29/05/2026
NAHCON Ta Yi Alƙawarin Mayar wa Alhazai Kuɗin Abincinsu Da Ya Lalace tare da ladabtar da masu laifi a Mina
Daga Aliyu Samba
Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta ce za ta tabbatar an mayar wa alhazan Najeriya da s**a fuskanci matsalar rashin ingantaccen abinci da walwala a Mina kudinsu, tare da hukunta duk wadanda aka samu da laifi.
Shugaban hukumar, Ambasada Ismail Abba Yusuf, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai bayan ya kai ziyara sansanonin alhazan Najeriya da ke Mina a yayin aikin Hajjin 2026.
Ya ce hukumar ta riga ta kai koken matsalar ga hukumomin Saudiyya kan yadda wasu kamfanonin abinci s**a gaza samar da ingantaccen abinci ga alhazai.
“Yayin rangadin da na yi yanzu, na gano cewa wasu jihohi ba a ba su abinci yadda ya kamata ba jiya da kuma karin kumallo na yau.
“Tuni muka dauki mataki tare da tuntubar hukumomin Saudiyya, kuma za mu saka kamfanonin da abin ya shafa cikin wadanda zamu dena aiki da su,” in ji shi.
Ambasada Ismail ya bayyana cewa hukumar ta sa an mayar abincin da aka ga bai dace da ci ba, tare da kokarin tabbatar da an biya diyyar asarar da alhazan s**a yi.
“Za mu tabbatar an mayar da kudin abincin da ba a kawo ba ko kuma wanda bai dace ba ga alhazai.
“Idan an samu kudin kafin su bar Saudiyya, za a ba su kai tsaye. Idan kuma ba haka ba, za a mikawa sakatarorin jihohi,” inji shi.
Sai dai shugaban NAHCON ya ce ba abin mamaki ba ne idan wasu alhazai ba su gamsu da dandanon abincin ba, domin akwai bambancin al’adu da salon girki tsakanin kasashe.
“Mun ji koke-koken da ake yi game da abincin, amma idan mutum ya bar kasarsa zuwa wata kasa, dole ne ya saba da al’adun wajen da ya je,”
Ya kara da cewa hukumar na duba yiwuwar dauko masu girki daga Najeriya a aikin Hajjin shekara mai zuwa domin su rika girka abincin da ya dace da alhazan Najeriya.
“Nan gaba, in sha Allah, muna son kawo masu girki daga Najeriya domin su yi wa alhazai girki sannan su koma gida bayan aikin Hajji,” inji shi.
Dangane da koke-koken da s**a shafi cunkoso da wuraren kwana, shugaban hukumar ya ce sun fara gudanar da bincike tare da kirga yawan alhazai a sansanonin jihohi daban-daban.
“Mun fara bincike kuma ni kaina na shiga aikin kirga alhazai a jihohi. Akwai abubuwan da muka gano, kuma idan lokaci ya yi za mu bayyana sakamakon binciken tare da hukunta masu laifi,” in ji shi.
Shugaban NAHCON ya kuma bayyana wasu sauye-sauyen da hukumar ta kawo domin inganta aikin Hajji a Najeriya.
Ya ce yanzu suna amfani da fasaha wajen neman biza, samun masauki da kuma biyan kudade domin rage cin hanci da inganta gaskiya a tsarin gudanarwa.
“Muna kokarin kawar da masu shiga tsakani ta hanyar tuntubar hukumomin Saudiyya kai tsaye domin su ba mu sunayen kamfanoni masu inganci,”
A cewarsa, hakan zai taimaka wajen rage kudin Hajji ga ’yan Najeriya tare da bai wa mutane da dama damar sauke farali.
Ya kuma ce hukumar ta inganta harkokin lafiya ta hanyar rajistar asibitoci tare da samar da isassun likitoci, ma’aikatan jinya da magunguna domin kula da lafiyar alhazai.
Duk da kalubalen da ake fuskanta sakamakon taruwar jama’a masu yawa, shugaban hukumar ya ce NAHCON za ta ci gaba da bai wa jin dadin alhazai fifiko a dukkan ayyukanta.