Kokiya

Kokiya Jaridar Kokiya jarida ce Mai yada labarai cikin harshen Hausa

domin Karin bayani +2348068171406
(2)

*Taɓarɓarewar tsaro, cin hanci da rashawa da matsin tattalin arziki shi ya sa muka so kifar da gwamnatin Tinubu" - Inji ...
10/08/2026

*Taɓarɓarewar tsaro, cin hanci da rashawa da matsin tattalin arziki shi ya sa muka so kifar da gwamnatin Tinubu" - Inji Kanal Ma'aji da ya so jagorantar yi wa Tinubu juyin mulki k**ar yadda ya fada ma matsu yi masa tambayoyi

Ƙungiyar NANS na bukatar a sa sharadin biyan N200 ga masu neman shiga shirin NYSC Ƙungiyar ɗaliban Nijeriya (NANS) ta bu...
10/08/2026

Ƙungiyar NANS na bukatar a sa sharadin biyan N200 ga masu neman shiga shirin NYSC

Ƙungiyar ɗaliban Nijeriya (NANS) ta buƙaci a mayar da biyan Naira 200 na shekara-shekara ya zama cikin sharudan da ɗalibai za su cika kafin a tura su shirin bautar ƙasa na NYSC.

Shugaban NANS na ƙasa, Akinteye Babatunde ne ya bayyana hakan a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, yayin da yake magana kan harkokin kuɗin ƙungiyar da kuma shirin sauya tsarin karɓar kuɗaɗen ƙungiyar.

KUNGA RABO FA
10/08/2026

KUNGA RABO FA

Idan ka sani fadi mana sunansa.
10/08/2026

Idan ka sani fadi mana sunansa.

Wani mummunan al'amari ya faru a ƙauyen Unguwar Baƙo da ke ƙaramar hukumar Ƙankara a jihar Katsina.Rahotanni sun ce wasu...
10/08/2026

Wani mummunan al'amari ya faru a ƙauyen Unguwar Baƙo da ke ƙaramar hukumar Ƙankara a jihar Katsina.

Rahotanni sun ce wasu mahara sun shiga wani shago da ake cajin waya, inda s**a umarci mai shagon da ya ba su wayoyin da ke hannunsa. Sai dai mutumin ya ƙi, yana mai bayyana cewa wayoyin amanar mutane ne, ba nasa ba ne, don haka ba zai iya ba su ba.

A cewar rahoton, nan take maharan s**a harbe shi. Mahaifiyarsa da ta ji ƙarar harbin ta fito daga cikin gida domin ganin abin da ke faruwa, ita ma aka kashe ta a wurin.

An ce lamarin ya faru ne a jiya, kuma ya jefa al'ummar yankin cikin alhini da jimami.
Allah Maɗaukakin Sarki Ya yi wa mamatan rahama, Ya karɓi shahadarsu, Ya ba iyalansu da al'ummar yankin haƙurin jure wannan babban rashi. Amin.

Daga Abubakar Usman Naibi

Malam Haruna Bashir magidancin da aka yi wa matarsa da ƴaƴansa kisan gilla, a Dorayi kano yayin walimar sabon aurensa a ...
10/08/2026

Malam Haruna Bashir magidancin da aka yi wa matarsa da ƴaƴansa kisan gilla, a Dorayi kano yayin walimar sabon aurensa a cikin auren gata na Gwamnatin Kano.

Rabeh Zubair Ibn Fadlallah (Rabeh)Daular Borno tsohuwar Daula ce a Afirka da aka kafa tun kafin karni na 10 wacce ta had...
10/08/2026

Rabeh Zubair Ibn Fadlallah (Rabeh)

Daular Borno tsohuwar Daula ce a Afirka da aka kafa tun kafin karni na 10 wacce ta hada da yankunan da yanzu ke cikin Najeriya da Nijar da Chadi da Kamaru da Sudan har Libya. Daular Kanem ta El Kanemi ta samo asali ne daga daular Saifuwa.

Rabih az-Zubayr bin Fadlallah (da larabci رابح فضل الله , رابح الزبير ابن فضل الله mai cinikin bayi ne wanda ta hanyar cin nasara ya kafa daula mai girma da karfi a Tsakiya da Yammacin Afirka a ƙarshen karni na 19. Babban hamshakin soja kuma shugaba, Rabih ya maye gurbin daular al-Kanemi na Daular Kanem–Bornu tare da dakile muradun Turawa a yankin na tsawon shekaru da dama.

Rabeh Zubair Ibn Fadlallah mutum ne da ya taso daga Sudan, wanda ke sana'ar fataucin bayi, inda yake saye ya kuma sayar da bayi. Masanin tarihi Zanna Boguma ya ce fataucin bayi ne dalilin da ya sa Rabeh ya yaki Borno.

A 1893 ne Rabeh ya kawo wa Borno hari.

"Rabeh Zubair Ibn Fadlallah ne ya rushe tsohuwar daular Borno bayan ya kaddamar da yaki kuma ya samu galabar kwace iko ya mayar da Dikwa a matsayin babban birnin daularsa". Rabeh ya kashe sarakunan Borno guda biyu, Shehu Kyarimi da Shehu Sanda Wudoroma.

