29/05/2026
As Salam
Siyasar Nigeria Cike Take Da Yaudara Da Munafunci Da Fadan Gangan.
Wasu Duk Abu daya suke wa Aiki APC Ce Suna Nan Dayawa.
Fatana Kada Talaka Yayi Fada Da Dan'uwan sa Talaka A Zabe Mai Zuwa Ka Zabi Wanda Ka ga Har Ga Allah Mutumin Kirki Ne Imma Mutanen Kirkin Zasu yi wuya to Masu Dama Dama .
Nidai Ko wani zaizo yace Zanyi Asarar Kuria Ta Dan Na Zabe wane in Naga shi Yafi dama dama Zan zabe shi don kar inje wajen Allah in Tashi a matsayin na Taimakawa Azzalumi.
Akwai Jamiyyun Boge Dayawa Duk APC Ne.
Ya Allah duk Wanda Ya Yaudari Alumma Allah Ka tozar shi duniya da lahira.
Ya Allah Duk Wanda Cinsa Allhairi ne a Garemu da Musulunchi da Arewa sannan Nigeria Allah ka bashi Kowanne Mataki Na Zaben Nan Biyar.
Ko A APC Yake da Tarkacen Ta Kamar NDC ko PRP Ko PDP Ta Wike Da Sauransu.
Ko ADC Yake Ko SDP da Sauransu.
Dr Abdulmuddalib Ahmad Gidado 29/5/26