Jaridar Alkiblah

Jaridar Alkiblah •Jaridar Al-Kiblah... (Mahangar Al'umma) Jarida ce da aka Samar da ita a Harshen Hausa Domin Kawo Muku Sahihan labarai.
(1)

30/05/2026

"Gaskiya ne, Akwai Masu Baiwa Gwamna Shawara da Kawai Munafurci S**a Sanya a Gaba, Sama da Ci Gaban Kano" SSA Panshekara

Da Dumi-Dumi; Liverpool Ta Raba Gari Da Arne Slot Bayan Gaza Kare Kambun Gasar FirimiyaA wani mataki da ya girgiza duniy...
30/05/2026

Da Dumi-Dumi; Liverpool Ta Raba Gari Da Arne Slot Bayan Gaza Kare Kambun Gasar Firimiya

A wani mataki da ya girgiza duniyar ƙwallon ƙafa, rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Liverpool ta raba gari da mai horas da 'yan wasanta, Arne Slot, bayan kakar wasa mai cike da takaici wadda ta hana ƙungiyar kare kambun gasar Premier League da ta lashe a bara.

Rahoton ya ce Liverpool ta yanke wannan hukunci ne bayan kammala kakar wasa a matsayi ta biyar a teburin gasar, lamarin da ya sa ta kasa yin gogayya mai ƙarfi wajen sake lashe kofin Firimiya k**ar yadda magoya bayanta s**a yi fata tun farkon kakar wasan.

Wannan mataki ya kawo ƙarshen zaman Arne Slot a filin Anfield cikin gaggawa, duk da cewa ya yi fice a kakar wasarsa ta farko inda ya jagoranci Liverpool zuwa lashe kambun Firimiya a karon farko da ya fara aiki da ƙungiyar bayan tafiyar tsohon kocinta mai dogon tarihi, Jurgen Klopp.

Nasarar da Slot ya samu a kakarsa ta farko ta sa magoya baya da masu sharhi s**a yi hasashen cewa zai iya gina sabuwar daular Liverpool bayan zamanin Klopp.

Sai dai sak**akon da ƙungiyar ta samu a kakar wasa ta biyu ya gaza cika waɗannan tsammani, inda Reds s**a kasa nuna ƙwarin da ya kai su ga kambun gasar a shekarar da ta gabata.

Har yanzu babu cikakken bayani kan wanda zai maye gurbin Slot, amma ana sa ran shugabannin Liverpool za su fara neman sabon koci da zai dawo da ƙungiyar kan turbar nasara tare da dawo da ita cikin masu fafatawa da kambun Firimiya a kakar wasa mai zuwa.

Wannan labari na ci gaba da jan hankalin masoya ƙwallon ƙafa a faɗin duniya, yayin da ake jiran ƙarin bayani daga mahukuntan Liverpool kan makomar ƙungiyar bayan wannan babban sauyi.

'Yan Sanda Sun Rufe Hanyoyin Zuwa Wajen Taron Tabbatar Da Jonathan A Matsayin Dan Takarar PDPJami’an ‘yan sanda sun to s...
30/05/2026

'Yan Sanda Sun Rufe Hanyoyin Zuwa Wajen Taron Tabbatar Da Jonathan A Matsayin Dan Takarar PDP

Jami’an ‘yan sanda sun to she hanyoyin da ke kaiwa cibiyar taron da wani bangare na jam’iyyar PDP ke shirin gudanarwa domin amincewa da tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben 2027.

Jaridar TheCable ta rawaito cewa, bangaren PDP karkashin jagorancin Kabiru Tanimu Turaki ya shirya gudanar da taron ne a Abuja, duk da adawar da ake yi da bangaren ministan Abuja, Nyesom Wike, ke marawa baya.

Matakin ya biyo bayan umarnin Hukumar Babban Birnin Tarayya (FCTA) da ta bukaci cibiyoyin taruka su yi hulda ne kawai da shugabannin jam’iyyun da INEC ta amince da su.

