Kokiya

Kokiya Jaridar Kokiya jarida ce Mai yada labarai cikin harshen Hausa

domin Karin bayani +2348068171406
(1)

Wasu sabbin hotunan da jaruma Nafisa Abdullahi ta dauka a kasar America.
11/05/2026

Wasu sabbin hotunan da jaruma Nafisa Abdullahi ta dauka a kasar America.

2027: Tinubu ne ya kafa jam'iyyar NDC don ya yi wa ƴan adawa illa - ADCJam’iyyar adawa ta ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bol...
11/05/2026

2027: Tinubu ne ya kafa jam'iyyar NDC don ya yi wa ƴan adawa illa - ADC

Jam’iyyar adawa ta ADC ta zargi Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma jam’iyyarsa ta APC da hannu wajen kafa sabuwar jam’iyyar NDC domin raunata haɗin kan ƴan adawa a Najeriya.

BBC ta rawaito cewa, zargin na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tafka muhawara tsakanin jam’iyyun siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

A cewar ADC, kafa jam’iyyar NDC wata dabara ce da aka ƙirƙira domin raba kan masu jefa ƙuri’a ga jam’iyyun hamayya, tare da rage ƙarfin manyan jam’iyyun adawa da ke shirin ƙalubalantar gwamnati mai mulki.

Jam’iyyar ta ce maimakon bunƙasa dimokaraɗiyya ta gaskiya, an kafa sabuwar jam’iyyar ne domin kawo cikas ga haɗin kai tsakanin ƴan adawa.

Sai dai jam’iyyar APC ta musanta zargin, inda ta ce ba ta da hannu wajen kafa jam’iyyar NDC, tare da ƙoƙarin wanke kanta daga zarge-zargen da ADC ke yi.

11/05/2026

Allah ya karawa Annabi Muhammad S.A.W Daraja

YANZU-YANZU: Masu neman takarar Sanatan Kano ta tsakiya sun janye wa Shekarau'Yan takarkarun Kano ta tsakiya na jam’iyar...
10/05/2026

YANZU-YANZU: Masu neman takarar Sanatan Kano ta tsakiya sun janye wa Shekarau

'Yan takarkarun Kano ta tsakiya na jam’iyar APC sun janyewa tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim shekarau domin tsayawa takarar sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyar APC ta jihar Kano kamar yadda Daily Nigerian Hausa ta rawaito.

DA DUMI-DUMI: Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya umarci magoya bayansa da su fice daga jam’iyyar PDP ...
10/05/2026

DA DUMI-DUMI: Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, ya umarci magoya bayansa da su fice daga jam’iyyar PDP tare da komawa jam’iyyar APC.

Me za ku ce?

Kamfanin dillancin labaran IRIB na Iran ya bayar da rahoton cewa, kwamandan sojojin kasar Ali Abdullahi ya ziyarci jagor...
10/05/2026

Kamfanin dillancin labaran IRIB na Iran ya bayar da rahoton cewa, kwamandan sojojin kasar Ali Abdullahi ya ziyarci jagoran addini Mojtaba Khamenei. Ya kara da cewa Khamenei ya yaba wa dakarun kasar tare da bayyana ci gaba da daukar matakan kare mutuncin Iran."

Amnesty ta ƙaddamar da bincike kan rikicin siyasa da daba a KanoƘungiyar kare haƙƙin bil Adama ta Amnesty International ...
10/05/2026

Amnesty ta ƙaddamar da bincike kan rikicin siyasa da daba a Kano

Ƙungiyar kare haƙƙin bil Adama ta Amnesty International ta sanar da fara bincike da sauraron bayanan jama’a kan yawaitar rikice-rikicen siyasa da ayyukan ‘yan daba a Jihar Kano bayan kashe-kashen da s**a faru a Kano da Gwarzo.

A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta bayyana cewa hare-haren da ake zargin ‘yan daba masu alaƙa da siyasa sun kai, sun yi sanadin mutuwar aƙalla mutum biyar a ranar 5 ga Mayun 2026.

Daraktan Amnesty International a Najeriya, Isa Sanusi, ya ce ayyukan ‘yan daba na barazana ga zaman lafiya da haƙƙin jama’a a Kano, yana mai cewa mutane na rayuwa cikin fargaba saboda tashin hankalin.

Ƙungiyar ta buƙaci jama’a, ƙungiyoyin farar hula da iyalan waɗanda abin ya shafa su bayar da bayanai domin gano masu hannu da kuma ‘yan siyasar da ake zargin suna ɗaukar nauyin rikicin.

