Jaridar Alkiblah

Jaridar Alkiblah •Jaridar Al-Kiblah... (Mahangar Al'umma) Jarida ce da aka Samar da ita a Harshen Hausa Domin Kawo Muku Sahihan labarai.

Moroko ta yi waje da Najeriya a AFCON ta 2026 bayan bugun daga kai sai mai tsaron gida.Kasashen biyu sun tashi wasa 0-0 ...
14/01/2026

Moroko ta yi waje da Najeriya a AFCON ta 2026 bayan bugun daga kai sai mai tsaron gida.

Kasashen biyu sun tashi wasa 0-0 bayan fafatawa ta tsawon mintuna 120.

Tawagar ta Moroko za ta kara da Senegal a wasan final a ranar Lahadi yayin da Najeriya za ta fafata da Masar a wasan neman matsayi na uku na gasar.

African CAF: Moroco ta Lallasa Najeriya a Bugun daga kai sai mai tsaron gida Najeriya na da ci 2 a ya yin da Morocco ta ...
14/01/2026

African CAF: Moroco ta Lallasa Najeriya a Bugun daga kai sai mai tsaron gida

Najeriya na da ci 2 a ya yin da Morocco ta zura kwallaye 4 a Bugun daga kai sai mai tsaron gida.

Morocco zata kara da Senegal a wasan karshe

Gwamnan Kano Abba Gida-Gida  Ba Ya Buƙatar Goyon Bayan Kwankwaso Don Shiga APC --- NNPPJam'iyyar NNPP ta ce Gwamna Abba ...
14/01/2026

Gwamnan Kano Abba Gida-Gida Ba Ya Buƙatar Goyon Bayan Kwankwaso Don Shiga APC --- NNPP

Jam'iyyar NNPP ta ce Gwamna Abba Yusuf na Kano ba ya buƙatar amincewar Sanata Rabiu Kwankwaso don shiga APC ko wata jam'iyyar da ya zaɓa.

Komawar Abba zuwa APC Ta Kankama, Zai Haɗu da Ganduje da Jiga Jigan APC a KanoMajiyoyi sun bayyana cewa Gwamnan Kano, Ab...
14/01/2026

Komawar Abba zuwa APC Ta Kankama, Zai Haɗu da Ganduje da Jiga Jigan APC a Kano

Majiyoyi sun bayyana cewa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, zai gana da Ganduje domin share fagen sauya sheƙa zuwa APC

An ce taron zai haɗa manyan shugabannin APC a Kano, ciki har da Sanata Barau Jibrin, domin kammala shirin sauya sheƙar gwamnan da magoya bayansa

Rahotanni sun nuna an ƙara tsaro a Gidan Gwamnatin Kano sakamakon tashin hankali tsakanin Kwankwasiyya da wasu ƙungiyoyin da ke goyon bayan gwamna

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ana sa ran zai gana da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje.

Wannan haduwar na zuwa ne gabanin sauya sheƙarsa daga NNPP zuwa jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya.

Abba Kabir zai gana da Abdullahi Ganduje

Wannan bayani ya fito ne daga Muhammad Garba, babban sakatare ga Ganduje yayin wata tattaunawa a gidan rediyo, cewar The Sun.

Garba ya ce taron zai buɗe hanya ga sauya sheƙar gwamnan, inda manyan shugabannin APC za su halarta domin cimma matsaya ta ƙarshe.

Ya bayyana cewa Sanata Barau Jibrin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, da shugaban APC na Kano, Abdullahi Abbas, za su halarci taron.

'Zuwan Abba Kabir zai karfafa APC'

A cewarsa, sauya sheƙar gwamnan da magoya bayansa zai taimaka wajen ƙarfafa jam’iyyar ta fuskar rajistar mambobi masu inganci.

Garba ya ce zuwan Abba Kabir zai ƙara ƙarfin APC wajen tunkarar zaɓe a faɗin ƙasar nan, ta hanyar gina sahihiyar rumbun bayanan mambobi.

