31/07/2025
Bayan Saɓani Ya Shiga tsakani, Shugaba Tinubu Ya Gana da na Hannun Daman Kwankwaso
A ƴan kwanakin nan, fadar shugaban kasa ta yi magana kan jagoran NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a lokuta daban-daban
Hakan ya biyo bayan s**ar da tsohon gwamnan Kano, Kwankwaso ya yiwa gwamnatin Bola Tinubu, inda ya ce tana fifita Kudu kan Arewa
Sai dai a ranar Laraba, ɗaya daga cikin waɗanda ake ganin na hannun daman Kwankwaso ne, Hon. Abdulmumin Kofa ya gana da Tinubu a sirrance
Shugaba Bola Tinubu ya gana da Hon. Abdulmumin Jibrin, ɗaya daga cikin abokan siyasa na jagoran NNPP na ƙasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
Hon. Abdulmumini, wanda ke wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji a Majalisar Wakilai ta Tarayya daga jihar Kano ya ziyarci Tinubu a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja ranar Laraba.
Ɗan Majalisar Tarayya na daga cikin masu biyayya ga tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Kwankwaso, kamar yadda Vanguard ta rahoto.
Abdulmumini Kofa ya amsa tambayoyin manema labarai jim kaɗan bayan ganawar sirri da Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Abdulmumini Kofa na shirin shiga APC?
Da aka tambaye shi ko yana shirin komawa APC ne, ɗan Majalisar ya bayar da amsa a nutse, yana mai cewa ba abin da ba zai iya faruwa ba.
"Ina ga lokacin wannan batun bai yi ba, amma dai komai na iya faruwa.
Abu mafi muhimmanci shi ne zaman lafiya da haɗin kan ƙasar nan. Kuma na yi imani cewa idan muka kai ga gabar, za mu tsallaka.”
Dan majalisar ya ce ziyarar da ya kai wa Shugaban Ƙasa ba abin mamaki ba ne idan aka yi la’akari da abokantaka mai tsawo tsakanin Tinubu da Kwankwaso.
Meyasa Kofa ya ziyarci Shugaba Tinubu?
“Na zo ne domin ganin Shugaban Ƙasa, kuma kamar yadda aka sani, akwai alaƙa tsakanin Tinubu da jagoranmu na NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.
"Saboda haka, ban ga abin mamaki ba dan na zo gaida shi, na duba lafiyarsa, da kuma tattauna wasu batutuwan ƙasa da nake ganin suna da amfani ga al’ummar Najeriya.” - Abdulmumini Kofa.
Kofa ya taɓo alaƙar Ƙwankwaso da Tinubu
Da aka tambaye shi ko ziyarar tasa tana da nasaba da wani yunkurin sulhu tsakanin Kwankwaos da fadar shugaban ƙasa, Jibrin ya ce dukkan shugabannin biyu suna da kishin ci gaban ƙasa duk da suna da banbancin ra'ayi.
A baya-bayan nan, Kwankwaso ya zargi gwamnatin Tinubu da fifita yankin Kudu a rabon ayyukan ababen more rayuwa.
Sai dai Abdulmumini Jibrin ya ce: “To, dukkansu manyan ‘yan siyasa ne, Shugaban Ƙasa babban ɗan siyasa ne, haka jagoranmu na NNPP, ina da yakinin cewa suna da kishin zaman lafiya, haɗin kai da cigaban Najeriya.."
Fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da ganawar Hon. Kofa da shugaba Tinubu a wani bidiyo da Dada Olusegun ya wallafa a shafinsa na X.