09/04/2026
Rikicin Kujerar Mataimakin Gwamnan Kano Ya Ɗauki Sabon Salo Bayan Murabus ɗin Gwarzo
Murabus ɗin tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya haifar da sabbin lissafin siyasa a faɗin jihar, inda manyan ƴan siyasa s**a fara fafatawa domin maye gurbin kujerar. Wannan lamari ya jawo hankalin masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar Kano, musamman ganin muhimmancin mukamin wajen tafiyar da gwamnati.
Rahotanni na nuni da cewa, Jibril Isma’il Falgore da Murtala Sule Garo su ne manyan ƴan takarar da ke kan gaba a fafatawar neman kujerar. Dukansu na da ƙarfi a siyasa da kuma goyon bayan magoya baya a fannoni daban-daban, lamarin da ke ƙara zafafa fafatawar cikin gida.
Masu sharhi na ganin cewa zaɓin wanda zai gaji kujerar zai iya tasiri sosai ga makomar siyasar Kano, musamman duba da yadda ake tunkarar zaɓuka masu zuwa. Ana sa ran shugabannin jam’iyya da masu ruwa da tsaki za su taka muhimmiyar rawa wajen yanke hukuncin wanda zai karɓi ragamar wannan muhimmin matsayi.