Jaridar Alkiblah

Jaridar Alkiblah •Jaridar Al-Kiblah... (Mahangar Al'umma) Jarida ce da aka Samar da ita a Harshen Hausa Domin Kawo Muku Sahihan labarai.

Babbar Alƙaliyar Najeriya Ta Haramta Amfani da Lakabin “Barrister” a Gaban SunaBabbar Alƙaliyar Najeriya (CJN), Mai Shar...
31/07/2026

Babbar Alƙaliyar Najeriya Ta Haramta Amfani da Lakabin “Barrister” a Gaban Suna

Babbar Alƙaliyar Najeriya (CJN), Mai Shari'a Kudirat Kekere-Ekun, ta ba da umarnin dakatar da amfani da lakabin “Barrister” a matsayin abin da ake sanyawa a gaban sunayen lauyoyi a duk wata mu'amala ta hukuma da ta shafi Kotun Ƙolin Najeriya.

Umarnin, wanda ya fara aiki nan take, ya shafi lauyoyi, ma'aikatan shari'a da masu rajistar kotu.

An bayyana cewa amfani da lakabin “Barrister” a gaban suna bai dace ba, kuma ya saɓa da ƙa'idodin ƙwarewa da ɗabi'ar aikin shari'a da ake buƙata a Kotun Ƙoli.

Sabon umarnin ya kuma tanadi cewa a daina amfani da lakabin a cikin wasiƙun hukuma, takardu, bayanan kotu, katunan shaida da duk wasu mu'amalolin hukuma da s**a shafi Kotun Ƙoli, tare da umartar shugabannin sassa su tabbatar da cikakken bin wannan doka.

Kotu ta yanke wa wata budurwa hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan Yari saboda yanke al'aurar saurayinta Babbar kotun ...
31/07/2026

Kotu ta yanke wa wata budurwa hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan Yari saboda yanke al'aurar saurayinta

Babbar kotun jihar Ekiti da ke zamanta a Ado-Ekiti ta yanke wa wata mata mai suna Joy Ikoja mai shekaru 35 hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari bayan samunta da laifin yanke gaban saurayinta, Ibrahim Usman.

An gurfanar da Ikoja ne kan tuhume-tuhume biyu da s**a hada da yunkurin kisa da kuma haddasa munanan raunuka, bayan wani rikici da ya faru a ranar 12 ga watan Afrilun shekarar 2025.

Kotun ta ji cewa Ikoja ta k**a saurayinta tare da wata kawarta a daki, lamarin da ya haddasa rikici inda ake zarginta da murde masa al'aura, wanda ya janyo masa mummunan rauni har aka garzaya da shi asibiti domin ceto rayuwarsa.

A yayin shari'ar, masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu hudu da hujjoji da s**a hada da rahoton likita da bayanan binciken 'yan sanda.

Sai dai wacce ake tuhuma ta musanta aikata laifin tare da cewa ba ta jikkata saurayin nata ba.

A hukuncin da Mai Shari'a Oyinkansola Oluboyede ta yanke, kotun ta wanke Ikoja daga zargin yunkurin kisa saboda rashin isassun hujjojin da ke nuna niyyar kashe wanda abin ya shafa. Sai dai kotun ta same ta da laifin haddasa munanan raunuka, tare da yanke mata hukuncin daurin shekaru bakwai a gidan yari.

Gwamna Abba Gida-Gida ya Taya Sarkin Kano Sanusi Ii Murnar Cika Shekaru 65Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya ...
31/07/2026

Gwamna Abba Gida-Gida ya Taya Sarkin Kano Sanusi Ii Murnar Cika Shekaru 65

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya taya Sarkin Kano, Khalifa Muhammadu Sanusi II, murnar cika shekaru 65 da haihuwa.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun sa, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ranar Juma’a, gwamnan ya bayyana Sarkin a matsayin jagora mai hangen nesa, hikima, jarumtaka da kishin tabbatar da adalci.

Gwamna Yusuf ya yaba da irin gudunmawar da Sarkin ya bayar wajen gina kasa, bunkasa ilimi da tattalin arziki, da kuma kare al’adu da addinin Kano.

Kazalika ya kuma ce tsawon shekarun da Sarkin ya yi yana hidima ga al’umma sun sanya ya samu karbuwa a Najeriya da kuma kasashen duniya.

Gwamnan ya yaba da kokarin Sarkin wajen inganta zaman lafiya, hadin kai da shugabanci nagari, tare da bayar da muhimmanci ga ilimi, tallafa wa mata da matasa, ci gaba mai dorewa da sauye-sauyen tattalin arziki.

