Fasihiya

Fasihiya Labaran Hausa Rahotanni, Adabi bunkasa aikin fasaha.

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Kashe Naira Biliyan 46 Domin Gyaran Filin Jirgin Sama na KanoDaga Aliyu SambaGwamnatin Ta...
29/07/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Kashe Naira Biliyan 46 Domin Gyaran Filin Jirgin Sama na Kano

Daga Aliyu Samba

Gwamnatin Tarayya ta amince da ware Naira biliyan 46 domin gudanar da aikin gyaran manyan filayen sauka da tashin jiragen sama (runways) na Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Mallam Aminu Kano (MAKIA), a wani yunƙuri na inganta tsaro da ingancin harkokin sufurin jiragen sama a ƙasar nan.

Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama da Bunƙasa Sararin Samaniya, Festus Keyamo, ne ya bayyana hakan a ranar Laraba yayin ƙaddamar da sabon ginin tashar jiragen sama ta cikin gida ta Muhammadu Adamu Dankabo da aka kammala gyaranta a filin jirgin saman na Kano.

Keyamo ya ce aikin gyaran manyan filayen jiragen saman zai ƙara tabbatar da tsaron zirga-zirgar jirage, sauƙaƙe gudanar da ayyukan sufurin sama tare da inganta jin daɗin fasinjoji. Ya ƙara da cewa hakan zai ƙara ɗaga matsayin Kano a matsayin babbar cibiyar harkokin jiragen sama a Arewacin Najeriya.

Ya bayyana cewa amincewar da gwamnatin ta bayar na cikin shirinta na ci gaba da inganta ababen more rayuwa a fannin sufurin jiragen sama, domin ƙara inganci, tsaro da bunƙasa ayyukan wannan fanni a faɗin ƙasar.

A yayin ziyarar tasa, Ministan ya kuma ƙaddamar da tashar cikin gida ta Muhammadu Adamu Dankabo da aka sabunta, wadda aka gyara domin inganta ayyukan karɓar fasinjoji da samar da ingantattun kayayyakin more rayuwa a filin jirgin saman.

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sauya Tsarin Tallafa wa Mata Zuwa Gina Arziki Mai ƊorewaGwamnatin Tarayya ta ce za ta karkata ...
29/07/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Sauya Tsarin Tallafa wa Mata Zuwa Gina Arziki Mai Ɗorewa

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta karkata shirin tallafa wa mata zuwa gina arziki mai ɗorewa maimakon rabon tallafin wucin gadi, domin kawo ƙarshen abin da ta kira “career beneficiaries” wato mutanen da ke ci gaba da karɓar irin wannan tallafi akai-akai. Domin cimma wannan buri, Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Haɗa Jama’a da Tsarin Tattalin Arziki da Kuɗi (PreCEFI), tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Harkokin Mata, za su shirya taron She’sIncluded 2026 a ranakun 19 zuwa 20 ga Agusta a Banquet Hall na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Mai bai wa Shugaban Ƙasa shawara kan haɗa jama’a cikin tattalin arziki da kuɗi, Dakta Nurudeen Zauro, ya ce taron zai tattaro jami’an gwamnati, hukumomin kula da harkokin kuɗi, bankuna, masu zaman kansu da abokan hulɗar ci gaba domin samar da hanyoyin da za su ƙara wa mata damar samun jari, shiga kasuwanci, fasaha da samar da ayyukan yi. Ya ce taron na bana mai taken “Designing for Delivery: Financing. Systems. Scale.” zai mayar da hankali ne kan aiwatar da yarjejeniyar A*o Accord da aka cimma a shekarar 2025.

Ministar Harkokin Mata, Imaan Sulaiman-Ibrahim, ta ce sake gudanar da taron karo na biyu alama ce da ke nuna tasirin shirin. Ta bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na son sauya tsarin da mata ke kasancewa masu karɓar tallafi kawai zuwa wanda zai ba su damar zama masu kafa kasuwanci, masu zuba jari da masu samar da ayyukan yi. A cewarta, ba za a iya cimma cikakken ci gaban ƙasa ba idan aka bar rabin al’umma a baya.

