Kokiya

Kokiya Jaridar Kokiya jarida ce Mai yada labarai cikin harshen Hausa

domin Karin bayani +2348068171406
(1)

Kafin karfe 12 na rana, Tinubu zai sha kaye a zaben 2027, inji Hon Gudaji Kazaure. Me za ku ce?
30/07/2025

Kafin karfe 12 na rana, Tinubu zai sha kaye a zaben 2027, inji Hon Gudaji Kazaure.

Me za ku ce?

Gwamna Abba Mu Ma Ga Kokenmu Na Gyaran Makarantar Haddar Alƙur'ani Ta G.T.Q.S.S Kiru.Ya maigirma Gwamna, muna yi maka fa...
30/07/2025

Gwamna Abba Mu Ma Ga Kokenmu Na Gyaran Makarantar Haddar Alƙur'ani Ta G.T.Q.S.S Kiru.

Ya maigirma Gwamna, muna yi maka fatan alkairi, sannan Muna so mu yi kira da kai a kan wani babban aikin alkhairi na gyara babbar makarantar Sikandiren Haddar Alƙur'ani da ke garin ƙiru.

Ya maigirma Gwamna, wannan makaranta ce da aka ƙirƙira a shekararar 1999, Amman tun daga wannan lokaci har zuwa yau babu wani shugaba da ya taɓa waiwayarta ya gyara ta.

Ya mai girma Gwamna, wannan makaranta ce Tilo da babu irinta a jihar Kano, mai ɗalibai sama da 4,000 ta yaye dubban mahaddata da malamai a jihar Kano, kuma tana kan yayewa. Tabbas matasan malamai da mahaddata da suke Kano , kaso 50 cikin ɗari Ɗaliban ta ne. Daga irin dalibanta ne a ka samu wanda ya zo na ɗaya a gasar musabuƙar alƙur'ani ta Duniya a shekarun baya, wanda hakan ya ƙarawa Kano ƙima da mutunci ta ɓangaren addini a Duniya.

Tabbas ba bu abin da ake koyarwa a makarantar face Allah ya ce, Annabi ya ce, safiya da rana da dare. Batu na Haddar Alƙur'ani kuwa dama Gidanshi ne.

A yanzu haka makarantar na neman rushewa, a dena kai ɗalibai, saboda matsaloli k**ar haka:

1. Dakunan kwanan da azuzuwan karatu zuba suke lokutan damina, ba Ni tagogi da ƙofifi da gadaje da banɗakuna da kujeru. don haka dalibai ba sa iya barci ko karatu cikin natsuwa

2. Ƙarancin Malamai, Makarantar na fuskantar ƙarancin malamai da za su sadaukar da rayuwarsu, musamman na addini. A baya an samu malaman da su ka rinƙa biyan wasu malaman daga salary ɗinsu domin su zo su tallafa, duka dan ganin sun ciyar da harkar addini gaba a Kano.

Tabbas Tahfeez Kiru makaranta ce ta al'ummar jihar Kano, ci gabata tamkar ci gaban addini ne a jihar, durkushewarta tamkar koma baya ne ga ilimin addinin musulunci a jihar Kano.

Muna fata kowa ya bada gudunmawar shi wajen yaɗawa har sakon ya kai ga Gwamnan Kano, ko wasu masu kishin da za su iya kawo ɗauki, Allah ya saka wa duk wanda ya taimaka da alkairi saboda aikin alkhairi ne.

Wannan hoto yana nuna ɗaya daga cikin manyan laifukan da mulkin mallaka ya aikata. Farar fatar da ke cikin hoton jami’in...
30/07/2025

Wannan hoto yana nuna ɗaya daga cikin manyan laifukan da mulkin mallaka ya aikata. Farar fatar da ke cikin hoton jami’in Turai ne a ƙasar Kongo, kuma yaron da ke kusa da shi yana rike da hannunsa da aka sar # — yana nuna bacin rai da azaba.

A zamanin mulkin Sarki Leopold na II na ƙasar Belgium, an tilasta wa mutanen gida su tara roba daga bishiyoyi. Wadanda s**a kasa cika ƙayyadaddun adadi na roba da aka sa su, ana hukunta su da azaba mai tsanani — ana sar # musu hannaye, kafa da kuma sauran sassa na jiki a matsayin hukunci ko kuma shaida cewa an kas$e su. Wannan lokacin da aka sani da ‘Congo Free State’ ya yi sanadin mutuw@r miliyoyin 'yan Afirka.

