Madubiya Online News

Madubiya Online News Labarai da dumiduminta

Hakika akwai darasi!!Sojaboy ya bi duk wata hanya ta sa6awa Allah domin samun daukaka amman ba inda ya je, ba wata nasar...
10/10/2025

Hakika akwai darasi!!

Sojaboy ya bi duk wata hanya ta sa6awa Allah domin samun daukaka amman ba inda ya je, ba wata nasara da ya samu, ya kashe kudi iya kudi amman Allah ya dulmuyarda shi.

Shi kuma Super uban lissafi ba kudi, ba ilimi, ba wayewa, amman lokaci daya Allah ya daukaka shi, ya yi nasara tare da trending. Kuma dukkanninsu 'yan Sokoto ne.

Malam, wallahi wayo ko dubara baza su sanya ka samu abinda Allah bai kaddare ka da samu ba, don haka ka mika lamarinka zuwa ga Allah, insha Allahu zaka samu abinda kake nema.

Daga S-bin Abdallah Sokoto

Ranar ‘Yan Social Media Ta Duniya!Wane ɗan Social Media ne a Najeriya rubuce-rubucensa yafi burgeka, kuma kake ganin yan...
10/10/2025

Ranar ‘Yan Social Media Ta Duniya!

Wane ɗan Social Media ne a Najeriya rubuce-rubucensa yafi burgeka, kuma kake ganin yana da amfani ga al’umma?

Kuyi mana mention* dinsa a comment section mu yaba da nagarta da tasirinsa!

CIGIYA: Ana Neman Aishatu MufidaAn nemi wata yarinya mai suna Aishatu Mufida, ’yar shekara 13, ’yar Malam Yahaya Jibrin....
06/10/2025

CIGIYA: Ana Neman Aishatu Mufida

An nemi wata yarinya mai suna Aishatu Mufida, ’yar shekara 13, ’yar Malam Yahaya Jibrin. Gidansu yana unguwar Chiroma (kusa da ƙaramin asibiti) a cikin garin Dukku, Jihar Gombe.

Aishatu Mufida ta ɓar gida tun ranar Talata, 30/9/2025, bayan sallar Azahar. Har zuwa yanzu ba a san inda take ba. An bincika wajen makwabta da sauran wuraren da ake zaton za a same ta, amma ba a same ta ba.

Idan Allah Ya nufa wani ya ganta, ana roƙon shi da ya taimaka ya dawo da ita gida, ko ya kai ta gidan Mai unguwa ko Hakimi, ko kuma ya kira mahaifinta a waɗannan lambobin:

📞 0802 110 2983
📞 0806 469 4283

Allah Ya sa a same ta lafiya.

Hanyar Gombe Zuwa Biu Na Bukatar Gyaran Gaggawa, Inji Sadiq Abdallah GombeWani ɗan ƙasa mai kishin ci gaban al'umma, Sad...
06/10/2025

Hanyar Gombe Zuwa Biu Na Bukatar Gyaran Gaggawa, Inji Sadiq Abdallah Gombe

Wani ɗan ƙasa mai kishin ci gaban al'umma, Sadiq Abdallah Gombe, ya bayyana damuwa kan tabarbarewar hanyar Gombe zuwa Biu, yana mai cewa hanyar na buƙatar agajin gaggawa domin rage asarar rayuka da dukiyoyi da ake fuskanta a kullum.

Ya roƙi Gwamnatin Tarayya, wakilan majalisa daga jihohin Gombe da Borno – musamman Sanatoci da 'yan Majalisar Wakilai – da su ɗauki lamarin da muhimmanci su kuma tashi tsaye don ganin an gyara hanyar.

Baya ga haka, ya nemi Kungiyar North East Development Commission (NEDC) da ta saka baki, tare da kiraye-kirayen a ga alhakin da ke wuyan kowa wajen ganin an kawo karshen wannan matsala.

"Kar ayi tuya a manta da albasa," in ji Sadiq, yana mai cewa bai k**ata a cigaba da yin shiru kan wannan matsala da ke barazana ga rayuwar jama'a.

Dorinar Ruwa Ta Halaka Matashi Mai Kamun Kifi A Kogin Dadinkowa, Dake Jihar GombeDaga Muhammad Kwairi WaziriWani matashi...
06/10/2025

Dorinar Ruwa Ta Halaka Matashi Mai Kamun Kifi A Kogin Dadinkowa, Dake Jihar Gombe

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Wani matashi mai sana’ar kamun kifi, Yahuza Kwadda, ya rasa ransa a cikin Kogin Dadinkowa da ke jihar Gombe bayan wata dorinar ruwa ta kai masa hari yayin da yake cikin ruwa yana kamun kifi.

A cewar mazaunin yankin, Sadiq Abdallah, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce dorinar ta biyo matashin ne kai tsaye a cikin kogin, inda ta kifar da kwale-kwalensu, s**a watse, kowa yana ƙoƙarin ceton ransa.

Yahuza ya yi ƙoƙarin tsira, amma dorinar ta ci gaba da binsa cikin kogin har ta kashe shi, lamari ya tayar da hankalin mazauna yankin, musamman ma masu sana’ar kamun kifi.

