Hausawa Global

Hausawa Global Kafa ce da ke kawo muku sahihan labarai daga Najeriya da sassan duniya cikin harshen Hausa.
(2)

Kamfanin Dillancin Labaran Gwamnatin Jamhuriyar Nijar (ANP) ya ce wasu sojojin ƙasar sun mutu a wani hari da mayaƙan Bok...
01/08/2026

Kamfanin Dillancin Labaran Gwamnatin Jamhuriyar Nijar (ANP) ya ce wasu sojojin ƙasar sun mutu a wani hari da mayaƙan Boko Haram s**a kai a kusa da garin N'Guigmi da ke Jihar Diffa, a kudu maso gabashin ƙasar.

A cewar ANP, an kai harin ne a ranar Jumma'a a yankin da ke kusa da iyakar Najeriya, Kamaru da Chadi, inda ƙungiyar Boko Haram ke da sansanoni. Sai dai kamfanin bai bayyana adadin sojojin da s**a mutu ba, yana mai cewa gwamnan Jihar Diffa, Janar Mahamadou Ibrahim, ya halarci jana'izar waɗanda aka kashe.

Sai dai kamfanin dillancin labarai na AFP ya ambato wasu majiyoyi na cewa sojoji goma ne s**a rasa rayukansu a harin. Boko Haram ta fara tayar da ƙayar baya a arewacin Najeriya tun shekarar 2009, kuma daga baya hare-harenta s**a bazu zuwa Nijar, Kamaru da Chadi, lamarin da ya sa ƙasashen s**a kafa rundunar tsaro ta haɗin gwiwa domin yaƙar ƙungiyar.

Gwamnatin Jihar Kano ta fara raba takardun mallakar filaye ga fiye da mataimakan gwamna 2,500, ciki har da SSAs, SAs, SR...
01/08/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta fara raba takardun mallakar filaye ga fiye da mataimakan gwamna 2,500, ciki har da SSAs, SAs, SRs, SSRs, PAs da 'Yan Akwatu, a wani shiri da ta ce na ƙarfafa mallakar gidaje da rage ƙarancin matsuguni.

Kwamishinan Filaye da Tsare-tsaren Birane, Abduljabbar Muhammad Umar Garko, ya gargaɗi waɗanda s**a amfana da kada su sayar da filayen ko su bari masu ƙwacen filaye su ƙwace musu su. Ya ce gwamnati ta tsara sabbin unguwannin tare da muhimman ababen more rayuwa, yayin da take ci gaba da inganta tsarin gudanar da harkokin filaye ta hanyar fasahar dijital.

01/08/2026

Martanin Madugu

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun daƙile yunƙurin da mayaƙan Boko Haram/ISWAP s**a yi na yin garkuwa da mutum 31 ...
01/08/2026

Dakarun rundunar Operation Hadin Kai sun daƙile yunƙurin da mayaƙan Boko Haram/ISWAP s**a yi na yin garkuwa da mutum 31 a kan hanyar Buratai zuwa Kamuya da ke ƙaramar hukumar Biu a Jihar Borno. Rundunar ta ce dakarunta sun kai ɗauki ne bayan samun bayanan sirri, inda s**a yi artabu da maharan, lamarin da ya tilasta musu barin mutanen da s**a sace da kuma motocin fararen hula huɗu kafin su tsere zuwa cikin daji.

A wata sanarwa da muƙaddashin jami'in yaɗa labarai na Operation Hadin Kai, Keftin Mohammed Goni, ya fitar, ya ce lamarin ya faru da misalin ƙarfe 3:45 na ranar 31 ga Yulin 2026. Ya ce baya ga ceto mutum 31, sojojin sun kuma ƙwato wasu babura da maharan s**a bari yayin tserewa, sannan s**a raka waɗanda aka ceto zuwa Buratai domin su ci gaba da tafiyarsu cikin aminci.

A wani lamari mak**ancin wannan, dakarun rundunar Operation Wabaizigan sun kuɓutar da mutum 14 da aka yi garkuwa da su a Jihar Edo. Rundunar ta ce bayan samun rahoton garkuwa da mutanen a kan babbar hanyar Benin zuwa Legas, dakarun s**a bi sawun masu garkuwar, inda s**a tilasta musu sakin mutum 11. Washegari kuma, bayan wani samame a cikin daji, sojojin sun ceto sauran mutum uku, tare da bayyana cewa duk waɗanda aka kuɓutar na cikin ƙoshin lafiya, yayin da ake ci gaba da farautar masu garkuwa da mutanen.

Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na CBS da Wall Street Journal sun ce wasu masu ba Shugaban Amurka Donald Trump shawa...
01/08/2026

Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na CBS da Wall Street Journal sun ce wasu masu ba Shugaban Amurka Donald Trump shawara sun nuna adawa da shirin da ake zargin Amurka da Isra'ila ke yi na kai sabbin hare-hare kan cibiyoyin mak**ashi na Iran.

A cewar rahotannin, an tattauna batun ne a wani taron majalisar ministocin Trump da aka gudanar a Camp David, inda wasu daga cikin masu ba shi shawara s**a nuna rashin amincewarsu da ƙaddamar da sabon farmakin. CBS ta ce Amurka da Isra'ila na nazarin yiwuwar kai hare-hare masu ƙarfi kan muhimman cibiyoyin mak**ashin Iran, yayin da Wall Street Journal ta ruwaito cewa Trump ya amince da wani sabon shiri na ƙara matsin lamba ga Tehran.