Ministar ta kuma bayyana cewa gwamnati na ƙarfafawa mata su shiga sassan tattalin arziki da s**a haɗa da mak**ashi ta hanyar shirin Women in the Natural Gas and Sustainable Energy (WINGS), domin su zama masu kera silinda, mallakar cibiyoyin gas da gudanar da kasuwanci a fannin mak**ashi. Ta kuma yi kira da a samar da tsarin bayanan masu cin gajiyar shirye-shiryen gwamnati ta hanyar bayanan (biometric), domin dakile maimaita karɓar irin wannan tallafi ba tare da ci gaba ba, tana mai cewa manufar gwamnati ita ce ta samar da mata masu ƙirƙirar arziki, ba masu dogaro da tallafi ba.

Shugaba Tinubu Ya Ba da Umarnin Farautar Maharan Kaduna Tare Da Ceto Wadanda Aka SaceShugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ...
28/07/2026

Shugaba Tinubu Ya Ba da Umarnin Farautar Maharan Kaduna Tare Da Ceto Wadanda Aka Sace

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da harin da aka kai ƙauyen Naridon da ke Ƙaramar Hukumar Kauru a Jihar Kaduna, inda ya umarci rundunonin tsaro su gaggauta farautar maharan tare da kuɓutar da mutanen da aka yi garkuwa da su.

Harin da aka kai da sanyin safiyar Litinin a unguwar Kamaru ya yi sanadin mutuwar kimanin mutum 30, ciki har da mata da yara, yayin da aka ƙone gidaje da dama. Shugaba Tinubu ya bayyana harin a matsayin dabbanci da rashin tausayi da aka aikata kan fararen hula marasa laifi.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Talata a Abuja, shugaban ya ce ya bai wa rundunar soji, 'yan sanda da hukumomin leƙen asiri umarnin ƙara zafafa sintiri da ayyukan tsaro domin kamo masu laifin cikin gaggawa, ceto waɗanda aka sace da kuma dawo da zaman lafiya a yankin.

Tinubu ya kuma gargaɗi masu ƙoƙarin tarwatsa zaman lafiyar da ake samu a Kaduna cewa ba za su tsere wa hukunci ba. Ya miƙa ta'aziyyarsa ga iyalan waɗanda s**a rasu, da Gwamna Uba Sani, da Gwamnatin Jihar Kaduna, tare da al'ummar jihar baki ɗaya.

Shugaban ya tabbatar da cewa Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da bai wa Kaduna cikakken goyon baya wajen yaƙi da matsalolin tsaro, yana mai jaddada ƙudirin gwamnatinsa na ƙarfafa kayan aikin tsaro da murƙushe ƙungiyoyin masu aikata laifuka. Haka kuma ya buƙaci al'umma su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai domin dakile hare-hare tun kafin su faru.

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba da Sabon Ɗakin Watsa Labarai na Zamani na NTA da Gyaran Cibiyar 'Yan Jarida ta ƘasaMinista...
28/07/2026

Ministan Yaɗa Labarai Ya Yaba da Sabon Ɗakin Watsa Labarai na Zamani na NTA da Gyaran Cibiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana gamsuwar sa kan sabon ɗakin watsa shirye-shiryen talbijin na zamani da aka kammala a hedikwatar Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), tare da cigaban da aka samu a aikin gyaran Cibiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (National Press Centre).

Idris, wanda ya bayyana cewa waɗannan ayyuka hujja ne ƙarara da ke nuna ƙudirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na zamanantar da cibiyoyin yaɗa bayanai na gwamnati, ya bayyana haka ne a ranar Litinin bayan ya duba waɗannan cibiyoyi da ke Abuja.

A cewar sa, waɗannan zuba jari wani ɓangare ne na ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na sake fasalta kafafen yaɗa labarai na gwamnati domin su samar wa da 'yan Nijeriya ingantaccen aikin watsa shirye-shirye da yaɗa bayanai.

Ya ce: "Abin da muka gani a yau cika alƙawarin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne na zamanantar da cibiyoyin watsa shirye-shiryen gwamnati a Nijeriya. Wannan yana ɗaya daga cikin mafi kyawun ɗakunan watsa shirye-shirye a Nijeriya, kuma yana cikin mafi inganci a nahiyar Afrika."

Ministan ya ce sabon situdiyon yana cikin mafi ingancin cibiyoyin watsa shirye-shirye a Afrika, kuma wani ɓangare ne na babban shirin zuba jari da ake aiwatarwa a NTA, Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Muryar Nijeriya (VON) da Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN).