Wani Matashi Ya Nuna Jimaminsa Bisa Rasuwar Janar Buhari, A Ranar Da Ya Gama Makaranta, Inda Ya Zana Hoton Buhari A Jiki...
30/07/2025

Wani Matashi Ya Nuna Jimaminsa Bisa Rasuwar Janar Buhari, A Ranar Da Ya Gama Makaranta, Inda Ya Zana Hoton Buhari A Jikin Rigarsa, Tare Da Rubuta Cewa Ya Yi Kewar Tsohon Shugaban Kasan

Matashin dan yankin Alkaleri ne dake jihar Bauchi.

Me za ku ce

Nayi mamaki da kwankwaso daya fito yace gwamnatin Tinubu ta fifita kudancin Nigeria akan arewacin Nigeria dan yaga bukat...
30/07/2025

Nayi mamaki da kwankwaso daya fito yace gwamnatin Tinubu ta fifita kudancin Nigeria akan arewacin Nigeria dan yaga bukatar sa bata biya ba ta shiga jam'iyar APC ba har itama gwamnatin Tinubu ta biye mai suke wasa da hankali talakawan nigeria in maye ya manta uwar da bata manta ba ya manta su s**a kawo gwamnatin Tinubu ya fito takarar shugaban kasa ta gangan dan kada dan arewacin Nigeria yayi nasara 2023

(1)Waye ya koyawa gwamnoni a Nigeria hana local government grant ana samun percentage mai tsoka
(2)Waye yayi mulki a jiharsa har yanzu burinsa ya cigaba da mulkar jihar sa
(3)Waye ya fito takarar shugaban kasa ta gangan dan arusa arewacin nigeria 2023
(4)Waye lokacin obasanjo akayi amfani da shi aka rusa arewacin nigeria da yiwa manyan arewacin nigeria ritayar dole !!
(5)Waye ya rusa darajar marautar kano number daya a duniya
(6)Waye yake bada umarni aka ringa rusa dukiyar yan kasuwar jihar sa
(7)Waye yace kifi ya cinye dukiyar al-ummar nigeria
(8)Waye yayiwa dukiyar yan fansho zagon kasa
(9)Waye ya cinye kudin 44 local government's five kilometers.

Cewar Dan Gwagwarmaya a Nigeria
Jabir A Bichi

Gwamna Bala Mohammed Ya Tashi Zuwa Banjul Tare da Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Don Halartar Taron Sahel Govern...
29/07/2025

Gwamna Bala Mohammed Ya Tashi Zuwa Banjul Tare da Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan Don Halartar Taron Sahel Governance Forum

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, a yau ya bar Najeriya zuwa Banjul, babban birnin ƙasar Gambiya, domin halartar zaman farko na Sahel Governance Forum, wanda za a gudanar daga 30 zuwa 31 ga Yuli, 2025.

An gayyaci Gwamna Bala a matsayin babban bako mai matsayi na kasa da kasa da kuma dan majalisar tattaunawa a taron, bisa gayyatar Goodluck Jonathan Foundation, wanda ke shirya taron tare da hadin gwiwar Gwamnatin Gambiya, Shirin Raya Kasashe na Majalisar Dinkin Duniya (UNDP – WACA), Ofishin UN don Yammacin da Tsakiyar Afirka (UNOWAS), da Ofishin Hadin Gwiwa na Musamman Kan Cigaba a Sahel.

A yayin zaman, Gwamna Bala zai kasance tare da tsohon shugaban Najeriya, Dr. Goodluck Ebele Jonathan, da sauran manyan shugabannin yankin Sahel domin gudanar da muhimman tattaunawa kan kyakkyawan shugabanci, ginin zaman lafiya, da cigaba mai dorewa a wannan yankin mai fama da ƙalubale.

Muhimmancin Ziyarar

Taron Sahel Governance Forum na nufin samar da dandalin fahimta tsakanin jagororin yankin, domin lalubo hanyoyin da za su taimaka wajen magance matsalolin tsaro, koma-bayan tattalin arziki, da ci gaban da ya dace da al’ummar yankin Sahel.