Fadar White House ba ta tabbatar da rahotannin kai hare-haren ba kai tsaye, kuma ba ta musanta su ba. Sai dai ta sake jaddada matsayar Amurka cewa ba za ta bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba. Yayin da rikicin ya shiga wata na shida, har yanzu Amurka na matsa wa Iran ta dakatar da shirinta na nukiliya, yayin da Tehran ke ci gaba da ƙin amincewa da hakan.

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun k**a mutum shida da ake zargi da taimaka wa mayaƙan ƙ...
01/08/2026

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun k**a mutum shida da ake zargi da taimaka wa mayaƙan ƙungiyar ISWAP wajen gudanar da ayyukansu a garin Damasak da ke Jihar Borno.

A cewar rundunar, an k**a waɗanda ake zargin ne a ranar 27 ga Yulin 2026, bayan samun bayanan sirri da s**a nuna cewa suna taimaka wa ƙungiyar ta hanyar samar mata da kuɗaɗe ta hanyar saye da sayar da shanu a kasuwannin Gubio, Damasak da Ajuwango.

Sojojin sun ce sun ƙwace mak**ai, mota da kuɗi naira 317,950 daga hannun waɗanda ake zargin. Sun ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike, tare da jaddada aniyarsu ta ci gaba da daƙile hanyoyin samar da kuɗi da kayan aiki ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya bayyana dalilin da ya sa aurensa da matarsa Maimuna Musa ya mutu, bayan wa...
01/08/2026

Fitaccen jarumin Kannywood, Adam A. Zango, ya bayyana dalilin da ya sa aurensa da matarsa Maimuna Musa ya mutu, bayan wani ɗan lokaci da aka yi ana ta ce-ce-ku-ce kan lamarin.

A wani gajeren bidiyo da ya wallafa, jarumin ya ce rabuwar tasu ta samo asali ne daga bambancin ƙwayoyin halitta na haihuwa, ba wai wani dalili na daban ba.

Zango ya kuma roƙi masoyansa da su kwantar da hankulansu tare da mutunta wannan sabon yanayi da yake ciki.

“Har yanzu fa ban saki waƙar ‘Malam Ka Yi Rawa’ ba, kiɗan kawai na saki, domin abin da ke cikin waƙar ya fi kiɗan zafi, ...
01/08/2026

“Har yanzu fa ban saki waƙar ‘Malam Ka Yi Rawa’ ba, kiɗan kawai na saki, domin abin da ke cikin waƙar ya fi kiɗan zafi, amma ake ta haushi.”

— Dauda Kahutu Rarara, mawaƙin siyasa,

Ministan Kuɗi, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa mafi yawan kuɗaɗen da gwamnati ta samu bayan cire tallafin man fetur da gy...
31/07/2026

Ministan Kuɗi, Taiwo Oyedele, ya bayyana cewa mafi yawan kuɗaɗen da gwamnati ta samu bayan cire tallafin man fetur da gyaran tsarin canjin kuɗaɗen ƙasashen waje na tafiya ne wajen biyan basuss**an gwamnati da kuma ƙarin kuɗaɗen gudanarwa.

Oyedele ya bayyana hakan ne a taron African Emerging Markets Forum da aka gudanar a Abuja. Ya ce kafin cire tallafin, tallafin man fetur da tsarin canjin kuɗaɗen waje suna lashe kusan kashi biyar cikin ɗari na kuɗaɗen shiga na ƙasar. Sai dai bayan sauye-sauyen da aka aiwatar a shekarar 2023, kuɗin ruwa kan basuss**a ya ƙaru daga kusan kashi 8 zuwa kashi 24, lamarin da ya sa aka karkatar da wani ɓangare na kuɗaɗen wajen biyan basuss**a.

Ya kuma ce gwamnati ta ƙara yawan kuɗin da take kashewa bayan ninka mafi ƙarancin albashi zuwa naira 70,000 a wata, tare da faɗaɗa shirin ba da rancen ilimi da ke biyan kuɗin makaranta da kuma ba ɗalibai sama da miliyan 1.5 tallafin kuɗin rayuwa na wata-wata.

Ministan ya yi watsi da rahoton Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) da ya nuna cewa miliyoyin 'yan Najeriya na ci gaba da rayuwa cikin talauci duk da sauye-sauyen tattalin arziki. A cewarsa, raguwar ƙarfin sayen kuɗin jama'a na ɗan lokaci wani sak**ako ne da ba za a guje masa ba bayan cire tallafin.

‘’Ina so na yi amfani da wannan dama in yi wa 'yan comment section godiya. Sak**akon zagin da s**a yi min, na samu Dala ...
31/07/2026

‘’Ina so na yi amfani da wannan dama in yi wa 'yan comment section godiya. Sak**akon zagin da s**a yi min, na samu Dala 644 daga Facebook’’.

- Lawan Ahmad, Tauraron Kannywood

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausawa Global posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausawa Global:

Shortcuts

Share