31/05/2026
Gwamnoni na Tattaunawar Ɗaga Mafi Ƙarancin Albashi zuwa N100,000 – NGF
Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) kuma gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bayyana cewa gwamnoni na nazarin yiwuwar ƙara mafi ƙarancin albashin ƙasa daga N70,000 zuwa N100,000.
Jaridar Punch ta rawaito cewa AbdulRazaq ya bayyana hakan ne ta cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya danganta matakin da hauhawar farashi da kuma tsadar rayuwa da ma'aikata ke fuskanta a faɗin ƙasar nan.
Ya ce gwamnatocin jihohi na ci gaba da tattaunawa da gwamnatin tarayya da kuma ƙungiyoyin ƙwadago domin cimma matsaya kan sabon tsarin albashi wanda zai inganta rayuwar ma'aikata tare da tabbatar da cewa jihohi za su iya biyan albashin ba tare da tangarda ba.
A cewarsa, manufar ita ce ƙara ƙarfin sayen kayan masarufi na ma'aikata da kuma tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan raya ƙasa da samar da muhimman hidimomin jama'a.
A halin yanzu, mafi ƙarancin albashi a Najeriya na N70,000 a wata, duk da cewa wasu jihohi sun fara biyan albashi sama da wannan adadi.