Sakataren yada labarai na bangaren Turaki, Ini Ememobong, ya ce sun cika dukkan sharuddan gudanar da taron kuma za su ci gaba da shirinsu k**ar yadda aka tsara tun farko.

Sai dai rahotanni sun nuna cewa an sauya wurin taron zuwa wani wuri a Area 10 da ke Abuja bayan kulle hanyoyin zuwa wurin da aka fara warewa.

An Sauya Alkalin Da Zai Saurari Karar Kalubalantar Shugabancin ADCBabban alkalin kotun tarayya ya sauya alkalin da zai s...
30/05/2026

An Sauya Alkalin Da Zai Saurari Karar Kalubalantar Shugabancin ADC

Babban alkalin kotun tarayya ya sauya alkalin da zai saurari karar da tsohon Mataimakin Shugaban Jam’iyyar ADC na kasa, Nafiu Bala, ya shigar yana kalubalantar shugabancin jam’iyyar karkashin jagorancin David Mark.

Inda tuni aka mayar da karar ga Alkalin Kotun Tarayya, Peter Lifu, domin ci gaba da shari’ar.

Nafiu Bala dai na neman kotu ta hana David Mark, Rauf Aregbesola da sauran mambobin kwamitin rikon kwarya na jam’iyyar gudanar da harkokin shugabanci, yana mai cewa nadin nasu ya saba wa kundin tsarin mulkin ADC da kuma Dokar Zabe.

Kazalika a cikin karar an hada da jam’iyyar ADC, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC da tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, cikin wadanda ake kara.

Sauyin alkalin ya biyo bayan umarnin da kotun ƙoli ta bayar na a gaggauta sauraron karar a Kotun Tarayya.

A baya dai, lauyoyin wadanda ake kara sun soki bukatar sauya alkalin, suna zargin mai karar da kokarin neman kotun da za ta fi masa anfani.

Bayan takaddamar, tsohon alkalin shari’ar, Emeka Nwite, ya dage sauraron karar har sai an samu cikakken kwafin hukuncin Kotun Koli.

Zaben Fidda Gwanin Jihar Adamawa da Aka Yi Ba Zabe Ba Ne Na Di Ne Rikici da rashin jituwa sun kara tsananta a cikin Jam’...
30/05/2026

Zaben Fidda Gwanin Jihar Adamawa da Aka Yi Ba Zabe Ba Ne Na Di Ne

Rikici da rashin jituwa sun kara tsananta a cikin Jam’iyyar NDC reshen jihar Adamawa, bayan gudanar da zaben fidda gwani da ya haifar da korafe-korafe daga wasu mambobin jam’iyyar da s**a bayyana rashin gamsuwa da yadda aka tafiyar da zaben.

Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun fara nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwanin ‘yan takarar kujerun Majalisar Jiha, Majalisar Tarayya, Majalisar Dattawa, Gwamna da kuma Shugaban Kasa.

Korafe-korafen dai na kunshe ne cikin wata wasika da ko-odinetan Jam’iyyar NDC na karamar hukumar Yola, Hon. Catherine M. Jatau, ya aikewa da Jaridar Al-Kiblah a ranar Juma’a 29 ga watan Mayun 2026.

A cikin wasikar, Jatau ya bayyana cewa ba su amince da sahihancin zaben fidda gwanin da aka gudanar ba, yana mai zargin cewa an gudanar da zaben cikin rashin gaskiya da karya ka’idojin dimokuradiyya.

“A cewar sanarwar da aka bayar, an ce za a fara zabe da karfe 11 na safe, amma abin mamaki sai aka fara kada kuri’a tun kafin lokacin da aka tsara. Wannan lamari ba dimokuradiyya ba ne, illa fyade ne ga tsarin dimokuradiyya,” k**ar yadda ya bayyana a cikin wasikar.