Ya ƙara da cewa aikin rajistar APC zai ƙarfafa tasirin jam’iyyar, bisa dogon tarihin biyayya da tsari da take da shi a Kano.

An kuma shawarci mambobin jam’iyyar APC da su zauna lafiya tare da goyon bayan ajandar “Renewed Hope” ta Shugaba Bola Tinubu.

Ajandar na mai da hankali kan bunƙasa tattalin arziki da walwalar jama’a, inda aka jaddada cewa haɗin kai na siyasa yana da muhimmanci.

A halin da ake ciki, an ƙara tsaurara tsaro a Gidan Gwamnatin Kano saboda tashin hankalin siyasa da ake fuskanta.

An jibge motocin sulke guda biyu da tankin ruwan zafi a bakin ƙofar Gidan Gwamnatin Jihar Kano domin tabbatar da zaman lafiya.

Haka kuma, an ga ƙarin jami’an tsaro masu makamai, musamman daga hukumar DSS, suna sintiri a harabar gidan gwamnati.

Rahotanni sun nuna cewa ƙarin tsaron na da alaƙa da rikicin da ke ƙaruwa tsakanin Kwankwasiyya da wasu ƙungiyoyin magoya bayan gwamna.

An Dakatar da Likitoci kan Barin Almakashi a Cikin Matar Aure yayin Tiyata a KanoHukumar kula da asibitocin Kano ta tabb...
14/01/2026

An Dakatar da Likitoci kan Barin Almakashi a Cikin Matar Aure yayin Tiyata a Kano

Hukumar kula da asibitocin Kano ta tabbatar da cewa barin almakashi a ciki ya kai ga mutuwar Aishatu Umar bayan tiyata a asibitin Abubakar Imam Urology

Rahotanni sun nuna cewa an dakatar da ma’aikata uku da ake zargi da hannu a lamarin, tare da mika batun ga kwamitin ladabtar da likitoci na jihar Kano

Baya ga dakatar da jami'an, hukumar ta yi alkawarin daukar tsauraran matakai domin hana sake faruwar irin wannan kuskure a asibitocin gwamnati a nan gaba

Hukumar kula da asibitocin jihar Kano ta tabbatar da cewa batun barin almakashi a cikin maras lafiya, Aishatu Umar ya faru a asibitin Abubakar Imam Urology.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a yammacin ranar Talata, inda ta ce binciken farko da aka gudanar ya tabbatar da sahihancin faruwar lamarin a wannan cibiya ta lafiya.

Sanarwar da hadimin gwamnan Kano, Ibrahim Adam ya wallafa a Facebook ta jaddada cewa an dauki matakin ne bisa umarnin babban sakataren hukumar, Dr. Mansur Mudi Nagoda.

An bar almakashi a ciki bayan tiyata

A cewar sanarwar, binciken da aka yi cikin gaskiya ya tabbatar da cewa marigayiya Aishatu Umar ta fuskanci matsala bayan wata tiyata da aka yi mata a asibitin Abubakar Imam Urology Centre.

Majiyar mu ta rahoto cewa bincike ya zo ne bayan zargin da iyalanta s**a yi cewa an yi sakacin barin almakashi a cikinta a lokacin tiyatar da aka mata.

Hukumar ta ce ta dakatar da ma’aikata uku da aka gano suna da alaka kai tsaye da lamarin daga duk wani aikin jinya da asibiti, nan take.

Matakin dakatarwar, a cewar hukumar, na wucin gadi ne har sai an kammala cikakken bincike, kuma an dauke shi a matsayin mataki na farko wajen kare martabar sana’ar likitanci da lafiyar marasa lafiya.

An mika lamarin ga kwamitin ladabtarwa

Hukumar ta kuma bayyana cewa ta mika lamarin ga Kwamitin Ladabtar da Likitoci na Jihar Kano domin ci gaba da bincike da daukar matakan hukunci idan an tabbatar da laifi.