Ya ce jagorancin Sarkin ya kasance abin koyi da kuma hasken fata da ci gaba ga al’ummar Kano da sauran sassan kasa.

Gwamna Yusuf ya yi addu’ar Allah Ya ba Sarkin lafiya, tsawon rai da karin hikima domin ci gaba da jagorantar Masarautar Kano da bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar da kasa baki daya.

Haka kuma, gwamnan ya sake tabbatar da aniyarsa ta ci gaba da aiki kafada da kafada da masarautar gargajiya wajen aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su inganta rayuwar al’umma da kuma kara daukaka matsayin Kano.

NNPCL ya Ɗauki Sama Da Ma'aikata 1,000.Kamfanin Man Fetur na Ƙasa NNPCL ya ɗauki matasa ƙwararru sama da 1,000 aiki a ci...
31/07/2026

NNPCL ya Ɗauki Sama Da Ma'aikata 1,000.

Kamfanin Man Fetur na Ƙasa NNPCL ya ɗauki matasa ƙwararru sama da 1,000 aiki a cikin ma’aikatansa bayan sun kammala shirin horo na tsawon shekara guda, wanda ya haɗa da ƴan internship, horo mai zurfi da kuma wanda aka tantance ƙwarewar su.

Babban Jami’in Gudanarwa na NNPC Ltd, Bayo Ojulari, ne ya bayyana hakan a cikin wani saƙo da ya wallafa a shafukan kamfanin na sada zumunta, inda ya bayyana wannan mataki a matsayin wani babban ci gaba ga kamfanin mai na ƙasa.

A cewar Ojulari, sabbin ma’aikatan da aka ɗauka sun fito ne bayan sun tsallake duk wani gwaji da tsarin zaɓe wanda ya haɗa da aikin horaswa, horo na musamman da kuma tantance yadda s**a gudanar da aikinsu.

Fittaciyar Mawakiyar Tyla ta cire Lagos daga jerin rangadin kide-kidantaMawaƙiyar Afirka ta Kudu, Tyla, ta cire Jihar  L...
31/07/2026

Fittaciyar Mawakiyar Tyla ta cire Lagos daga jerin rangadin kide-kidanta

Mawaƙiyar Afirka ta Kudu, Tyla, ta cire Jihar Lagos daga jerin wuraren da za ta ziyarta domin gudanar da wakokinta da kide-kide na APOP World Tour.

An dauki wannan matakin ne bayan wasu ‘yan Najeriya sun yi kira da a kaurace wa kide-kidanta sak**akon sabbin hare-haren kyamar baki da ake kai wa ‘yan Najeriya a Afirka ta Kudu.

Duk da cire Lagos, sauran wuraren da aka tsara gudanar da kide-kiden a Turai, Arewacin Amurka da Afirka ta Kudu sun ci gaba da kasancewa a jadawalin rangadin.

Ghana ta Amince Da Ƙudurin Tsawaita Wa'adin Mulkin Shugaban ƘasaGwamnatin Ghana ta amince da wani kudiri na yin gyaran K...
31/07/2026

Ghana ta Amince Da Ƙudurin Tsawaita Wa'adin Mulkin Shugaban Ƙasa

Gwamnatin Ghana ta amince da wani kudiri na yin gyaran Kundin Tsarin Mulkin ƙasar domin tsawaita wa'adin mulkin shugaban ƙasa daga shekara huɗu zuwa shekara biyar.

An kuma rage mafi ƙarancin shekarun da ake buƙata ga ɗan takarar shugaban ƙasa daga shekara 40 zuwa shekara 35.

An samar da waɗannan shawarwarin gyaran ne bayan wani kwamitin da Shugaba John Mahama ya kafa a bara ya gudanar da nazari kan Kundin Tsarin Mulkin shekarar 1992.

Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari'a, Dominic Ayine, ya sanar da cewa gwamnati ta amince da shawarwarin kwamitin.

Gwamnatin Kano Ta Gargaɗi Asibitoci: Ba Za Mu Lamunci Wasa da Rayukan Jama'a baGwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ba z...
30/07/2026

Gwamnatin Kano Ta Gargaɗi Asibitoci: Ba Za Mu Lamunci Wasa da Rayukan Jama'a ba

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa ba za ta lamunci duk wani sakaci da zai iya jefa rayuwar al'umma cikin haɗari ba, tare da jaddada aniyarta ta ƙarfafa sa ido kan ayyukan cibiyoyin lafiya masu zaman kansu.

Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, ne ya bayyana hakan yayin wani taron horaswa da Hukumar Private Health Institutions Management Agency (PHIMA) ta shirya wa mamallakan asibitoci masu zaman kansu, shugabanninsu da jami'an tattara bayanan lafiya na ƙananan hukumomi.

Dakta Labaran ya nuna damuwa kan yadda wasu asibitoci masu zaman kansu ba sa miƙa bayanan ayyukansu ga gwamnati, lamarin da ke hana shigar da su cikin babban rumbun bayanan lafiya na jihar da na ƙasa.

A cewarsa, kimanin kashi 35 cikin 100 na al'ummar Jihar Kano na neman kulawar lafiya ne a asibitoci masu zaman kansu, saboda haka wajibi ne waɗannan cibiyoyi su bi ƙa'idojin gwamnati wajen tattarawa da miƙa bayanan marasa lafiya.

Ya jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta zuba ido tana kallon duk wanda ya kafa asibiti yana gudanar da ayyukansa ba tare da bin ƙa'idoji ba, yana mai cewa kare rayuka da inganta ayyukan kiwon lafiya na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatin jihar ta sa a gaba.

> "Ko da mutum ya kashe kuɗi mai yawa wajen gina ko kafa asibiti, gwamnati ba za ta ƙyale shi ya yi wasa da rayukan jama'a ko ya karya ƙa'idojin aikin lafiya ba," in ji Kwamishinan.

Ya kuma buƙaci dukkan asibitoci masu zaman kansu da su haɗa kai da gwamnati wajen samar da sahihan bayanan lafiya, domin inganta tsare-tsare da manufofin da s**a shafi lafiyar al'umma a jihar Kano.

"Ku Sauka Idan Ba Za Ku Iya Tallata Tinubu ba a 2027" --- Shugaban APC Ya Gargaɗi Masu Muƙaman SiyasaShugaban Jam'iyyar ...
30/07/2026

"Ku Sauka Idan Ba Za Ku Iya Tallata Tinubu ba a 2027" --- Shugaban APC Ya Gargaɗi Masu Muƙaman Siyasa

Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya gargaɗi masu riƙe da muƙaman siyasa a gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, musamman waɗanda ake kira technocrats, da su sauka daga muƙamansu idan ba za su iya mara wa jam'iyyar baya a shirye-shiryen zaɓen 2027 ba.

Yilwatda ya bayyana hakan ne a Abuja yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki na jam'iyyar, inda ya ce duk wanda ya samu muƙami a ƙarƙashin gwamnatin APC yana da alhakin kare manufofin gwamnati da kuma bayyana nasarorin da ta samu ga al'umma.

A cewarsa, ba za a yi amfani da sunan technocrat a matsayin uzuri na guje wa ayyukan siyasa ba, yana mai cewa duk wanda ba zai iya tallata manufofin gwamnatin Shugaba Tinubu da na jam'iyyar APC ba, ya k**ata ya yi murabus domin a ba wa wanda zai iya yin hakan damar riƙe muƙamin.

> "Duk wanda ba zai iya tallata jam'iyyar APC da manufofin gwamnatin Shugaba Tinubu ba, ya k**ata ya sauka daga muƙaminsa domin a ba wa wani damar da zai taimaka wa jam'iyyar," in ji Yilwatda.

Shugaban na APC ya kuma yi kira ga duk masu riƙe da muƙamai na siyasa da su ƙara kusantar jama'a, su riƙa bayyana ayyukan da gwamnatin Tinubu ke aiwatarwa, yana mai cewa hakan na da muhimmanci wajen neman goyon bayan al'umma gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

Kalaman nasa na zuwa ne ya yin da jam'iyyar APC ta fara ƙara ƙaimi wajen shirye-shiryen tunkarar zaɓukan shekarar 2027, tare da ƙarfafa haɗin kai tsakanin shugabanninta da masu riƙe da muƙamai a gwamnatin tarayya.

Hankula Sun Tashi; Ana Tsaka Da Zaman Shari'a, 'Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Kotun Shari'ar Musulunci Rahotanni daga Jiha...
30/07/2026

Hankula Sun Tashi; Ana Tsaka Da Zaman Shari'a, 'Yan Bindiga Sun Kutsa Cikin Kotun Shari'ar Musulunci

Rahotanni daga Jihar Katsina sun ce wasu 'yan bindiga sun kutsa cikin wata Kotun Shari'ar Musulunci ya yin da ake tsaka da zaman shari'a, inda s**a riƙa harbe-harbe tare da tambayar inda alƙalin kotun yake.

Majiyoyi daga yankin sun shaida cewa lamarin ya haifar da ruɗani a harabar kotun, inda alkalai, lauyoyi da sauran mutanen da ke wurin s**a nemi mafaka domin tsira.