Ya yaba wa shugabanni da ma'aikatan NTA bisa goyon bayan da suke bai wa shirin sauye-sauyen, yana mai cewa gyaran ba ya tsaya kan gine-gine kawai, har ma ya shafi inganta shirye-shirye, ƙwarewar aiki, ƙirƙire-ƙirƙire da bunƙasa ƙwarewar ma'aikata.

Ya ce aikin sayo sababbin kayan aikin watsa shirye-shirye na zamani ga tashoshin NTA a faɗin ƙasar nan, tare da irin wannan zuba jari a sauran kafafen yaɗa labarai na gwamnati, zai inganta matuƙa aikin watsa shirye-shiryen hidimar jama'a a Nijeriya.

Idris ya bayyana cewa sake ƙaddamar da shirin sauya fasahar watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital (Digital Switch Over – DSO) wata babbar nasara ce wadda ke ƙara ƙarfafa shirin zamanantar da harkar watsa shirye-shirye a Nijeriya.

Ya ce: "Shirin 'Digital Switch Over' da kuma zuba jari a sababbin kayan aikin watsa shirye-shirye sun buɗe sabon babi ga fannin yaɗa bayanai a Nijeriya. Da zarar an kammala wannan shirin gyare-gyare, 'yan Nijeriya za su shaida cikakken sauyi a tsarin watsa shirye-shiryen gwamnati."

Ministan ya kuma bayyana cewa Shugaba Tinubu ya himmatu wajen inganta walwalar ma'aikatan fannin yaɗa labarai, yana mai jaddada cewa gwamnatin na fahimtar muhimmancin zuba jari ba kawai a gine-gine da kayan aiki ba, har ma a kan ma'aikata.

Bayan kammala duba cibiyoyin NTA, Ministan ya ziyarci Cibiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa da ke Radio House, inda ya nuna gamsuwa da yadda aikin gyaran yake tafiya.

Ya ce sabuwar Cibiyar 'Yan Jaridar za ta zama cibiyar aikin kafafen yaɗa labarai ta zamani mai ɗauke da kayan aiki na duniya da kuma intanet mai saurin gaske domin taimaka wa 'yan jarida masu bibiyar harkokin gwamnati da manyan abubuwan da ke faruwa a ƙasa.

Ya ce: "Dole ne Cibiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa ta cika manufar ta ta kasancewa babbar cibiyar aikin kafafen yaɗa labarai a Nijeriya. Ana sake fasalta ta ne domin samar wa 'yan jarida da yanayi mai kyau da kuma kayayyakin zamani da za su taimaka masu wajen gudanar da aikin su yadda ya k**ata."

Ministan ya buƙaci 'yan kwangilar da ke aikin da su kammala shi a cikin wa'adin da aka tsara, yana mai cewa zai sake dawowa domin yin dubawar ƙarshe kafin a ƙaddamar da cibiyar.

Ya sake jaddada cewa gyare-gyaren da ake yi a kafafen yaɗa labarai na gwamnati suna nuna ƙudirin Shugaba Tinubu na ƙarfafa sadarwa da jama'a, inganta yaɗa sahihan bayanai da kuma ɗaga darajar fannin yaɗa labarai na Nijeriya zuwa matakin ƙasa da ƙasa.

An Hallaka 'Yan Ta'adda da Dama a Sabbin Hare-haren Sojoji Ta Sama da Ƙasa a Faɗin NajeriyaDakarun Rundunar Sojin Najeri...
25/07/2026

An Hallaka 'Yan Ta'adda da Dama a Sabbin Hare-haren Sojoji Ta Sama da Ƙasa a Faɗin Najeriya

Dakarun Rundunar Sojin Najeriya sun kashe 'yan ta'adda da dama tare da tarwatsa maboyarsu a wasu sabbin hare-hare da s**a kai ta sama da ƙasa a jihohin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma. Hare-haren da aka gudanar ƙarƙashin Operation HADIN KAI da Operation FANSAN YAMMA sun kuma haifar da ceto waɗanda aka sace, k**a masu garkuwa da mutane da kuma ƙwato mak**ai da sauran kayayyakin sadarwa.

A Jihar Borno, dakarun Bataliya ta 212 sun k**a wani da ake zargin ɗan ƙungiyar ISWAP ne a kan hanyar Maiduguri zuwa Monguno, inda aka same shi da na'urar Starlink, na'urar Wi-Fi mai tashoshi shida, wayar salula da kuɗi. Haka kuma, dakarun Bataliya ta 82 sun ceto wasu 'yan mata biyu a yankin Gwoza, waɗanda s**a bayyana cewa an sace su tun watan Agustan 2025 a kan hanyar Pulka zuwa Ngoshe, kuma s**a tsere daga sansanin 'yan ta'adda da ke Dutsen hMandara.

