30/05/2026
Zaben Fidda Gwanin Jihar Adamawa da Aka Yi Ba Zabe Ba Ne Na Di Ne
Rikici da rashin jituwa sun kara tsananta a cikin Jam’iyyar NDC reshen jihar Adamawa, bayan gudanar da zaben fidda gwani da ya haifar da korafe-korafe daga wasu mambobin jam’iyyar da s**a bayyana rashin gamsuwa da yadda aka tafiyar da zaben.
Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun fara nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwanin ‘yan takarar kujerun Majalisar Jiha, Majalisar Tarayya, Majalisar Dattawa, Gwamna da kuma Shugaban Kasa.
Korafe-korafen dai na kunshe ne cikin wata wasika da ko-odinetan Jam’iyyar NDC na karamar hukumar Yola, Hon. Catherine M. Jatau, ya aikewa da Jaridar Al-Kiblah a ranar Juma’a 29 ga watan Mayun 2026.
A cikin wasikar, Jatau ya bayyana cewa ba su amince da sahihancin zaben fidda gwanin da aka gudanar ba, yana mai zargin cewa an gudanar da zaben cikin rashin gaskiya da karya ka’idojin dimokuradiyya.
“A cewar sanarwar da aka bayar, an ce za a fara zabe da karfe 11 na safe, amma abin mamaki sai aka fara kada kuri’a tun kafin lokacin da aka tsara. Wannan lamari ba dimokuradiyya ba ne, illa fyade ne ga tsarin dimokuradiyya,” k**ar yadda ya bayyana a cikin wasikar.
Ya kara da cewa yadda aka gudanar da zaben ya nuna karara akwai rashin adalci, zamba da kuma rashin gaskiya daga wasu da s**a jagoranci tsarin zaben.
Hakazalika, ya yi zargin cewa daya daga cikin masu neman takara yana ci gaba da rike mukamin sakataren jam’iyyar yayin da yake shiga takara, abin da ya ce ya saba wa dokoki da ka’idojin jam’iyyar.
“Mun gudanar da zabe ne tare da wanda har yanzu yake rike da mukamin sakataren jam’iyya, alhali ka’idojin doka ya tanadi cewa dole ne ya sauka daga mukaminsa kafin shiga takara,” in ji wasikar.
Jatau ya ce ya rubuta wasikar ne a madadin mambobin jam’iyyar da dama da ke nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben, yana mai gargadin cewa rashin daukar mataki kan lamarin na iya janyo rabuwar kai da rikici a cikin jam’iyyar.
Daga karshe, ya yi kira ga shugabannin Jam’iyyar NDC a matakin jiha da na kasa da su gaggauta shiga tsakani tare da gudanar da bincike mai zaman kansa domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar jam’iyyar.
Ya kuma bukaci uwar jam’iyyar da ta dauki matakin gaggawa domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da hadin kai tsakanin mambobinta a jihar Adamawa.