LABARIN WATA TIRELAR GIYA DA HISBAH Wannan labarin na ɗauke da ƙalubalen da hukumar Hisbah take fuskanta game da abin da...
29/07/2025

LABARIN WATA TIRELAR GIYA DA HISBAH

Wannan labarin na ɗauke da ƙalubalen da hukumar Hisbah take fuskanta game da abin da ya shafi doka.

Yadda Abin ya faru

Hukumar Hisbah ta taɓa k**a tirela maƙare da giya, ta kai wannan mota kotu, masu giyar s**a ɗau lauya, hukumar Hisbah ita ma ta ɗau lauya, aka je Hisbah ta gabatar da dokokin ta da s**a hana sha da sarrafawa da kuma ta,amuli da duk kayan maye, don haka ta nemi Alƙali da yayi hukunci akan wannan TIRELAR, cewa ya ƙwace ta, ya damƙa wa hukumar Hisbah tare da court order aje a ƙone ta.

Sai lauyan ɓangaren masu mota ya tashi yace, ita wannan mota ta giya da aka k**a an k**a ta ne akan titin gwamnatin tarayya, inda dokar jiha bata aiki, saboda haka ina roqon mai girma Alƙali da ya saki wannan motar kuma ya umarci yan HISBAH suyi mata rakiya har ta bar jihar nan.

Alƙali yace ya gamsu da hujjojin da wannan lauya ya bayar don haka an saki wannan motar, yan HISBAH ku sa mota gaba, kusa mota baya, kusa motan giya a tsakiya, kuyi mata rakiya ta bar jihar.

Sai wani ya koma gefe ya raɗa wa ƴan HISBAH idan kun je wuri kaza, motar zata yi clear, to titin da zata hau na jiha ne, ku riqe ta a nan, ƴan HISBAH s**a yi rakiya ransu a ɓace ,sai iya wanda ya san bayanin, zuwa can zasu wuce sai s**a yi kwana, sai ga su sun faɗo kan titin jiha, sai yan HISBAH s**a ce ayi parking, an karya doka, mu koma, aka koma.

HISBAH ta ce to mun yi ɗa,a da biyayya lokacin da aka k**a giyan nan, kan titin nan na federal government ne, an bamu umarni mu je mu rakata, to mun rakata sai kuma ta faɗo kan titin jiha sai muka k**a ta.

Sai Alƙali yace, to yanxu kuma kuje ku fasata, kai kuma an baka kwana talatin (30) ai zaka yi appeal (ɗaukaka ƙara), in kwana talatin (30) ya cika baka yi appeal ba hukumar Hisbah, tazo ta karɓi court order taje ta gama da wannan giyan.

Daga cikin Maƙalar da SHEIKH AMINU IBRAHIM DAURAWA ya gabatar a ABU ZARIA.

Mai TAKEN ƘALUBALEN DA AIKIN HISBAH YAKE

Tinubu ya baiwa ƴan wasan Super Falcons kyautar lambar girma ta ƙasa da dala dubu 100 ga kowacce Shugaba Bola Ahmed Tinu...
29/07/2025

Tinubu ya baiwa ƴan wasan Super Falcons kyautar lambar girma ta ƙasa da dala dubu 100 ga kowacce

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bai wa 'Yan tawogar ƙwallon ƙafar mata ta ƙasa, Super Falcons lambar girmamawa ta kasa ta 'Officer of the Order of the Niger (OON)' saboda nasarar da su ka samu.

A ranar Asabar ne Super Falcons su ka doke kasar Morocco, wacce ta karɓi baƙuncin gasar, inda s**a lashe kofin WAFCON karo na goma (10) a tarihi.

Shugaba Tinubu, wanda ya tarbi tawagar ta Super Falcons a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, ya kuma bayyana cewa kowacce daga cikin ƴan wasa 24 za ta samu kudi daidai da dala $100,000.

“Na karɓi wannan kofi a madadin daukacin yan Najeriya, kuma ina mai cewa: na gode da jajircewarku, kishinku da kuma tuna mana da ƙarfin hali da ruhin Najeriya.

"A madadin ƙasa mai godiya, ina bai wa 'yan wasan da kuma kociyoyin su guda 11 lambar girmamawa ta Officer of the Order of the Niger (OON).” inji Tinubu.