Ana sa ran cewa wannan mataki zai tabbatar da cewa duk wani hukunci da za a dauka ya yi daidai da dokoki, ka’idojin sana’a, da kuma dabi’un aikin likitanci.

Sakon ta’aziyya da alkawarin gyara

Hukumar ta mika sakon ta’aziyyarta ga iyalan marigayiya Aishatu Umar, tana mai bayyana alhininta kan irin wannan rashi mai radadi.

Har ila yau, hukumar ta tabbatar wa al’ummar Kano cewa za ta kara karfafa tsarin sa ido a cikin asibitocin gwamnati tare da tabbatar da bin ka’idojin
sana’a yadda ya kamata.

Bayanin mijin matar da aka yi wa tiyata

A gefe guda kuma mijin Aishatu Abubakar da ta rasu bayan mata tiyata saboda barin almakashi a cikinta ya fito ya yi magana.

Mijin matar ya kara da cewa sun shafe watanni suna zuwa asibiti domin duba abin da ke damun matar ta shi amma ba a gano damuwarta ba.

Bayan shafe lokaci ne ya bayyana cewa sun ziyarci wasu asibitoci domin a duba lafiyar matar, a can ne kuma ya ce aka gano an bar almakashi a cikinta.

Mun samu labarin cewa a na takurawa chiyamomin ƙananan hukumomi da sauran masu riƙe da madafun iko kan cewa dole su saka...
13/01/2026

Mun samu labarin cewa a na takurawa chiyamomin ƙananan hukumomi da sauran masu riƙe da madafun iko kan cewa dole su saka hannu a takarda cewa Kwankwaso za su bi ko Ganduje --- Madugun Kwankwasiyya

Wata Uwar Ƴa'ya Biyar Ta Rasu Sakamakon Zargin Sakacin Likitoci a KanoWata mummunar annoba ta girgiza Jihar Kano bayan r...
13/01/2026

Wata Uwar Ƴa'ya Biyar Ta Rasu Sakamakon Zargin Sakacin Likitoci a Kano

Wata mummunar annoba ta girgiza Jihar Kano bayan rasuwar wata uwa mai ‘ya’ya biyar, Aishatu Umar, sakamakon zargin sakaci daga likitoci a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Abubakar Imam Urology Centre, mallakin gwamnati.

Rahotanni sun nuna cewa Aishatu Umar ta rasu ne bayan an yi mata tiyata, inda ake zargin an bar almakashi a cikin jikinta, lamarin da ya haddasa mata matsananciyar rashin lafiya har zuwa rasuwarta.

Iyalan marigayiyar sun bayyana lamarin a matsayin sakaci na likitoci, tare da kira ga hukumomi da su gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da adalci.

Baffa Babba 'Dan Agundi: Yadda Ganduje Ya So Kwankwaso Ya Jawo Abba zuwa APCTsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Gand...
13/01/2026

Baffa Babba 'Dan Agundi: Yadda Ganduje Ya So Kwankwaso Ya Jawo Abba zuwa APC

Tsohon Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya nuna ɓacin ransa kan kalaman da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi a kansa

Duk da haka, Ganduje ya bayyana cewa APC na maraba da lale da yiwuwar dawowar Gwamna Abba Kabir Yusuf cikin ikon jam’iyya mai mulki a matakin kasa

Makusancin tsohon Gwamnan, Alhaji Baffa Babba 'Dan Agundi ne ya tabbatar da haka a yayin da ake zaman jiran sauya shaƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf

Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana rashin jin daɗinsa kan wasu kalamai da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi a kansa.

Tsohon Gwamnan na Kano ya bayyana kalaman da cewa ba su dace ba, kuma masu tayar da hankali ne a yayin da maganar sauya sheƙa Gwamna Abba Kabir Yusuf ke kara kwari.

Wannan bayani ya fito ne daga makusancin Ganduje, Dakta Baffa Babba Dan’agundi, yayin da yake zantawa da manema labarai wanda kuma aka wallafa a shafin Facebook na DC Hausa.

