View Point Hausa

  • Home
  • View Point Hausa

View Point Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from View Point Hausa, Media, .

View Point Hausa dandalin labarai ne mai zaman kansa da ke bayar da sahihan bayanai, bincike mai zurfi da nazari kan al’amuran da s**a shafi Arewacin Najeriya da duniya baki ɗaya.

Barkanku da SallahAllah Ya Maimaita Mana
27/05/2026

Barkanku da Sallah
Allah Ya Maimaita Mana

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UNRahotanni daga Bayero University Kano sun tabbatar da rasuwar Dr. Musa Adamu Labaran, ...
25/05/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI’UN

Rahotanni daga Bayero University Kano sun tabbatar da rasuwar Dr. Musa Adamu Labaran, mataimakin Dean na Faculty of Communication kuma malami a Sashen Mass Communication na jami’ar, wanda ya rasu a safiyar yau Litinin bayan gajeruwar rashin lafiya. 

Marigayi Dr. Musa Adamu Labaran fitaccen malami ne kuma masani a fannin sadarwa da harkokin yada labarai a Bayero University Kano. Ya kasance daya daga cikin manyan malaman Faculty of Communication, inda ya bayar da gudunmawa sosai wajen koyarwa, jagoranci da ci gaban dalibai.

An san shi da kwarewa da jajircewa wajen gudanar da ayyukan jami’a. Ya taba rike mukamin Assistant Exams Officer a Faculty of Communication, sannan daga baya aka nada shi Mataimakin Dean (Deputy Dean) na Faculty din bayan sake zaben Farfesa Umar Faruk Jibril a shekarar 2024. 

Dr. Musa Adamu Labaran ya samu digirorinsa na B.Sc, M.Sc da PhD daga Bayero University Kano, abin da ya nuna cikakkiyar alaka da jami’ar tun daga matakin karatu har zuwa koyarwa da shugabanci. Ya kasance cikin malaman da s**a sadaukar da rayuwarsu wajen bunkasa ilimi da tarbiyyar dalibai. 

A tsawon shekarun aikinsa, ya taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa Sashen Mass Communication tare da bayar da gudunmawa a harkokin gudanarwa da shirye-shiryen Faculty of Communication. Abokan aiki da dalibansa sun bayyana shi a matsayin mutum mai mutunci, tawali’u da son taimakon al’umma.

Rasuwarsa ta girgiza iyalai, abokan aiki, dalibai da daukacin al’ummar jami’ar BUK, musamman Faculty of Communication inda ya yi fice wajen koyarwa da jagoranci. Sakonnin ta’aziyya na ci gaba da fitowa daga malamai, dalibai da abokan arziki suna addu’ar Allah Ya jikansa da rahama.

Muna rokon Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa, Ya baiwa iyalansa, abokan aikinsa da daukacin al’ummar Bayero University Kano hakurin jure wannan babban rashi.
View Point Hausa

Wanene Zabin Ku?
23/05/2026

Wanene Zabin Ku?

21/05/2026

HANYOYI UKU DA ZA’ABI ABI A DAKILE FADAN DABA A JIHAR KANO.
SHEIKH IBRAHIM KHALIL
VIEW POINT HAUSA

Shugabannin Arewa Su Tashi Tsaye Domin Ceto Yankin — Janar Ibrahim Badamasi BabangidaTsohon Shugaban Ƙasa, Janar Ibrahim...
21/05/2026

Shugabannin Arewa Su Tashi Tsaye Domin Ceto Yankin — Janar Ibrahim Badamasi Babangida

Tsohon Shugaban Ƙasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya yi kira ga shugabannin Arewa da su tashi tsaye domin ceto yankin daga mawuyacin halin da yake ciki, yana mai bayyana damuwarsa kan matsalolin tsaro, talauci da rashin ci gaba da s**a addabi yankin.

Janar Babangida ya bayyana hakan ne yayin da yake nuna damuwa kan yadda Arewa ke cigaba da fuskantar ƙalubale iri-iri da s**a haɗa da rashin tsaro, rashin aikin yi da kuma koma bayan ilimi da tattalin arziki.

A cewarsa, lokaci ya yi da shugabanni da masu ruwa da tsaki za su haɗa kai domin nemo hanyoyin da za su fitar da yankin daga halin da yake ciki kafin lamarin ya ƙara taɓarɓarewa.

“Shugabannin Arewa kuyi ƙoƙarin fidda yankin Arewa daga mawuyacin halin da yake ciki. Mu tamu ta kare. Ina ji a jikina kamar bazan tsallake wannan shekarar ba,” inji Janar Babangida.