Ya kara da cewa yadda aka gudanar da zaben ya nuna karara akwai rashin adalci, zamba da kuma rashin gaskiya daga wasu da s**a jagoranci tsarin zaben.

Hakazalika, ya yi zargin cewa daya daga cikin masu neman takara yana ci gaba da rike mukamin sakataren jam’iyyar yayin da yake shiga takara, abin da ya ce ya saba wa dokoki da ka’idojin jam’iyyar.

“Mun gudanar da zabe ne tare da wanda har yanzu yake rike da mukamin sakataren jam’iyya, alhali ka’idojin doka ya tanadi cewa dole ne ya sauka daga mukaminsa kafin shiga takara,” in ji wasikar.

Jatau ya ce ya rubuta wasikar ne a madadin mambobin jam’iyyar da dama da ke nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben, yana mai gargadin cewa rashin daukar mataki kan lamarin na iya janyo rabuwar kai da rikici a cikin jam’iyyar.

Daga karshe, ya yi kira ga shugabannin Jam’iyyar NDC a matakin jiha da na kasa da su gaggauta shiga tsakani tare da gudanar da bincike mai zaman kansa domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar jam’iyyar.

Ya kuma bukaci uwar jam’iyyar da ta dauki matakin gaggawa domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da hadin kai tsakanin mambobinta a jihar Adamawa.

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana jin daɗinsa kan yadda jihohin Najeriya ba sa fama da matsalar biyan albashi...
30/05/2026

Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana jin daɗinsa kan yadda jihohin Najeriya ba sa fama da matsalar biyan albashin ma’aikata k**ar yadda lamarin yake a baya kafin hawansa mulki.

Tinubu ya yi wannan bayani ne a ranar Juma’a a Legas lokacin da ya karɓi tawagar Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ƙarƙashin jagorancin Kashim Shettima, waɗanda s**a kai masa ziyarar gaisuwar Sallah.

Shugaban ƙasar ya ce sauye-sauyen da gwamnatinsa ta aiwatar sun taimaka wajen ƙara kuɗaɗen shiga na jihohi, lamarin da ya sauƙaƙa musu wajen cika muhimman alhakin da s**a rataya a wuyansu, ciki har da biyan albashin ma’aikata a kan lokaci.

Me za ku ce?

Hukumar Kashe Gobara A Kano Ta Tabbatar da Mutuwar Mutane Uku Sak**akon Faɗawa RijiyaLamarin dai ya faru a Samegu da ke ...
29/05/2026

Hukumar Kashe Gobara A Kano Ta Tabbatar da Mutuwar Mutane Uku Sak**akon Faɗawa Rijiya

Lamarin dai ya faru a Samegu da ke ƙaramar hukumar Kumbotso inda wani mutum mai shekaru 40 ya faɗa rijiyar sai kuma ƙauyen Madarin Taba da ke ƙaramar hukumar Warawa a nan kuma mutane biyu su ka faɗa rijiyar.

Maimagana da yawun hukumar Saminu Yusuf Abdullahi ya ce su na ci gaba da bincike don gano dalilin faruwar lamarin.

"Irin lalatar da ake kawo mana Kano, mutane suna ganin muna da Gwamna mai hakuri, kowa zai yi abinda ya ga dama. Nasiha ...
29/05/2026

"Irin lalatar da ake kawo mana Kano, mutane suna ganin muna da Gwamna mai hakuri, kowa zai yi abinda ya ga dama. Nasiha ta gare ka, a matsayin ɗan uwa, ka tashi ka faɗa wa mutane akwai gwamnati" - Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II

Rikici Ya Kunno Kai a NDC Bayan Zaben Fidda Gwani a AdamawaRikici da rashin jituwa sun kara tsananta a cikin Jam’iyyar N...
29/05/2026

Rikici Ya Kunno Kai a NDC Bayan Zaben Fidda Gwani a Adamawa

Rikici da rashin jituwa sun kara tsananta a cikin Jam’iyyar NDC reshen jihar Adamawa, bayan gudanar da zaben fidda gwani da ya haifar da korafe-korafe daga wasu mambobin jam’iyyar da s**a bayyana rashin gamsuwa da yadda aka tafiyar da zaben.

Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun fara nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben fidda gwanin ‘yan takarar kujerun Majalisar Jiha, Majalisar Tarayya, Majalisar Dattawa, Gwamna da kuma Shugaban Kasa.

Korafe-korafen dai na kunshe ne cikin wata wasika da ko-odinetan Jam’iyyar NDC na karamar hukumar Yola, Hon. Catherine M. Jatau, ya aikewa da Jaridar Al-Kiblah a ranar Juma’a 29 ga watan Mayun 2026.

A cikin wasikar, Jatau ya bayyana cewa ba su amince da sahihancin zaben fidda gwanin da aka gudanar ba, yana mai zargin cewa an gudanar da zaben cikin rashin gaskiya da karya ka’idojin dimokuradiyya.

“A cewar sanarwar da aka bayar, an ce za a fara zabe da karfe 11 na safe, amma abin mamaki sai aka fara kada kuri’a tun kafin lokacin da aka tsara. Wannan lamari ba dimokuradiyya ba ne, illa fyade ne ga tsarin dimokuradiyya,” k**ar yadda ya bayyana a cikin wasikar.

Ya kara da cewa yadda aka gudanar da zaben ya nuna karara akwai rashin adalci, zamba da kuma rashin gaskiya daga wasu da s**a jagoranci tsarin zaben.

Hakazalika, ya yi zargin cewa daya daga cikin masu neman takara yana ci gaba da rike mukamin sakataren jam’iyyar yayin da yake shiga zaben, abin da ya ce ya saba wa dokoki da ka’idojin jam’iyyar.

“Mun gudanar da zabe ne tare da wanda har yanzu yake rike da mukamin sakataren jam’iyya, alhali ka’idoji da doka ya tanadi cewa dole ne ya sauka daga mukaminsa kafin shiga takara,” in ji wasikar.

Jatau ya ce ya rubuta wasikar ne a madadin mambobin jam’iyyar da dama da ke nuna damuwa kan yadda aka gudanar da zaben, yana mai gargadin cewa rashin daukar mataki kan lamarin na iya janyo rabuwar kai da rikici a cikin jam’iyyar.

Daga karshe, ya yi kira ga shugabannin Jam’iyyar NDC a matakin jiha da na kasa da su gaggauta shiga tsakani tare da gudanar da bincike mai zaman kansa domin tabbatar da adalci da kuma kare martabar jam’iyyar.

Ya kuma bukaci uwar jam’iyyar da ta dauki matakin gaggawa domin tabbatar da dorewar zaman lafiya da hadin kai tsakanin mambobinta a jihar Adamawa.

Zafafan Hotuna daga wajen Hawan Nassarawa a Jihar Kano.Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif ne ya karbi sarkin da tawagarsa a g...
29/05/2026

Zafafan Hotuna daga wajen Hawan Nassarawa a Jihar Kano.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusif ne ya karbi sarkin da tawagarsa a gidan gwamnatin Jiha.

Shugaban Hukumar Kula da Gandun Daji na birnin Dhaka a Bangladesh, Rafiqul Islam Talukder, ya ce sun dauki matakin kai d...
29/05/2026

Shugaban Hukumar Kula da Gandun Daji na birnin Dhaka a Bangladesh, Rafiqul Islam Talukder, ya ce sun dauki matakin kai dabbar gidan Zoo bisa amincewar gwamnati.

Hotunan Saniyar ya karade shafukan sada zumunta a ciki da wajen kasar, sak**akon k**a da yanayin fuskar Shugaban Amurka..

Address

Guda Abdullahi Street Farm Center Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Alkiblah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Alkiblah:

Share