Kalaman Rabiu Kwankwaso sun damu Abdullahi Ganduje

A cewar Baffa Babba 'Dan Agundi, Ganduje ne da kansa ya bayyana masa yadda kalaman s**a dame shi matuƙa, kuma bai ji dadinsu ba.

Ya ce: “Dr. Ganduje ya shaida min cewa bai ji daɗi ko kaɗan da kalaman da Sanata Kwankwaso ya yi a kansa ba."

'Dan Agundi ya bayyana cewa Ganduje ya zargi Sanata Kwankwaso da kiransa da suna makiyi a gaban magoya bayansa.

Ya ce hakan ya faru ne a lokacin da Kwankwaso ke zargin Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da shirin ƙwace iko da wasu hukumomin gwamnati domin amfani da su kan abokan hamayyarsa na siyasa.

Ya ce: “Ganduje ya bayyana min cewa irin waɗannan kalamai ba su dace ba, musamman a wannan lokaci da Jihar Kano ke buƙatar haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba na bai ɗaya.

APC na maraba da Gwamna Abba Gida Gida

Sannan Ya ƙara da cewa Ganduje ya yi imanin cewa yiwuwar dawowar Gwamna Abba Kabir Yusuf jam’iyyar APC ya kamata ta zama dama ta sulhu da haɗin gwiwa a tsakanin manyan ‘yan siyasar jihar, ba sabani da ƙarin rikici ba.

Ya ce: “A fahimtar Ganduje, dawowar Gwamnan Kano APC ya kamata ta zama wata hanya da za a haɗu, a manta da banbance-banbance, a mayar da hankali kan ciyar da Kano gaba."

Dakta Ganduje ya kuma jaddada cewa, la’akari da shekarunsu da gogewarsu a siyasa, shi da Sanata Kwankwaso ya kamata su rika taka rawar dattawan ƙasa, maimakon ci gaba da rikicin siyasa.

Ya ce: “Ya yi imanin babu dalilin ci gaba da saɓani, domin dukkanninsu sun kai matakin da ba su da wata babbar buƙata ta siyasa, tunda sun kammala iyakar wa’adin rike muƙaman zaɓe."

Da yake magana kan rahoton dawowar Gwamna Abba Kabir Yusuf APC, Dan’agundi ya bayyana hakan a matsayin abin farin ciki da ƙarfafawa ga jam’iyyar APC a Kano.

Ya ƙara da cewa shirye-shiryen tarbar Gwamnan a hukumance sun yi nisa, ya kuma yi addu’ar Allah Ya kawo zaman lafiya da haɗin kai a Kano, tare da fatan dawowar Gwamna Abba APC za ta haifar da ci gaba mai ɗorewa.

Zaben 2027: Ana Neman Tinubu Ya Dawo da Nasir El Rufa'i cikin Jam'iyyar APCWani tsohon ɗan takarar gwamna a Kebbi ya nem...
13/01/2026

Zaben 2027: Ana Neman Tinubu Ya Dawo da Nasir El Rufa'i cikin Jam'iyyar APC

Wani tsohon ɗan takarar gwamna a Kebbi ya nemi Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gaggauta shawo kan Nasir El-Rufai ya koma APC

Ya ce sauye-sauyen siyasa a Arewa maso Yamma sun bar shugaban ƙasa ba tare da manyan abokai masu ƙarfi ba a yankin

Malam Salihu Isa Nataro ya yi nuni da cewa dawowar Nasir El-Rufai na iya ƙarfafa tasirin APC da tara ƙuri’u a zaben 2027 da ke tafe

Wani jigo a jam’iyyar APC a jihar Kebbi, Malam Salihu Isa Nataro, ya yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya ɗauki mataki cikin gaggawa domin dawo da Nasir el-Rufai cikin jam’iyyar APC.

Nataro, wanda ya taɓa tsayawa takarar gwamna a Kebbi a ƙarƙashin APC, ya bayyana cewa yanayin siyasar Arewa maso Yamma na bukatar matakan gaggawa domin ƙarfafar shugaban ƙasa a yankin.