Har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, ba a samu gawar Yahuza ba, sai dai ana ci gaba da gudanar da bincike da neman sa a cikin kogin.

Jama’a sun shiga jimami tare da yin addu’ar Allah ya gafarta masa da kuma bai wa iyalansa haƙurin jure wannan rashin.

DA DUMI-DUMI: Sarkin Nafada Ya Kaddamar Da Sabbin Dokokin Rage Tsadar Aure A GarinDaga Muhammad Kwairi WaziriWakilin Mai...
06/10/2025

DA DUMI-DUMI: Sarkin Nafada Ya Kaddamar Da Sabbin Dokokin Rage Tsadar Aure A Garin

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Wakilin Mai Martaba Sarkin Nafada, Alhaji Umaru Muhammad Baraya (Madakin Nafada), dake jihar Gombe, ya gabatar da sabon tsarin rage tsadar aure da kuma magance matsalolin da ke hana sauƙin aure a cikin al’umma. Taron ya gudana ne a Unguwar Madaki, Gundumar Nafada Central Ward, tare da goyon bayan manyan hukumomi, kotun majistare, da jami’an tsaro.

Sabon dokar za ta fara aiki daga shekara ta 2025, inda matasa s**a samu gargadi mai tsanani da kada su tsokani ko raina ’yan mata da kalaman "aure yayi arha". Duk wanda aka k**a yana aikata hakan zai fuskanci hukunci.

Wannan mataki na daga cikin kokarin da ake yi don karfafa tarbiyya da inganta zaman lafiya a Nafada da Jihar Gombe baki ɗaya.

YANZU-YANZU: An Karrama Mawaki Rarara Da Digirin DigirgirJami'ar European-American ne s**a karrama shi, inda taron ya sa...
20/09/2025

YANZU-YANZU: An Karrama Mawaki Rarara Da Digirin Digirgir

Jami'ar European-American ne s**a karrama shi, inda taron ya samu halartan masu fada a ji.

YANZU-YANZU: Yadda Ƴan Achaba Ke Cigaba Da Zanga-zanga A Cikin Garin BauchiƳan achaba a garin Bauchi sun shiga zanga-zan...
20/09/2025

YANZU-YANZU: Yadda Ƴan Achaba Ke Cigaba Da Zanga-zanga A Cikin Garin Bauchi

Ƴan achaba a garin Bauchi sun shiga zanga-zanga suna nuna ƙorafi kan yadda ake cafke musu babura bisa rashin lambar allo (plate number), lambar jiki (body number), da kuma takardar lasisin tuki.

Bayan sun isa ofishin hukumar da ke kula da ababen hawa domin bayyana damuwarsu, rikici ya kaure wanda ya tilasta jami’an tsaro shiga tsakani don kwantar da tarzoma.

Ƴan achaban sun bazu cikin unguwanni daban-daban na Bauchi, suna zagaye suna neman a saurare su. Hotuna daga wurin sun nuna yanda lamarin ya ɗauki hankalin jama’a da hukumomin tsaro.

Ana sa ran hukumomi za su yi duba na musamman don warware matsalar cikin lumana.

DA DUMI-DUMI: Shugabannin jam'iyyar hadaka ADC na jihar Gombe sun gana da Atiku Abubakar, karkashin jagorancin halastacc...
19/09/2025

DA DUMI-DUMI: Shugabannin jam'iyyar hadaka ADC na jihar Gombe sun gana da Atiku Abubakar, karkashin jagorancin halastaccen shugaban jam'iyyar na jihar Gombe Mallam Danladi Yau.

A tare da shugaban jam'iyyar akwai sakataren jam'iyyar na jihar Gombe da mataimakin shugaban jam'iyyar da sauran shugabanni.

Da Ɗumi-Ɗumi:- DWI Ta yi Allah-wadai da Zarge-zarge mara sa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungi...
19/09/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- DWI Ta yi Allah-wadai da Zarge-zarge mara sa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

Ɗa Ɗumi-Ɗumi:- Jam'iyyar hadaka ta ADC ta jihar Gombe tace bata shirya wani taro a jihar Gombe ba, jam'iyyar tace masu k...
18/09/2025

Ɗa Ɗumi-Ɗumi:- Jam'iyyar hadaka ta ADC ta jihar Gombe tace bata shirya wani taro a jihar Gombe ba, jam'iyyar tace masu kokarin shirya taron ba 'yayan jam'iyyar bane.

Jam'iyyar ADC reshen Jihar Gombe tana sanar da yaya da magoya bayanta dama ɗokacin al'umma cewa babu wani taron data shirya a hotel na Maidugu a gobe juma'ar nan 19/09/2025.

Masu iƙirarin shirya wannan taro ba ƴaƴan jam'iyyar ADC ba ne.

Don haka shugabannin jam'iyyar ta ADC na Jihar Gombe suke ankarar da jama'a su yi watsi da wannan taro, sannan suna kira ga jami'an tsaro su ɗauki matakin da ya dace kan masu yin sojan gona da sunan Jam'iyyar ADC a Jihar Gombe.

Wannan saƙo ankararwa ne na musamman daga shugaban Jam'iyyar ADC na Jihar Gombe, Malam Danladi Ya'u.

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Ch

Address

Zoo Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madubiya Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madubiya Online News:

Share