Hausawa Global

Hausawa Global Kafa ce da za ta ringa kawo muku labaran halin da ake ciki a Najeriya dama sassan duniya cikin harshen Hausa.

Za ma ku iya tura mana labarai da hotunan halin da ake ciki a yankunanku mu wallafa ta lambar whatsapp 08022624347

Gwamnatin Donald Trump tana neman amincewar majalisar dokokin Amurka domin sayar da mak**ai ga Isra’ila da darajarsu ta ...
19/09/2025

Gwamnatin Donald Trump tana neman amincewar majalisar dokokin Amurka domin sayar da mak**ai ga Isra’ila da darajarsu ta kai kusan dala biliyan shida, in ji jaridar Wall Street Journal ranar Juma’a.

Rahoton ya ce shirin ya haɗa da yarjejeniyar sayar da jiragen yaki na Apache guda 30 kan dala biliyan 3.8, da kuma motoci masu sulke na sojojin ƙasa guda 3,250 kan dala biliyan 1.9.

Jaridar ta ce ta samu wannan bayani ne daga wasu takardu da ta duba, tare da bayanan daga mutanen da ke da masaniya kan lamarin.

Inter Miami na gab da kammala sabuwar yarjejeniya da Lionel Messi mai shekara 38, wanda ya fara taka leda a kulob din na...
19/09/2025

Inter Miami na gab da kammala sabuwar yarjejeniya da Lionel Messi mai shekara 38, wanda ya fara taka leda a kulob din na MLS a shekarar 2023. Sabon kwantiragin zai kasance na dogon lokaci domin ci gaba da riƙe gwarzon dan wasan gaban Argentina.

Majalisar Dinkin Duniya ta kada kuri’a a ranar Juma’a domin bai wa shugaban Falasɗinu Mahmoud Abbas damar yin jawabi ga ...
19/09/2025

Majalisar Dinkin Duniya ta kada kuri’a a ranar Juma’a domin bai wa shugaban Falasɗinu Mahmoud Abbas damar yin jawabi ga taron shekara-shekara na shugabannin duniya mako mai zuwa ta hanyar bidiyo, bayan da Amurka ta ƙi ba shi visa zuwa New York.

Wannan kudiri ya kuma amince da bai wa Abbas da sauran manyan jami’an Falasɗinu damar shiga tarurrukan MDD da tarukan kasa da kasa ta bidiyo a cikin shekara guda, idan aka hana su tafiya Amurka.

Haka kuma, Abbas zai sami damar yin jawabi ta bidiyo a wani babban taro da za a gudanar a Majalisar Dinkin Duniya ranar Litinin karkashin jagorancin Saudiyya da Faransa, wanda manufarsa ita ce neman goyon baya ga mafita ta ƙasar biyu, inda ake sa ran wasu ƙasashe za su ayyana amincewa da ƙasar Falasɗinu.

Ƙungiyar Al-Nassr ta Saudiyya na neman dan wasan tsakiyar Manchester United, Casemiro, wanda kwantiraginsa zai kare a ba...
19/09/2025

Ƙungiyar Al-Nassr ta Saudiyya na neman dan wasan tsakiyar Manchester United, Casemiro, wanda kwantiraginsa zai kare a bazara. Dan wasan Brazil mai shekara 33 na iya zama sabon ɗan wasa a Saudi Pro League idan aka cimma yarjejeniya.

Gwamnatin jihar Sokoto ta dakatar da shugabannin makarantu shida bisa zargin karɓar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba da kuma sab...
19/09/2025

Gwamnatin jihar Sokoto ta dakatar da shugabannin makarantu shida bisa zargin karɓar kuɗaɗe ba bisa ƙa’ida ba da kuma saba wa dokoki. Kwamishinan Ilimi, Ahmad Ila, ya bayyana cewa gwamnati ba za ta lamunci rashin bin doka da cin zarafin dalibai da iyayensu ba.

Makarantun da abin ya shafa sun haɗa da Nana Girls Secondary School, GDSS Gagi, GDSS Mana, Giginya Memorial College, Mana Basic Secondary School, da GDSS Silame. An kafa kwamitin bincike karkashin Farfesa Mustapha Tukur domin gano gaskiyar lamarin, yayin da shugabannin da aka dakatar s**a mika ragamar aiki ga mataimakansu.

Kungiyar Benfica ta tabbatar da naɗa Jose Mourinho a matsayin sabon kociyanta kan kwantiragin da zai kai har zuwa ƙarshe...
19/09/2025

Kungiyar Benfica ta tabbatar da naɗa Jose Mourinho a matsayin sabon kociyanta kan kwantiragin da zai kai har zuwa ƙarshen kakar 2027. Mourinho, mai shekara 62, ya gaji Bruno Lage wanda aka sallama bayan rashin nasara da Qarabag a gasar Champions League.