Tsohon shugaban ƙasar ya jaddada cewa makomar Arewa tana hannun shugabanninta da matasa, yana mai kira ga al’umma da su rungumi haɗin kai, zaman lafiya da kuma jajircewa wajen cigaban yankin.

Kalaman nasa na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da tattaunawa kan hanyoyin da za a magance matsalolin da s**a dabaibaye yankin Arewa da ma ƙasar baki ɗaya.

View Point Hausa

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso: Samun Takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa Babbar Nasara Ce ga Jihar KanoJagoran Jam’iyyar NDC ...
19/05/2026

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso: Samun Takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa Babbar Nasara Ce ga Jihar Kano

Jagoran Jam’iyyar NDC a Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa samun takarar Mataimakin Shugaban Ƙasa wata babbar nasara ce ga al’ummar Jihar Kano da ma Arewa baki ɗaya.

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne yayin da yake magana kan muhimmancin bai wa Kano damar taka muhimmiyar rawa a siyasar ƙasa, inda ya ce wannan ci gaba alama ce ta yadda jihar ke ƙara samun karɓuwa da tasiri a harkokin siyasar Najeriya.

Ya ƙara da cewa wannan dama da aka samu na iya zama wata kafa da za ta buɗe ƙofofi ga Kano domin samun cikakkiyar takarar Shugaban Ƙasa a nan gaba, idan aka ci gaba da haɗin kai da kyakkyawan shugabanci.

A cewarsa, Kano jiha ce mai yawan al’umma, tarihi da kuma ƙarfin siyasa, don haka tana da dukkanin cancantar da za ta iya kai ta ga jagorancin ƙasa a lokaci mai zuwa.

Sanata Kwankwaso ya kuma yi kira ga matasa da sauran al’ummar jihar da su ci gaba da bada goyon baya ga manufofin da za su kawo ci gaba, haɗin kai da cigaban dimokuraɗiyya.

Ya jaddada cewa siyasa ba ta ƙare da neman mukami kawai ba, illa tana buƙatar jajircewa, haɗin kai da sadaukarwa domin tabbatar da muradun al’umma.

DA DUMI-DUMI:Abba Kabir Yusuf ya amince da bai wa kowane maniyyacin aikin Hajjin bana daga Kano State tallafin Riyal 200...
11/05/2026

DA DUMI-DUMI:
Abba Kabir Yusuf ya amince da bai wa kowane maniyyacin aikin Hajjin bana daga Kano State tallafin Riyal 200 domin rage musu nauyin kashe-kashen da ake fuskanta yayin gudanar da aikin Hajji.

Wannan mataki na daga cikin kokarin gwamnatin jihar wajen tallafawa maniyyata da saukaka musu harkokin tafiya da gudanar da ibadarsu cikin kwanciyar hankali.

Abubakar Idris Dadiyata wanda aka fi sani da “Dadiyata” matashi ne ɗan gwagwarmayar siyasa kuma mai fafutukar bayyana ra...
10/05/2026

Abubakar Idris Dadiyata
wanda aka fi sani da “Dadiyata” matashi ne ɗan gwagwarmayar siyasa kuma mai fafutukar bayyana ra’ayinsa a kafafen sada zumunta. Ya yi suna musamman wajen s**ar gwamnati da kuma bayyana matsalolin al’umma ta hanyar rubuce-rubuce da bidiyoyi a shafukan sada zumunta.

A ranar 2 ga watan Agustan shekarar 2019 ne aka ruwaito cewa wasu mutane da ba a san ko su waye ba sun ɗauke shi daga gidansa da ke Barnawa a jihar Kaduna. Rahotanni sun bayyana cewa mutanen sun zo ne cikin dare sannan s**a tafi da shi ba tare da bayyana kansu ba. Tun daga wannan lokaci babu cikakken bayani game da inda yake ko halin da yake ciki.

Lamarin ɓacewar Dadiyata ya tayar da kura sosai a Najeriya, inda mutane da dama s**a riƙa kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su binciko abin da ya faru da shi. Kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam, ‘yan jarida da masu fafutuka sun yi ta yaɗa taken neman a bayyana gaskiya game da halin da yake ciki.

Shekaru da s**a biyo baya, an riƙa samun jita-jita daban-daban game da Dadiyata, amma babu wata hukuma da ta tabbatar da gaskiyar waɗannan bayanai. Har yanzu iyalansa da masoyansa suna cigaba da neman a fito da sahihin bayani kan inda yake da abin da ya same shi.

Tsararren Labari

Wanene Dadiyata?

Abubakar Idris wanda aka fi sani da Dadiyata, matashi ne ɗan Najeriya da ya yi fice wajen amfani da kafafen sada zumunta domin bayyana ra’ayinsa kan harkokin siyasa da rayuwar al’umma. Ya kasance mutum mai kaifin magana wanda ke s**ar shugabanni da bayyana damuwar talakawa.