A Jihar Yobe kuwa, dakarun Brigade ta 27 sun daƙile wani harin dare da 'yan ta'adda s**a kai wani wurin binciken sojoji a hanyar Buni Yadi zuwa Buni Gari da ke ƙaramar hukumar Gujba. Sai dai sojoji biyu sun rasa rayukansu yayin fafatawar, yayin da aka lalata motar yaƙi ta 'yan ta'addan. A wani samame kuma, dakarun Bataliya ta 233 tare da haɗin gwiwar mafarauta sun k**a mutane biyar da ake zargin masu garkuwa da mutane ne a ƙauyen Jegalari na ƙaramar hukumar Fune, inda aka ƙwato bindigogi, alburusai da wayoyin hannu.

Rahoton ya ce hare-haren sama da aka kai bisa bayanan sirri sun yi mummunar illa ga 'yan ta'adda. A yankin Kala Balia da ke ƙaramar hukumar Marte ta Borno, jiragen yaƙin sama sun kashe kusan 'yan ta'adda 15 bayan an gano maboyarsu. Haka kuma, a wani harin dare da aka kai tsakanin Bama da Maiduguri, an kashe wasu 'yan ta'adda takwas bayan jiragen yaƙi sun yi luguden wuta kan wuraren da aka gano motsinsu.

A Arewa maso Yamma, dakarun Operation FANSAN YAMMA sun fafata da 'yan ta'adda a Dutsen Gambada da ke ƙaramar hukumar Gummi ta Jihar Zamfara. Haka kuma, dakarun Brigade ta 12 sun hana wani yunƙurin satar mutane a kan hanyar Kabba zuwa Ayere a Jihar Kogi tare da ceto mutum shida da aka sace, waɗanda aka kai Asibitin St. Joseph da ke Kabba domin kula da lafiyarsu. A Jihar Nasarawa ma, dakarun Operation WHIRL STROKE sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi a yankin Tunga na ƙaramar hukumar Awe.

A Kudu maso Gabas kuwa, dakarun Operation UDO KA sun kai samame wani maboyar masu aikata laifuka a yankin Awara Waterside, inda s**a ƙwato bindigogin Lee-Enfield da G3 tare da alburusai masu yawa. Rundunar Sojin Najeriya ta ce waɗannan nasarori sun nuna cewa ana ci gaba da matsa wa 'yan ta'adda da masu garkuwa da mutane lamba ta hanyar amfani da ingantattun bayanan sirri da haɗin gwiwar hare-haren sama da ƙasa, tare da jaddada aniyarta na ci gaba da yaƙi har sai an kawar da dukkan ƙungiyoyin masu aikata laifuka a faɗin ƙasar.

Dakarun Operation HADIN KAI Sun Cafke Mutane Biyar da Ake Zargi da Garkuwa da Mutane a YobeDakarun rundunar Operation HA...
25/07/2026

Dakarun Operation HADIN KAI Sun Cafke Mutane Biyar da Ake Zargi da Garkuwa da Mutane a Yobe

Dakarun rundunar Operation HADIN KAI tare da haɗin gwiwar ƙungiyar mafarauta ta Jihar Yobe sun k**a wasu mutane biyar da ake zargi da hannu a ayyukan garkuwa da mutane a ƙauyen Jegalari da ke ƙaramar hukumar Fune ta jihar.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar ranar Juma’a, ta ce jami’an Bataliya ta 233 da ke sansanin soji na Damaturu ne s**a gudanar da samamen bayan samun sahihan bayanan sirri kan ayyukan waɗanda ake zargin.

Sanarwar ta ce a yayin samamen, an ƙwato bindigogi uku ƙirar AK-47 da aka ƙera a gida, bindiga guda ta gida, harsasai iri-iri da kuma wayoyin hannu huɗu da ake zargin suna da alaƙa da ayyukan laifin.

Rundunar ta ce ana ci gaba da tsare waɗanda ake zargin tare da kayayyakin da aka ƙwato domin gudanar da bincike da tantance rawar da s**a taka a laifukan garkuwa da mutane da sauran ayyukan ta’addanci.

Operation HADIN KAI ta jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da hare-haren da s**a dogara da bayanan sirri domin hana ‘yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka samun damar gudanar da ayyukansu a yankin Arewa maso Gabas.