Tsohon kociyan Chelsea ya koma horar da tamaula cikin gajeren lokaci, bayan rabuwa da Fenerbahce, inda Benfica ta hana ƙungiyar ta Turkiya samun gurbi a gasar zakarun Turai.

Mourinho ya fara aikin kociya a Benfica tun 2000, amma ya bar ƙungiyar bayan jagorantar wasanni 10 saboda rashin jituwa tsakaninsa da shugabannin kulob ɗin.

Brands Biya, ‘yar shugaban Kamaru Paul Biya, ta tayar da hankula bayan ta wallafa bidiyo a TikTok tana kira ga ‘yan kasa...
18/09/2025

Brands Biya, ‘yar shugaban Kamaru Paul Biya, ta tayar da hankula bayan ta wallafa bidiyo a TikTok tana kira ga ‘yan kasar da kada su kada wa mahaifinta kuri’a a zaben shugaban kasa da za a gudanar ranar 12 ga Oktoba, 2025.

A cikin sakonta, ta ce Kamaru na fuskantar mummunan yanayi na siyasa da tattalin arziki, don haka lokaci ya yi da za a ba dan takarar adawa dama domin kawo sauyi da cigaba.

Wannan furuci daga ‘yar shugaban ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda jama’a ke bayyana mamaki da kuma tattaunawa kan wannan matsayi da ta dauka.

‘Yan bindiga da ke tafiya a kan babura sun kai mummunan hari a ƙauyen Takoubatt, jihar Tillaberi da ke yammacin Nijar, i...
17/09/2025

‘Yan bindiga da ke tafiya a kan babura sun kai mummunan hari a ƙauyen Takoubatt, jihar Tillaberi da ke yammacin Nijar, inda s**a harbe aƙalla mutane 22 yayin da suke halartar bikin baftisma. Rahotanni sun ce maharan sun fara kashe mutum 15 a wajen bikin kafin daga bisani su kashe wasu bakwai a cikin ƙauyen.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da faruwar lamarin ga kamfanin dillancin labaran AFP, yayin da kafafen watsa labarai a ƙasar s**a bayyana cewa wannan hari ya jefa al’umma cikin tashin hankali da alhini. Mai fafutukar kare haƙƙin ɗan adam, Maikoul Zodi, ya ce lamarin ya sake nuna yadda jama’ar da ba su ji ba, ba su gani ba ke fuskantar mummunan tasiri na hare-haren ta’addanci a Tillaberi.

Rahotanni sun nuna cewa hukumomin soji ƙasar sun ƙara yawan dakarunsu a yankin don daƙile hare-haren ƙungiyoyin da ke da alaƙa da Al-Qaeda da ISIS. Sai dai duk da hakan, Human Rights Watch ta ce ƙungiyoyin sun kashe mutane 127 a hare-hare biyar tun watan Maris, yayin da ACLED ta ƙiyasta cewa sama da mutum 1,800 aka kashe a Nijar tun Oktoban 2024, mafi yawan su a Tillaberi.

Hukumomin Saudiyya sun saki wasu ƴan Najeriya uku da aka tsare a Jidda bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi. Wadanda aka ...
17/09/2025

Hukumomin Saudiyya sun saki wasu ƴan Najeriya uku da aka tsare a Jidda bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi. Wadanda aka saki su ne Maryam Hussain Abdullahi, Abdullahi Bahijja Aminu da Abdulhamid Saddieq, bayan bincike ya gano cewa ba su da hannu a lamarin.

Rahotanni sun ce wasu mutane da ke aiki a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano (MAKIA) ne ake zargi da manna sunayen mutanen a kan wasu akwatuna da ke ɗauke da miyagun ƙwayoyi. A cewar Hukumar NDLEA, mutanen ukun sun shiga jirgin Ethiopian Airline ET940 daga Kano zuwa Jidda a ranar 6 ga watan Agusta, 2025 domin yin Umara, inda daga bisani aka k**a su suna isa Jidda.

Bincike ya kai ga k**a wani mutum mai shekara 55, Mohammed Ali Abubakar da aka fi sani da Bello Karama, wanda ake zargi da jagorantar safarar tare da wasu mutum uku ciki har da ma’aikacin jirgin. Tuni an gurfanar da shi da sauran abokan harkallarsa Celestina Emmanuel Yayock, Abdulbasit Adamu Sagagi da Jazuli Kabir a gaban kotu bisa tuhume-tuhume da s**a shafi safarar miyagun ƙwayoyi.

Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga fargabar da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi cewa tsana...
16/09/2025

Fadar shugaban ƙasa ta mayar da martani ga fargabar da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya yi cewa tsananin yunwa da matsin rayuwa na iya jawo juyin-juya-hali a Najeriya. Fadar ta ce wannan magana tsohon tunani ne da bai dace da halin da ake ciki a yanzu ba.

A cewar fadar, kalaman Atiku na da nasaba da siyasa kawai, inda ta jaddada cewa manufofin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu sun fara haɓaka daidaiton tattalin arziki kuma suna ɗora ƙasar kan hanyar farfaɗowa.

Sai dai Atiku ya zargi gwamnati da ƙirƙiro manufofin da s**a jefa ƙasar cikin mawuyacin hali, inda ya ce sun ƙara tsananta hauhawar farashi, ƙarancin abinci, da matsalar rashin aikin yi da ke addabar talakawa.

Kwamitin binciken Majalisar Ɗinkin Duniya ya zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi kan Palasɗinawa tun bayan fara yaƙin...
16/09/2025

Kwamitin binciken Majalisar Ɗinkin Duniya ya zargi Isra’ila da aikata kisan kiyashi kan Palasɗinawa tun bayan fara yaƙin da ta kaddamar kan Hamas a shekarar 2023. Sabon rahoton ya ce an samu hujjojin da s**a tabbatar da aikata huɗu daga cikin abubuwa biyar da dokokin ƙasa da ƙasa ke ɗauka a matsayin kisan kiyashi.

Rahoton ya bayyana abubuwan da s**a haɗa da kashe rukuni na mutane, jikkata su matuƙa har da matsalolin tunani, ɗaukar matakai don lalata su da gangan, da kuma hana haihuwar al’umma. Hakanan ya kawo kalaman shugabannin Isra’ila da yadda ake tafiyar da dakarun tsaron ƙasar a matsayin hujjojin da ke nuna aniyar kisan kiyashi.

Sai dai a nasa ɓangaren, ma’aikatar harkokin wajen Isra’ila ta yi watsi da rahoton, tana mai cewa rahoton ba shi da tushe kuma ba shi da ingantacciyar hujja.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa sama da shekaru biyu da Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki,...
15/09/2025

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana cewa sama da shekaru biyu da Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki, babu wata alama da ke nuna zai iya magance matsalar yunwa da talauci da ke addabar ’yan Najeriya. Atiku ya ce yunwar da ake fama da ita a ƙasar abin kunya ne musamman ga talakawa da marasa galihu. Ya jaddada cewa mafi yawan juyin juya halin da aka gani a duniya ya samo asali ne daga yunwa da matsin rayuwa, musamman matsalar rayuwa ta kunci a cikin ƙasar da ke da albarkatu.

Atiku cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Paul Ibe, ya fitar a ranar Litinin, ya ce duk da cewa babban aikin kowace gwamnati shi ne tsaron rayuka da walwalar jama’a, al’ummar Najeriya a halin yanzu suna cikin mawuyacin hali na talauci da yunwa a karkashin gwamnatin Tinubu ta jam’iyyar APC. Ya kara da cewa wannan matsala tana haifar da ƙarin aikata laifuka irin su damfara, ta’addanci, garkuwa da mutane, ɗabi’un ’yan kungiyar asiri, shaye-shaye da maido da al’adu na sadaukar da rayuka.

Ya yi nuni da cewa wannan mummunan yanayi ya zama dama ta yin nazari, inda ya kawo misali da juyin juya halin Faransa, na Rasha a 1917 da kuma “Arab Spring” wanda ya fara daga Tunisia bayan wani matashi ya yi ƙona kansa saboda takaicin rayuwa, sannan ya bazu ya girgiza gabashin duniya. A cewarsa, a Najeriya ma za a iya cewa boren EndSARS ya samo asali daga takaicin yunwa da rashin kulawa daga gwamnati.

Atiku ya ce duk da ikirarin gwamnatin Tinubu na yin sauye-sauye, gaskiyar magana ita ce rashin wadatar abinci ya zama ruwan dare a ƙasar. Ya bayyana cewa kowace gwamnati mai mutunci sai ta fara da kare jama’arta da inganta walwalarsu. Ya jaddada cewa tun da gyare-gyare ana yi ne don al’umma, dole ne a yi su da tausayi da jinkai. A cewarsa, “Ko gwamnati ta yarda ko ta ƙi, gaskiyar rayuwarmu ita ce talakawa suna mutuwa da yunwa, yayin da sauran marasa ƙarfi ke rayuwa ne kawai a ƙarƙashin muguwar manufar wannan gwamnati.”

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausawa Global posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausawa Global:

Share