A ranar 22 ga Afrilu, 1900, sojojin Faransa s**a yi wa sansaninsa kawanya a yakin Kousséri, inda aka kashe Rabeh yayin da yake kokarin tserewa ta kogin Chari, bayan ya yi mulki a shekaru bakwai da watanni bakwai da kwanaki bakwai a Borno. Dansa Fadlallah ya ci gaba da gwagwarmaya na dan lokaci kafin shi ma turawan Faransa s**a kashe shi, shi ma a shekarar 1901.

Bayan sun kashe Rabeh ne s**a aza Shehu Sanda Kura daga zuriyar Elkanemi a matsayin Shehun Borno a Dikwa a 1900. A 1901 s**a tube shi s**a kuma daura dan uwansa Umar Abubakar Garbai, kakan Shehun Borno na yanzu.

Lokacin Turawan mulkin Mallaka, tsohuwar Masarautar Borno ta rabu gida biyu inda Dikwa ta koma karkashin ikon turawan mulkin mallaka na Jamus, bisa wata yarjejeniya tsakanin turawan Faransa da Birtaniya da kuma Jamus na mulkin mallaka.

Daga baya Abubak

Abin takaici ne idan muka tuna cewa, kakaninmu sun rayu ne a cikin irin wannan yanayi...
10/08/2026

Abin takaici ne idan muka tuna cewa, kakaninmu sun rayu ne a cikin irin wannan yanayi...

Kotu a Kano ta bada umarnin tsare matar da ake zargi da yanke wa saurayinta al’auraWata Kotun Majistare da ke Gyadi-Gyad...
10/08/2026

Kotu a Kano ta bada umarnin tsare matar da ake zargi da yanke wa saurayinta al’aura

Wata Kotun Majistare da ke Gyadi-Gyadi a Kano ta bayar da umarnin tsare Maimunatu Idris, mai shekara 25, wadda ake zargi da yanke wa saurayinta al’aura da wuka a wani otal da ke Badawa, Kano.

An gurfanar da Maimunatu a gaban kotun bisa zargin haddasa mummunan rauni da kuma yunƙurin kisa.

Alkalin kotun mai lamba 40, Mai Shari’a Sadiya Usman, ta saurari ƙarar bayan lauyan gwamnati, Barrista H. A. Sani Buhari, ya nemi izinin karanta wa wadda ake zargin takardar tuhuma.

A yayin zaman, Maimunatu ta amsa zargin yin rauni, wanda kotun Majistare ke da hurumin saurara, yayin da ba ta amsa zargin yunƙurin kisa ba, kasancewar kotun ba ta da hurumin sauraron irin wannan tuhuma.

Daga bisani, mai gabatar da ƙara ya nemi a sanya ranar ci gaba da shari’ar, inda kotun ta sanya ranar 9 ga Satumba, 2026.

Mai Shari’a Usman ta kuma bayar da umarnin ci gaba da tsare Maimunatu a gidan yari har zuwa ranar da za a sake sauraron ƙarar.

Rahotanni sun ce Maimunatu, wadda asalinta ‘yar ƙaramar hukumar Maigatari ce a Jihar Jigawa, an k**a ta ne a ranar 27 ga Yuli, 2026, bayan zargin kai wa saurayinta hari a Durbar Hotel da ke Kano.

Ana zargin cewa ta gayyaci saurayin nata zuwa otal domin su zauna tare, kafin daga bisani ta yi amfani da wuka ta kai masa harin bayan ta gano cewa yana shirin auren wata mace.

An garzaya da wanda lamarin ya rutsa da shi zuwa Asibitin Urology na Abubakar Imam domin samun kulawar gaggawa, yayin da ‘yan sanda s**a kwato wukar da ake zargin an yi amfani da ita tare da k**a Maimunatu a wurin.

Mahaifin Lionel Messi ya mutu Mahaifin shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Argentina, Lionel Messi, Jorge Messi, ya ra...
09/08/2026

Mahaifin Lionel Messi ya mutu

Mahaifin shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Argentina, Lionel Messi, Jorge Messi, ya rasu yana da shekara 68 k**ar yadda jaridar PUNCH ta rawaito.

Rahotanni sun ce Jorge ya rasu ne da misalin ƙarfe 10 na dare ranar Juma’a a wani asibiti da ke birnin Rosario na Argentina, bayan fama da rashin lafiya na dogon lokaci.

Jorge ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa rayuwar ɗansa Messi, musamman lokacin da yake ƙarami. Ya taimaka wajen ganin an samu maganin da Messi ke buƙata domin matsalar girma, sannan ya taimaka wajen kai shi Barcelona yana da shekara 13.

Ya kuma kasance wakilin Messi na tsawon shekaru, yana kula da harkokin kwangiloli da yarjejeniyoyin kasuwanci na ɗansa.

Jorge, wanda ke da ‘ya’ya huɗu, Lionel, Rodrigo, Matias da Maria Sol, ya kasance mutum mai ƙauracewa haske duk da muhimmiyar rawar da ya taka a rayuwar ɗansa.

Mutuwar tasa ta zo ne bayan an samu rahotannin cewa yana fama da rashin lafiya, lamarin da ya sa Messi ya bayyana damuwarsa kan halin da iyalinsa ke ciki a lokacin gasar cin kofin duniya ta 2026.

Rasuwar Jorge ta yi babban gibi ga iyalin Messi, musamman ganin irin gudunmawar da ya bayar wajen taimaka wa ɗansa ya zama ɗaya daga cikin fitattun ‘yan wasan ƙwallon ƙafa a tarihi.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kokiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share