Jaridar The Guardian ta rahoto ya ce bayan sauke Dr Abdullahi Umar Ganduje daga shugabancin APC, yankin Arewa maso Yamma ya rasa wani babban ginshiƙi da ke iya jan ragamar goyon bayan Tinubu.

Dalilan kiran dawo da Nasir El-Rufai APC

Nataro ya bayyana cewa sake daidaita ƙungiyoyin siyasa a Arewa na nuna cewa dole ne Shugaba Tinubu ya ɗauki Arewa maso Yamma da muhimmanci fiye da da.

Ya ce babu wani jigo mai ƙarfi a yankin da ke da cikakken tasiri wajen tara ƙuri’u ga shugaban ƙasa, lamarin da ke buƙatar dawo da El-Rufai domin cike wannan gibi.

A cewarsa, El-Rufai na da tasiri sosai a tsakanin masu ruwa da tsaki a Arewa maso Yamma, kuma hakan na iya taimaka wa APC wajen shawo kan ƙalubalen siyasa da ke tafe.

Maganar Nataro kan Rabiu Kwankwaso

Nataro ya ce ya kamata rade-radin da ke yawo kan yiwuwar Rabiu Musa Kwankwaso shiga sabuwar haɗaka a ƙarƙashin jam’iyyar ADC ya tayar da hankalin duk masu goyon bayan Shugaba Tinubu.

Ya ƙara da cewa ko da gwamnan Kano na yanzu, Abba Yusuf, ya shiga APC, hakan kaɗai ba zai wadatar wajen cike gibi a yankin ba.

A ra’ayinsa, akwai buƙatar mutum mai tasiri da kwarewa wajen tsara dabarun siyasa a Arewa maso Yamma, wanda ya ce El-Rufai ne ya fi dacewa da wannan rawar.

Nataro ya daura alhakin nesanta El-Rufai daga jikin Tinubu kan wasu ‘yan siyasa masu hassada da masu adawa cigabansa.

Tasirin dawowar El-Rufai ga Tinubu

Nataro ya ce akwai gagarumin aiki da ke gaban APC wajen tallata Shugaba Tinubu a Arewa maso Yamma kafin zaben 2027.

Daily Post ta wallafa cewa ya bayyana cewa El-Rufai na da kwarewa da ƙarfin hali da za su ba shi damar jagorantar wannan aiki cikin nasara.

Ana Shirin Sakin Ƴan Ta'adda 70, Sun Laftawa Manoma a Kano da Katsina HarajiYan bindiga sun ƙara sako manoma a gaba inda...
13/01/2026

Ana Shirin Sakin Ƴan Ta'adda 70, Sun Laftawa Manoma a Kano da Katsina Haraji

Yan bindiga sun ƙara sako manoma a gaba inda s**a yanka masu harajin girbin N50,000 kan kowace eka a Kano da Katsina

Manoma na fuskantar barazana idan s**a ki biyan kuɗin da ya haɗa da lalata masu amfanin gona da kai masu munanan hare-hare

Wannan na zuwa a yayin da gwamnatin jihar Katsina ta kammala shirin sakin mutane 70 da ake zargi da alaƙa da ’yan bindiga

Rahotanni sun nuna cewa ƙungiyoyin ’yan bindiga da ke aiki a wasu sassan jihohin Kano da Katsina na tilasta wa manoma biyan harajin noma kafin girbi amfanin gonakinsu.

A yanzu haka, ƴan ta'addan na karɓar N50,000 kan kowacce eka daga manoman rake, lamarin ya shafi harkar manoman masara.

Jaridar The Guardian ta wallafa cewa ana zargin cewa waɗannan ƙungiyoyi sun kafa wata hanya ta mulki mai zaman kanta a muhimman dazuzzuka na yankin.

Rahotanni sun tabbatar da cewa a waɗannan wurare ne ƴan ta'addan ke karɓar kuɗin haraji tare da tsoratar da al’umma.