Har ila yau, rundunar ta buƙaci al’umma su kasance masu sa ido tare da kai rahoton duk wani motsi ko mutum da ake zargi ga jami’an tsaro mafi kusa, tana mai cewa haɗin kan jama’a da bayar da sahihan bayanai na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaron al’umma.

Rundunar soja ta wanke mutumin da aka zarga da alaƙa da ’yan ta’addaRundunar sojin Nijeriya ta "Operation Haɗin Kai" ta ...
24/07/2026

Rundunar soja ta wanke mutumin da aka zarga da alaƙa da ’yan ta’adda

Rundunar sojin Nijeriya ta "Operation Haɗin Kai" ta bayyana cewa ta wanke wani mutum da a baya aka ruwaito a matsayin wanda ake zargi da alaƙa da ’yan ta’adda, bayan bincike ya tabbatar da cewa ba shi da wata alaƙa da kowace ƙungiyar ta’addanci.

A cikin wata sanarwa da Muƙaddashin Jami’in Yaɗa Labarai na Rundunar, Kyaftin Mohammed Goni, ya fitar a yau Alhamis, rundunar ta ce mutumin, mai suna Aboubakar Muhammad Zein-Nur, wanda aka fi sani da Houdairi, sojojin Bataliya ta 68 sun k**a shi ne yayin wani samame na bibiyar bayanai bayan harin da aka kai a Cross Kauwa.

Sanarwar ta bayyana cewa an tsare shi ne bisa ƙa’idojin aiki na rundunar saboda halin rashin tsaro da ake ciki a yankin Arewa-maso-gabas da kuma yadda ’yan ta’adda ke amfani da hanyoyin kan iyaka wajen zirga-zirga da safarar kayayyakin aikin su.

Ta ce cikakken binciken sirri da sauran matakan bincike sun tabbatar da cewa Zein-Nur ba shi da wata alaƙa da kowace sananniyar ƙungiyar ta’addanci.

Binciken ya kuma nuna cewa shi mazaunin ƙauyen Shattu Anguba da ke Bosso a Jamhuriyar Nijar ne, kuma yana sana’ar kiwon raƙuma a yankin da ke ƙetaren Kogin Komadougou.

Bayan kammala binciken, Operation Haɗin Kai ta bayyana cewa ta wanke mutumin daga duk wani zargi na alaƙa da ’yan ta’adda.

Rundunar ta jaddada cewa duk mutanen da ake k**awa bisa zargi a lokacin ayyukan soja ana bi da su ne bisa tanadin doka da kuma tsauraran matakan tantancewa domin bambance fararen hula marasa laifi da ’yan ta’adda.

Ta kuma sake tabbatar da aniyar ta ta ci gaba da hana ’yan ta’adda samun damar gudanar da ayyukan su, tare da kiyaye ƙa’idojin ƙwarewar aiki, mutunta haƙƙin ɗan'adam da bin doka.

2027: Shugabannin Arewa maso Gabas sun Jaddada Goyon Baya Ga Shugaba TinubuShugabannin yankin Arewa maso Gabas sun bayya...
24/07/2026

2027: Shugabannin Arewa maso Gabas sun Jaddada Goyon Baya Ga Shugaba Tinubu

Shugabannin yankin Arewa maso Gabas sun bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Tinubu domin ya sake tsayawa takara a zaben 2027, tare da alkawarin tattara kuri’un yankin ga jam’iyyar APC.

Gwamnoni, ministoci, ’yan majalisa, sarakuna da dattawan jihohin Borno, Adamawa, Bauchi, Gombe, Taraba da Yobe ne s**a kai wa Tinubu ziyarar godiya a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja. Ziyarar ta biyo bayan matakin Tinubu na sake zaben Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, a matsayin abokin takararsa.

Gwamnan Borno kuma shugaban kungiyar gwamnonin Arewa maso Gabas, Farfesa Babagana Zulum, ya ce matakin ya nuna yadda shugaban kasa ke daraja biyayya, kwarewa da sadaukarwa. Ya ce ci gaba da barin Shettima a matsayin mataimakin shugaban kasa ya kara wa yankin kwarin gwiwa.

Zulum ya yaba wa gwamnatin Tinubu kan ayyukan hanyoyi, noma, ilimi, tallafa wa matasa da kuma kula da ’yan gudun hijira a yankin. Ya tabbatar wa shugaban kasa cewa shugabanni da magoya bayan APC a Arewa maso Gabas za su hada kai domin tabbatar da nasarar Tinubu da sauran ’yan takarar jam’iyyar a 2027.

