Kalam Station KS

Kalam Station KS a radio online station that brings you genuine reports nonstop

Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya samu lambar girmamawa ta Justic...
10/10/2025

Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya samu lambar girmamawa ta Justice of Peace (JP) daga ƙungiyar May Peace Prevail On Earth International, wacce ke da alaƙa da Sashen yada Labarai na Majalisar Dinkin Duniya (UN Department of Public Information).

Wannan karramawa ta biyo bayan gudunmawar da Shugaban Hukumar yake bayarwa wajen bunƙasa zaman lafiya a duniya.

"Labarina — a powerful tale of struggle and survival. AGY speaks his truth, echoing the pain of the unheard while callin...
21/03/2025

"Labarina — a powerful tale of struggle and survival. AGY speaks his truth, echoing the pain of the unheard while calling leaders to serve justice and remember the people's plight. Produced by Unchained Vibes Africa. "

Stream and share!!!

Stream Labarina song from AGY. Producer: Unchained Vibes Africa. Release Date: March 21, 2025.

Mai Martaba Sarki Malam Muhammadu Sunusi Lamido Sunusi Ya Shiga Fadarsa Inda Ya Sami Rakiyar Gwamnan Jahar Kano Da Matai...
25/05/2024

Mai Martaba Sarki Malam Muhammadu Sunusi Lamido Sunusi Ya Shiga Fadarsa Inda Ya Sami Rakiyar Gwamnan Jahar Kano Da Mataimakinsa.

MUHIMMIN BAYANI AKAN AVACOINWasu mutanen sun ɗauka cewar da zarar kayi register na AVACOIN shikenan zaka jira lokaci yay...
08/03/2024

MUHIMMIN BAYANI AKAN AVACOIN

Wasu mutanen sun ɗauka cewar da zarar kayi register na AVACOIN shikenan zaka jira lokaci yayi ka cire ƴan Dalolinka ne kawai, to abun ba haka yake ba, dole sai kana yin wannan aiki a kullum:-
1) A jikin hoton dake ƙasa zaku ga inda nayi alamar wata Kifiya tayi nuni zuwa ga wasu Lambobi, waɗannan lambobi sune adadin Gold Dust da ake baka kullum, sun kai guda 7,500.

Ana so kayi ta danna Maballin Gold 🪙 har sai kaga waɗannan Lambobi sun kare, Ƙarewar su shine yake tabbatar da cewar ka gama haƙar Gold Dust dinka na wannan rana. Sai kuma ka jira gobe domin sake maimaita hakan.

2) Idan har a kowacce rana zaka ƙarar da waɗannan Gold Dust guda 7,500, to ko shakka babu zaka samu Dala 67 wanda yayi daidai da Naira 100,000 a cikin wata biyu Kacal.

3) Ga waɗanda suke da mutanen da s**ayi Register a ƙarƙashin su (Referral) zasu iya samun Dala 67 a ƙasa da watanni biyu.

4) Wanda baiyi Register ba, ga Link

Sabbin nadin muk**ai guda biyar da sabon gwamnan Kano yayiSabon gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nada Dakta A...
29/05/2023

Sabbin nadin muk**ai guda biyar da sabon gwamnan Kano yayi

Sabon gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya nada Dakta Abdullahi Baffa Bichi a matsayin sakataren gwamnatin jihar Kano, da kuma Shehu Sagagi a matsayin shugaban ma'aikatan fadar gwamnati, sai kuma Dakta Farouk Kurawa a matsayin babban sakatarensa.

Ragowar sun hada da, Abdullahi Ibrahim Rogo, a matsayin shugaban tsare-tsare (Chief Protocol), da kuma Sanusi Bature Dawakin Tofa a matsayin sakataren yada labarai na gwamna.

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta K**a Wanda ya yaɗa kalaman ɓatanci akan Jarumin Kannywood.Rundunar Yan sandan Jihar Ka...
09/11/2022

Rundunar Yan Sandan Jihar Kano ta K**a Wanda ya yaɗa kalaman ɓatanci akan Jarumin Kannywood.

Rundunar Yan sandan Jihar Kano ta Samu Nasarar k**a wani matashi mai Suna Imam Abdullahi indabawa mai Kimanin shekaru 30 a duniya bisa zargin yaɗa kalaman bata suna tare da neman wasu kuɗaɗe daga Abdulaziz Sha'aibu Wanda aka fi sani da Malam Ali na cikin Shirin kwana casa'in tare da yi masa barazanar cigaba da bata masa suna idan bai biya shi wasu kudade ba.