Amnesty ta kuma gargadi cewa ci gaba da rikicin siyasa da amfani da ‘yan daba na iya kawo cikas ga dimokuraɗiyya da hana jama’a shiga harkokin siyasa cikin walwala, tare da kira ga hukumomi da jam’iyyun siyasa su mutunta doka da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Zaben Gwaji:Bari Muga Waye Zaiyi NasaraMuje Zuwa........
10/05/2026

Zaben Gwaji:

Bari Muga Waye Zaiyi Nasara

Muje Zuwa........

Rikicin ADC: Bangaren Nafi'u Bala ya bukaci a dakatar da sayar da Fom din neman takaraBangaren jam’iyyar ADC karkashin j...
09/05/2026

Rikicin ADC: Bangaren Nafi'u Bala ya bukaci a dakatar da sayar da Fom din neman takara

Bangaren jam’iyyar ADC karkashin jagorancin Nafiu Bala ya bukaci shugabancin jam’iyyar da David Mark ke jagoranta da ta dakatar da sayar da fom din takara har sai an kammala shari’ar shugabanci da ke gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Sakataren kwamitin amintattu na ADC, Rufus Akanmi, ya bayyana cewa an cimma matsayar ne a taron kwamitin da aka gudanar ranar Alhamis, inda ya gargadi masu sayen fom cewa za su yi hakan ne bisa kasadarsu.

A wani bangare kuma, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja karkashin jagorancin Mai shari’a Emeka Nwite ta dage sauraron karar shugabancin jam’iyyar ba tare da sanya ranar ci gaba ba.

Lauyan masu karar ya bayyana cewa Kotun Koli ta yi watsi da karar daukaka kara da aka shigar kan lamarin, amma kuma ya nemi a mayar da shari’ar zuwa wani alkalin daban.

Sai dai lauyoyin bangaren David Mark sun soki matakin, suna zargin masu karar da kokarin jinkirta sauraron karar da kuma neman sauya alkali domin biyan bukatarsu.

Kotun ta ce ba za ta dauki mataki kan wasikar neman sauya alkalin ba tare da sauraron dukkan bangarorin da ke karar ba, kafin daga bisani ta dage shari’ar na wani lokaci mara kayyadewa.

ANA MAYAR DA YARAN MUSULMAI ZUWA KIRISTANCI A KANO!!!Ana tuhumar wani kirista Soja da Sace wata Yarinya budurwa Musulma ...
09/05/2026

ANA MAYAR DA YARAN MUSULMAI ZUWA KIRISTANCI A KANO!!!

Ana tuhumar wani kirista Soja da Sace wata Yarinya budurwa Musulma mai suna Amina a ƙaramar hukumar Tofa a Jihar Kano ya kai ta barikin Sojoji na Janguza ya ajiye ta har tsawon Shekaru biyu

Iyayen budurwar tun bayan ɓatan ta s**ai ta neman ta amma ba su gan ta ba su ka haƙura s**ai ta yin addu'ah har zuwa Shekaru biyu

Kwatsam wata rana sai ga Yarinya Amina ta fito daga barikin Soja za ta yi Cefane sai 'Ƴan garinsu s**a gan ta nan s**a je s**a faɗawa Iyayeta su kuma Iyayen sai s**a je s**a faɗawa Hukumar Hisba

Hukumar Hisba ta shiga fafutuka har s**a karɓo budurwa Amina ta dawo gida amma kwananta ɗaya sai Sojan ya kuma zuwa ya kira ta ya koma da ita cikin Bariki nan ma Hukumar Hisba da Iyayenta s**a yi ƙoƙari s**a ƙarɓota bayan wani Capting ɗin Soja ya saka baki

Wannan dai Sojan ya kuma dawowa ya kuma ɗauke Amina ya Chanja mata addini ya mayar da ita kirista sannan ya Chanja mata suna ya ajiyeta a ɗakinsa a bariki

Bayan fitar Labarin a Shekaranjiya sai Hankalin Jami'an Soja ya tashi Saboda tsoron abinda ka iya faruwa Sai jiya s**a ɗauko Amina s**a dawo da ita wajen Iyayena ta hannun Hukumar Hisba

Muna fatan Shugannin gidan Soja za su ja hankain wannan Sojan a kan ya fita Sabgar Amina Ya ƙyalewa Iyayenta 'Ƴar su ya barta ta yi addinin ta na Musulunci ya cire Son ta daga zuciyarta

Allah Ya tsare mu Ya tsare mana zuri'ah da yin kafurci bayan musulnci.

Abbas Adamu - 9 - 5 - 2026 -

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kokiya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share