Yadda Aka Ɗauke Shi

A shekarar 2019 ne aka wayi gari da labarin cewa wasu mutane sun shiga gidansa da ke Kaduna cikin dare s**a tafi da shi. Tun daga wannan rana ba a sake ganin sa ba, lamarin da ya jefa iyalansa da abokansa cikin damuwa.

Martanin Jama’a

Bayan ɓacewar sa, mutane da dama sun nuna damuwa tare da neman gwamnati ta bayyana gaskiya. Masu fafutuka da kungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam sun yi ta kira da a gudanar da bincike mai zurfi.

Har Yanzu Ana Neman Gaskiya

Duk da shekaru da s**a wuce, har yanzu babu tabbacin abin da ya faru da Dadiyata. Lamarin ya ci gaba da zama ɗaya daga cikin manyan batutuwan da ke tayar da hankali a Najeriya, musamman wajen tattauna batun ‘yancin faɗin albarkacin baki da tsaron masu ra’ayi daban-daban

Sai dai a Makon da yagaba Rahotanni suna ta Zagayawa a Kafafan sada Zumunta kan Zargin Wani Jami’in Dan Sanda da Kashe Dadiya
In Babban Sufeton Yan’sandan Nigeria Ya Bada Umarni ga Rundunar Yan’Sanda Su Gudanar da Bincike a Kan Zargin

View Point Hausa.

Bayyanar Wanda Ake Zargi da Kashe Dadiyata Ya Jawo Cece-KuceAn shiga cikin yanayi na cece-kuce da muhawara bayan bayyana...
09/05/2026

Bayyanar Wanda Ake Zargi da Kashe Dadiyata Ya Jawo Cece-Kuce

An shiga cikin yanayi na cece-kuce da muhawara bayan bayyanar wani mutum da ake zargi da hannu a batun batan tare da kashe Dadiyata, lamarin da ya dade yana jan hankalin al’umma musamman a shafukan sada zumunta da kafafen yada labarai.

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon Hadimin Tsohon Gwamnan Jihar Zamfara kuma Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana wasu bayanai masu tayar da hankali dangane da yadda aka gudanar da lamarin. A cewarsa, akwai zarge-zargen cewa wani jami’in dan sanda na da hannu a cikin mutuwar Dadiyata.

Wannan bayani ya sake tayar da hankalin jama’a, inda mutane da dama ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar abin da ya faru tare da tabbatar da adalci.

Tun bayan bacewar Dadiyata, mutane da dama sun rika bayyana damuwa tare da neman hukumomi su fito da sahihan bayanai game da halin da ake ciki. Batun ya dade yana daga cikin manyan muhawarorin siyasa da kare hakkin bil’adama a Najeriya.

Masu sharhi kan harkokin siyasa sun bayyana cewa sabon zargin da aka fitar na iya kara matsa lamba ga hukumomin tsaro domin su sake duba wannan al’amari da zurfi.

Al’umma dai na ci gaba da jiran sahihan bayanai daga hukumomi kan gaskiyar lamarin, yayin da ake kira da a tabbatar da adalci ga kowa ba tare da nuna son kai ba
Jaridar View Point Hausa Tayi Kokarin Ji daga Hukumomin da Lamarin Ya Shafa Amma Har Izuwa Yanzu bamuji daga Garesu ba

View Point Hausa.

LABARI DA DUMI-DUMIAn samu wani sabon bayani mai tayar da hankali daga bakin wani tsohon SSA na tsohon Gwamnan Jihar Zam...
08/05/2026

LABARI DA DUMI-DUMI

An samu wani sabon bayani mai tayar da hankali daga bakin wani tsohon SSA na tsohon Gwamnan Jihar Zamfa Bello Matawalle, inda ya bayyana yadda ake zargin wani jami’in dan sanda da hannu a kisan Dadiyata.

Rahotanni sun bayyana cewa tsohon hadimin ya yi wannan bayani ne yayin wata tattaunawa, inda ya ce akwai bayanai da suke nuna yadda lamarin ya faru da kuma mutanen da ake zargi da hannu a ciki. Wannan batu ya sake jawo ce-ce-ku-ce da martani daga jama’a musamman a kafafen sada zumunta, yayin da mutane ke kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin gano gaskiyar lamarin.

Al’umma da dama sun bayyana damuwarsu kan yadda batun bacewar Dadiyata ya dade yana jan hankali ba tare da samun cikakken bayani daga hukumomi ba. Wasu kuma na ganin wannan sabon zargi zai iya bude wata kafa ta sake bincike domin gano hakikanin abin da ya faru.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan wannan sabon zargi ba.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when View Point Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share