13/08/2026
IRAN TA ƘARA KAIFI: Jami’in Soji Ya Ce Za Ta Kai Hari Fiye Da Da A Duk Wani Yaƙi Na Gaba
Wani babban jami’in sojin Iran ya ce ƙasar za ta ɗauki matakin kai hari fiye da na baya idan aka sake samun wani yaƙi a nan gaba.
Ya ce Iran tana shirye-shiryen fuskantar ko wane irin yanayi, kuma za ta mayar da martani mai ƙarfi idan aka sake kai mata hari.
Wannan furuci na zuwa ne yayin da ake ci gaba da samun zazzafar takaddama tsakanin Iran da Amurka, musamman kan Mashigar Hormuz.
Shin wannan gargadi ne kawai, ko kuwa Iran tana shirin sabon mataki idan aka sake barkewar yaƙi?