A cewar majiyoyin, alƙalin kotun ya samu damar tserewa ta wata taga da ke jikin ginin kotun kafin maharan su isa inda yake, lamarin da ya sa s**a kasa cimma shi.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a tabbatar da samun asarar rayuka ko jikkata ba.

Haka kuma, Rundunar 'Yan Sandan Jihar Katsina da mahukuntan shari'a ba su fitar da wata sanarwa kan lamarin ba.

'Dan Shekara 18 Ya Kafa Tarihi a Matsayin Farfesa Mafi Ƙarancin Shekaru a Duniya Nathan Thomas ya zama farfesa mafi ƙara...
30/07/2026

'Dan Shekara 18 Ya Kafa Tarihi a Matsayin Farfesa Mafi Ƙarancin Shekaru a Duniya

Nathan Thomas ya zama farfesa mafi ƙarancin shekaru a duniya bayan ya fara koyarwa yana da shekaru 18 kacal a kwalejin Miami Dade

Matashin ya kammala digirin farko da na biyu a fannin Injiniyan Lantarki kafin ya fara aiki, abin da ya sa ya shiga kundin tarihin duniya

Yanzu haka dai Nathan na koyarwa tare da karantar digirin lauya, yana shirin ƙwarewa a dokokin kare haƙƙin fasaha da kirkire-kirkire

A lokacin da ɗalibai matasa s**a shiga ajin koyon shirye-shiryen kwamfuta a Miami Dade College a watan Agustan 2023, sun yi mamakin ganin cewa wanda zai koya musu darasin yana kusan shekarunsu.

Duk da haka, Nathan Thomas ya tsaya a gaban ajin cikin ƙwarewa, yana koyar da darussan da ya kware a kansu tun yana ƙarami.

Wannan na kunshe ne a cikin rahoton da aka wallafa a shafin kundin tarihi na duniya, watau Guinness World Records.

Nathan, wanda aka haifa a ranar 9 ga Satumba, 2004 a Amurka, ya fara shiga kwalejin Miami Dade tun yana da shekara 10 ta hanyar tsarin haɗa karatun sakandare da jami'a.

Daga baya ya koma jami'ar kasa da kasa ta Florida yana da shekara 14 domin ci gaba da karatunsa.

Tun kafin ya kai shekarun da mafi yawan matasa ke shiga jami'a, Nathan ya riga ya samu digirin farko da na biyu a fannin Injiniyan Lantarki, dukkansu tare da sak**akon girmamawa.

Bayan kammala karatunsa, Nathan ya koma Miami Dade College a matsayin malami.

A ranar da ya fara koyarwa yana da shekaru 18 da kwanaki 346, ya zama farfesa mafi ƙarancin shekaru a duniya, inda ya karya tarihin da Colin Maclaurin ya riƙe tsawon fiye da shekaru 300.

Haka kuma, ya fi Alia Sabur ƙarancin shekaru da kwanaki 16 lokacin da ita ma ta kafa tarihin farfesa mafi ƙarancin shekaru a shekarar 2008.

Shekaru ba su hana koyarwa ba

Nathan ya ce bai taɓa damuwa da kasancewarsa ƙarami ba, domin manufar kowa a aji ita ce koyon ilimi.

“Da zarar ka shiga aji, duk wanda yake wurin ya zo ne domin ya koya. Shekaru ba su da muhimmanci idan ana maganar ilimi,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa abin da ya fi mayar da hankali a kai shi ne taimaka wa ɗalibai su fahimci darasi da kuma ƙarfafa masu ƙoƙarin koyo.

Nathan ya bayyana cewa tun yana yaro yake son karatu, musamman fannin kimiyya da fasaha (STEM), domin lissafi shi ne darasin da ya fi fahimta.

Kasancewar iyayensa injiniyoyi ya taimaka wajen gina sha'awarsa tun yana ƙarami.

Yanzu yana karantar lauya Bayan kafa tarihi a fannin koyarwa, Nathan bai tsaya ba.

Yanzu yana koyar da darussa ta yanar gizo tare da karantar digirin lauya a jami'ar koyon lauyanci ta Miami, inda yake sa ran kammala karatunsa a shekarar 2028.

Ya bayyana cewa burinsa shi ne ya ƙware a fannin dokokin kare haƙƙin fasaha da kirkire-kirkire, domin ya haɗa ilimin injiniya da na shari'a wajen taimaka wa masu ƙirƙira da masana fasaha.

Address

Guda Abdullahi Street Farm Center Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Alkiblah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Alkiblah:

Shortcuts

Share