01/08/2026
Kamfanin Dillancin Labaran Gwamnatin Jamhuriyar Nijar (ANP) ya ce wasu sojojin ƙasar sun mutu a wani hari da mayaƙan Boko Haram s**a kai a kusa da garin N'Guigmi da ke Jihar Diffa, a kudu maso gabashin ƙasar.
A cewar ANP, an kai harin ne a ranar Jumma'a a yankin da ke kusa da iyakar Najeriya, Kamaru da Chadi, inda ƙungiyar Boko Haram ke da sansanoni. Sai dai kamfanin bai bayyana adadin sojojin da s**a mutu ba, yana mai cewa gwamnan Jihar Diffa, Janar Mahamadou Ibrahim, ya halarci jana'izar waɗanda aka kashe.
Sai dai kamfanin dillancin labarai na AFP ya ambato wasu majiyoyi na cewa sojoji goma ne s**a rasa rayukansu a harin. Boko Haram ta fara tayar da ƙayar baya a arewacin Najeriya tun shekarar 2009, kuma daga baya hare-harenta s**a bazu zuwa Nijar, Kamaru da Chadi, lamarin da ya sa ƙasashen s**a kafa rundunar tsaro ta haɗin gwiwa domin yaƙar ƙungiyar.