Da yake mayar da martani, Tinubu ya ce goyon bayan da yankin ya nuna abin faranta rai ne, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da inganta tattalin arziki, tsaro da hanyoyin mota. Ya ce hadin gwiwar gwamnatin tarayya da jihohi na da muhimmanci wajen yaki da ta’addanci da fashi da makami, tare da tabbatar da zaman lafiya da walwalar ’yan Najeriya.

21/07/2026

tana nuna takaici ta alokacin corona.

Gwamnatin Tinubu ba ta ci bashin tiriliyan ₦80 k**ar yadda ake yaɗawa ba –Ministan KuɗiDaga Aliyu SambaA kwanakin nan an...
21/07/2026

Gwamnatin Tinubu ba ta ci bashin tiriliyan ₦80 k**ar yadda ake yaɗawa ba –Ministan Kuɗi

Daga Aliyu Samba

A kwanakin nan ana yawan yaɗa cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta karɓi sabon bashi har tiriliyan ₦80 cikin shekaru uku. Sai dai Ministan Kuɗi kuma Ministan Tattalin Arziki na Ƙasa, Taiwo Oyedele, ya bayyana wa Kwamitin Majalisar Dattawa kan Kuɗi cewa wannan fahimta ba ta yi daidai da yadda ake ƙididdige bashin ƙasa ba.

A cewarsa, abin da mutane da dama suke yi shi ne kwatanta bashin da aka gada lokacin da gwamnati ta hau mulki da bashin da ake da shi yanzu, sannan su ɗauka cewa duk bambancin sabon bashi ne. Amma a zahiri, akwai wasu muhimman dalilai guda biyu da s**a sa adadin bashin ya ƙaru a takardu ba tare da hakan na nufin an karɓi sabon bashi irin yadda ake faɗa ba.

Na farko, bayan sauye-sauyen tattalin arziki da kuma faɗuwar darajar naira, dole aka sake ƙididdige bashin ƙasashen waje zuwa darajar naira. Tunda ana rubuta bashin Najeriya ne da naira, sauyin canjin kuɗi ya ƙara sama da tiriliyan ₦40 a kan adadin bashin da ake gani a takardu. Wannan ba sabon bashi ba ne, ƙimar bashin da ake bin Najeriya ce kawai ta canza saboda darajar naira ta sauya.

Na biyu, akwai bashin Ways and Means da gwamnatin baya ta ci daga Babban Bankin Najeriya (CBN), wanda Majalisar Dokoki ta amince a mayar da shi cikin bashin gwamnati na hukuma. Wannan mataki ya ƙara kusan tiriliyan ₦33 a cikin bayanan bashin ƙasa. Amma wannan ma ba sabon bashi ba ne, domin bashin ya riga ya wanzu tun kafin wannan gwamnati; an dai shigar da shi cikin kundin bashin gwamnati ne.

Ministan ya kuma yi bayanin cewa wani ɓangare mai yawa na bashin cikin gida da gwamnati ke karɓa yanzu na sake fasalin tsoffin basuss**a (refinancing) ne. Wato idan tsohon bashi ya kai lokacin biya, gwamnati kan karɓi wani bashi domin biyan tsohon. Wannan ba yana nufin an ƙara sabon nauyin bashi ba.

Saboda haka, gwamnatin tarayya ta ce ba gaskiya ba ne a ce ta karɓi sabon bashi har tiriliyan ₦80 cikin shekaru uku. A cewar gwamnati, babban abin da ya sa adadin bashin ya ƙaru a takardu shi ne sauyin darajar naira, shigar da tsohon bashin Ways and Means cikin bayanan hukuma, da kuma sake fasalin tsoffin basuss**a, ba wai saboda an ci sabon bashi daidai da adadin da ake yaɗawa ba.

Ministan ya ƙara da cewa duk bashin da gwamnatin Tinubu ke karɓa ana karkata shi ne zuwa manyan ayyukan ci gaban ƙasa da ababen more rayuwa, tare da tabbatar da cewa ana kula da dorewar bashin Najeriya domin kada ya zama nauyi ga tattalin arzikin ƙasa.

Address

Kano

Telephone

+2349028483925

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fasihiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fasihiya:

Shortcuts

Share