Yan ta'adda na karban haraji kan wuraren manoma

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa bincike ya nuna cewa ’yan bindigan sun kafa sansani a dajin Rugu da ke ƙaramar hukumar Faskari a Katsina, da kuma dajin Falgore a ƙaramar hukumar Doguwa ta Kano.

A waɗannan wurare, suna karɓar abin da s**a kira “harajin gona” daga manoma, tare da yin barazana ga duk wanda ya ƙi bin umarninsu na biyan kuɗin

Rahoton ya nuna cewa manoman da s**a ƙi biyan harajin na fuskantar tsoratarwa, ana lalata amfanin gonarsu, har ma da yi musu barazanar kai hari.

Wannan lamari ya tilasta wa manoma da dama barin gonakinsu gaba ɗaya, lamarin da ke barazana ga samar da abinci a yankin da Arewacin Najeriya.

Yan ta'adda na cin karensu babu babbaka

Manoman rake su ne s**a fi shan wahala a halin yanzu, sai dai manoman masara ma na cikin wadanda ke fuskantar muzgunar mutanen.

Rahotanni sun ce waɗannan dazuzzuka na cikin muhimman yankin samar da abinci tsakanin jihohin Kano da Katsina.

Wannan yankin na samar da rake da masara zuwa manyan kasuwanni irin su Kasuwar Dawanau a Kano da ake fitar wa ɓangarori da dama na duniya.

Duk da kasancewar wuraren bincike da shingayen sojoji da ’yan sanda a titin Falgore, rahoton ya nuna cewa ’yan bindigan na aiki a kilomita biyar kacal daga wuraren shingen tsaro.

Wasu mazauna yankunan da manoma sun bayyana halin da ake ciki a matsayin karɓe iko a hankali, inda ’yan bindiga ke kafa dokoki, tare da mallakar harkokin tattalin arzikin yau da kullum ba tare da wata turjiya ba.

Zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga gwamnatocin jihohin da abin ya shafa ko kuma hukumomin tsaro ba.

Sauya Sheka:Yadda aka kara jibge karin jami’an tsaro a gidan gwamnatin KanoAn jibge jami’an tsaro a gidan Gwamnatin Kano...
12/01/2026

Sauya Sheka:Yadda aka kara jibge karin jami’an tsaro a gidan gwamnatin Kano

An jibge jami’an tsaro a gidan Gwamnatin Kano ya yin da gwamna Abba ke shirin sauya sheƙa zuwa APC

An tsaurara tsaro a gidan gwamnatin Jihar Kano a ranar Litinin, biyo bayan rahotannin da ke nuni da shirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na ficewa daga jam’iyyarsa ta NNPP zuwa APC.

Jaridar Daily Trust ta lura da tarin jami’an tsaro daga rundunar ‘yan sandan Najeriya da kuma hukumar tsaron farin kaya (DSS) a babbar kofar shiga gidan gwamnatin.

Duk da cewa ba a tabbatar da shirin ficewar a hukumance ba, amma bayanai na nuni da cewa gwamnan zai sauya sheka daga yanzu zuwa kowanne lokaci.

Majiyar mu ta lura cewa akalla motocin tsaro masu sulke na ‘yan sanda da DSS sun kasance a muhimman wurare, ciki har da babbar kofar shiga da kuma zagayen hanya da ke kaiwa gidan gwamnatin.

An jibge motocin yaƙi tare da tsaurara matakan tsaro a Gidan Gwamnatin Kano a yayin da ake dakon sauya sheƙar Gwamna Abb...
12/01/2026

An jibge motocin yaƙi tare da tsaurara matakan tsaro a Gidan Gwamnatin Kano a yayin da ake dakon sauya sheƙar Gwamna Abba Kabir Yusuf daga Jam'iyyar NNPP zuwa APC.

Address

Guda Abdullahi Street Farm Center Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Alkiblah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Alkiblah:

Share