Hakan na kunshe cikin wata tattaunawa da Kakakin rundunar yan sanda ta jihar Kano SP Abdullahi Haruna Kiyawa yayi da wanda ake zargi da mai ƙara a yammacin talatar data gabata, a shedikawatar yan sanda dake Bompai a Kano.

Matashin da ake zargi ya amsa laifin sa a gaban lawyan sa, inda ya nemi da ayi masa afuwa bisa abubuwan da ya aikata na kuskure. Ya kuma bayyana cewa shi mai wa'azi ne da ya samu zamiya yayin wa'azin sa, har ta kai shi ga wallafa rubutun da ya taba mutunci da ƙima ta Jarumin Kannywood Abdulaziz Sha'aibu.

A nasa bangaren, Jarumi Abdulaziz Sha'aibu ya koka matuka da yanda a cewar sa matashin ya cutar da shi da rubutun da ya wallafa, inda ya kara da cewa, Indabawa ya nemi ya bashi kudi don ya dakatar da yaɗuwar wannan rubutu na cin mutunci da take masa, tare da yi masa barazanar cigaba da yada wasu rubuce-rubucen a wasu kafafen muddin bai bashi kudi ba.

Tuni dai rundunar yan sanda sun kammala bincike kuma zasu mika wanda ake tuhuma zuwa kotu.

Jarida Radio
9/11/22

YANZU-YANZU: ASUU ta janye dakatar da yajin aiki Kungiyar Malaman Jami’o'i ta Ƙasa,  ASUU ta janye yajin aikin da ta sha...
14/10/2022

YANZU-YANZU: ASUU ta janye dakatar da yajin aiki

Kungiyar Malaman Jami’o'i ta Ƙasa, ASUU ta janye yajin aikin da ta shafe watanni takwas ta na yi.

Kungiyar ta yanke shawarar janye yajin aikin ne a babban taron Kwamitin Zartaswarta da ya gudana a Abuja a jiya Alhamis.

A safiyar yau Juma’a ne dai wani babban jami’in na ASUU da ya halarci taron ya shaida wa Daily Trust cewa, “Gaskiya ne, mun janye yajin aikin… Nan gaba kaɗan da safiyar nan Shugaban ASUU na Kasa zai fitar da sanarwar a hukumance.”

Wata takwas cif ke nan da malaman jami’o’in gwamnati su ka shafe su na yajin aikin da kungiyar ta kira tun ranar 14 ga ga watan Fabrairu, 2022.

A cigaba da sauraren shari'ar da akeyi tsakanin sheikh  Abduljabar Nasir kabara da Gwamnatin kano, Malam Abduljabar ya n...
11/08/2022

A cigaba da sauraren shari'ar da akeyi tsakanin sheikh Abduljabar Nasir kabara da Gwamnatin kano, Malam Abduljabar ya nemi kotu da ta bashi dama yayi s**a kan tuhume tuhumen da akeyi masa.

Sai dai kotu ta tafi hutun mintuna 15 domin tayi nazari kafin tai kwaraya kwaryar hukunci kan hakan.

Bayan dawowa kotun ta ce Malam Abduljabbar din Yana da damar yin s**a kan wannan roko da yayi.

Kotu a Kano ta yankewa malamin nan Abdulmalik Tanko hukuncin kisa da zaman gidan yari na Shekara 5 sak**akon k**a shi da...
28/07/2022

Kotu a Kano ta yankewa malamin nan Abdulmalik Tanko hukuncin kisa da zaman gidan yari na Shekara 5 sak**akon k**a shi da laifin kashe dalibarsa Hanifa Abubakar.

Ya kuka kalli hukuncin?👇
https://bit.ly/3S7BKeE

Dr. Mustapha Umar Imam, Daya neDaga Cikin Fasinjojin Da Aka Sace A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja. Shi Ne: Dokta M...
24/07/2022

Dr. Mustapha Umar Imam, Daya ne
Daga Cikin Fasinjojin Da Aka Sace A Harin Jirgin Kasan Kaduna Zuwa Abuja.

Shi Ne:

Dokta Mustapha Umar Imam, Mataimakin farfesa ne a kasar China, amma ya dawo Najeriya bisa bukatar koyarwa a Asibitin UDUS dake Sokoto. Ya kasance shugaban farko wadanda s**a fara koyarwa akan yadda za,a kare kai daga kamuwa da cutar Covid-19, lokacin da cutar ta fara.

Mu sanya shi da sauran fasinjojin cikin addu'a don Allah, Allah ya kubutar mana dasu Ameen.

Daga- Muhammad Dahiru Shugaba

© Vanguard Hausa

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kalam Station KS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kalam Station KS:

Share