Jabir A Bichi dan gwagwarmaya a nigeria Budaddiyar wasika zuwa ga gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf Cikin ikon Allah z...
28/07/2025

Jabir A Bichi dan gwagwarmaya a nigeria

Budaddiyar wasika zuwa ga gwamnan jihar kano Abba Kabir Yusuf

Cikin ikon Allah zanyi amfani da wannan damar na bawa gwamnan jihar kano abba kabir yusuf shawara daya kai kudiri zauran majalisar jihar kano don a amin cemai ya fidda kudin don sabunta makarantun jihar kano gaba daya da sabunta asibitocin jihar kano gaba daya da samar da asibitin sha katafi a mazabun jihar kano gaba daya don bawa mutannan karkara taimakon gaggawa akan lokaci
ina fatan mai girma gwamnan jihar abba kabir yusuf zai duba wannan shawarar tawa da idon basira ba tarai da adawa ba Allah ya bawa jihar kano da nigeria cigaba mai amfani

Cewar Dan Gwagwarmaya a Nigeria
Jabir A Bichi

Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, Ya Yi Hasashen Komawar Peter Obi Zuwa Jam’iyyar PDPTsohon gwamnan j...
28/07/2025

Tsohon Gwamnan Jihar Borno, Sanata Ali Modu Sheriff, Ya Yi Hasashen Komawar Peter Obi Zuwa Jam’iyyar PDP

Tsohon gwamnan jihar Borno kuma jigo a siyasar Najeriya, Sanata Ali Modu Sheriff, ya bayyana cewa akwai alamun cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Mista Peter Obi, na dab da komawa jam’iyyar PDP domin sake yin takara a zaben shugaban kasa na 2027.

Sanata Sheriff ya ce, “Bisa bayanan da ke gabana, duk da cewa ba zan fadi komai a hukumance ba, akwai yiwuwar Peter Obi zai dawo jam’iyyar PDP a kowane lokaci daga yanzu, kuma zai tsaya takarar shugaban kasa a ƙarƙashin tutar PDP.”

Wannan furuci na zuwa a daidai lokacin da ake ci gaba da rade-radin sauyin matsayi daga wasu fitattun ’yan siyasa a Najeriya, musamman yayin da shirye-shiryen zaben 2027 ke kara daukar zafi.

Peter Obi, wanda ya taba kasancewa mataimakin dan takarar shugaban kasa a PDP kafin ya fice daga jam’iyyar a shekarar 2022 domin tsayawa takara a karkashin Labour Party, bai kai ga yin wani karin bayani kan maganar ba a hukumance. Sai dai maganganun Sanata Sheriff na iya janyo ce-ce-ku-ce.

Dan Gwagwarmaya Jabir A Bichi: Da Dan Arewa Ne Ya Yada Cewa Buhari Ya Saki Aisha, Da Tuni An K**a ShiWani dan gwagwarmay...
28/07/2025

Dan Gwagwarmaya Jabir A Bichi: Da Dan Arewa Ne Ya Yada Cewa Buhari Ya Saki Aisha, Da Tuni An K**a Shi

Wani dan gwagwarmaya a Najeriya, Jabir A. Bichi, ya bayyana cewa idan wani dan Arewa ne ya yada jita-jitar cewa marigayi tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya saki matarsa Aisha Buhari kafin rasuwarsa, da tuni jami'an tsaro sun cafke shi, ko da kuwa ya fito ya karyata maganar.

Jabir ya ce hakan na nuna yadda ake daukar mataki cikin gaggawa akan mutane, musamman ‘yan Arewa, idan s**a fadi wani abu da bai yi wa wasu ko gwamnati dadi ba.

Ya kara da cewa:
"Wallahi, nayi imani cewa in dan Arewacin Najeriya ne ya yada cewa marigayi Muhammadu Buhari ya saki Aisha Buhari kafin ya rasu, da tuni ko addu’ar uku ba za a bari a yi ba, jami’an tsaro da tuni sun cafke shi, ko da kuwa ya fito ya karyata maganar."

Wannan furuci ya janyo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda masu fashin baki ke ganin akwai bukatar a rika kallon duk ‘yan kasa da idon adalci, ba tare da nuna bambanci ba.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kokiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share