafa wa Ajandar Sabunta Fata da ci gaban ƙasa.

Ministan ya taya Ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji murnar ƙaddamar da sabbin dandalan tare da kira ga masu ruwa da tsaki da su ci gaba da haɗa kai domin gina tsarin haraji mai gaskiya da inganci wanda zai amsa buƙatun ’yan Nijeriya.

Taron ya samu halartar Ministan Kuɗi kuma Mai Kula da Tattalin Arziki, Mista Taiwo Oyedele; Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Misis Didi Esther Walson-Jack; Shugaba kuma Babban Jami’in Gudanarwa na Ofishin kula da ƙorafe-ƙorafen haraji, John C. Nwabueze; da sauran manyan jami’an gwamnati da masu ruwa da tsaki.

Address

Kano

Telephone

+2349028483925

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fasihiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fasihiya:

Share