Jaridar Alkiblah

Jaridar Alkiblah •Jaridar Al-Kiblah... (Mahangar Al'umma) Jarida ce da aka Samar da ita a Harshen Hausa Domin Kawo Muku Sahihan labarai.

Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo Ya Jagoranci Taron Lafiya, Ya Bada Kayan AikiDaga: Abbas Yakubu Yaura Shugaban Karamar H...
02/10/2025

Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo Ya Jagoranci Taron Lafiya, Ya Bada Kayan Aiki

Daga: Abbas Yakubu Yaura

Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Hon. Dakta Mani Tsoho (PhD), yau Alhamis ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki kan harkokin lafiya a karamar hukumar Gwarzo.

Taron, wanda ya haɗa shugabanni, ma’aikatan lafiya, da sauran manyan masu ruwa da tsaki, ya mayar da hankali kan inganta walwalar jama’a da tabbatar da cewa al’umma suna samun ingantattun ayyukan lafiya.

A wani gagarumin mataki na tallafa wa sashen lafiya, Shugaban ya sayawa motar Ambulance ta Asibitin Gwarzo sabbin tayoyi tare da wasu kayayyakin aikin lafiya domin ƙara sauƙaƙa ayyuka da kuma inganta hidimar jinya ga marasa lafiya.

Dakta Mani Tsoho ya jaddada cewa lafiya ita ce ginshikin ci gaban al’umma, don haka gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da zuba jari wajen kyautata asibitoci da samar da kayan aikin zamani domin sauƙaƙa wa jama’a.

Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da haɗa kai da gwamnati wajen kare lafiyar jama’a da tsaftace muhalli domin tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga kowa da kowa.

Najeriya @65: Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo Ya Taya Gwamna Abba Kabir  Murnar Cika Shekaru 65 Da Samun ‘Yancin KaiA ya...
01/10/2025

Najeriya @65: Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo Ya Taya Gwamna Abba Kabir Murnar Cika Shekaru 65 Da Samun ‘Yancin Kai

A yayin da Najeriya ke bikin cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai, Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Hon. Dakta Mani Tsoho, ya aike da sakon taya murna ga Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, al’ummar Gwarzo da kuma daukacin al’ummar Najeriya baki ɗaya.

Dakta Mani Tsoho ya bayyana wannan ranar ta zagayowar tunawa da samun ‘yancin kai a matsayin rana ta tarihi, ta tunani, hadin kai da sabon fata ga al’umma, inda ya jaddada cewa juriyar ‘yan Najeriya da jajircewar su sune tushen ci gaban kasa.

Haka zalika, ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa ingantaccen shugabanci da manufofin jin kai da yake aiwatarwa, wadanda s**a kasance alheri da ci gaba ga jama’a, musamman ma al’ummar Karamar Hukumar Gwarzo.

“Yau muna murnar cika shekaru 65 da samun ‘yancin kai. Ya kamata mu tuna da sadaukarwar da magabatanmu s**a yi wajen kafa kasa, tare da sabunta kudurinmu na gina Najeriya mai wadata, dunkulalliya, da zaman lafiya.

"A madadin Majalisar Karamar Hukumar Gwarzo, ina taya Gwamnanmu mai kishin kasa, al’ummar Gwarzo, Jihar Kano da daukacin al’ummar Najeriya murnar wannan rana mai tarihi. Allah Ya albarkaci Najeriya, Ya ba mu makoma mai haske,” in ji shi.

Shugaban ya yi kira ga al’ummar Gwarzo da su ci gaba da mara wa manufofin gwamnati baya tare da dagewa wajen tabbatar da zaman lafiya, hadin kai da kishin kasa domin amfanin kowa.

Ikon Alla: An Haife Jariri Mai Fuska 2, Ido 4 a Jihar BauchiWata mata a Bauchi ta haifi jariri mai fuska biyu da kai gud...
01/10/2025

Ikon Alla: An Haife Jariri Mai Fuska 2, Ido 4 a Jihar Bauchi

Wata mata a Bauchi ta haifi jariri mai fuska biyu da kai guda, abin da ya dauki hankalin al'umma saboda ganin wani bakon al'amari

An yi wa matar mai suna Hannatu tiyata kyauta a babban asibitin Azare, inda likitoci s**a tabbatar da cewa wannan jariri yana da bakin siffofi

Iyayen jaririn sun roki gwamnati da al'umma da su tallafa musu saboda rashin hali da bukatar kulawa ta musamman da yaron zai bukata

A wani lamari mai cike da al'ajabi, wata mata mai suna Hannatu, da ke zaune a kauyen Magonshi, ta haifi jariri mai fuska biyu da kai guda daya.

Allah Ya sauke ta lafiya lau a babban asibitin gwamnatin jihar Bauchi da ke Azare, inda likitoci su ka ce ba kasafai ake ganin irin wannan haihuwa ba.

A hira da Mijin Hannatu, Malam Bala Sa’idu, ya yi da jaridar Aminiya, ya bayyana cewa lamarin wani mu’ujiza ne daga Allah SWT.

Bauchi: Abin da iyayen jaririn ke cewa

Malam Bala Sa’idu, ya ce duk da cewa jaririn bai zo da kamanni na yau da kullum ba da aka saba gani ba, sun karɓi lamarin da hannu biyu da yardar Allah.

A cewarsa, matarsa ta raini cikin har na tsawon makonni 42, wanda ya zarce lokacin haihuwa na al’ada da jama'a su ka sani.

Ya gode wa babban likitan asibitin, Dr. Bello Idris, wanda ya jagoranci tiyatar haihuwar ba tare da karɓar ko sisin kwabo ba.

Malam Bala ya roki gwamnatin jihar Bauchi da kungiyoyin agaji su taimaka masu ganin an ceto lafiyar jaririn, kasancewar su ba su da halin biyan kuɗin kula da lafiyarsa a gaba.

Likitocin Bauchi sun yi mamaki

Dr. Bello Idris, babban likitan da ya jagoranci tiyatar, ya bayyana cewa a duk tsawon shekarunsa a aikin likitanci, bai taba ganin irin wannan yanayi ba.

Ya ce samun irin wannan jariri yana faruwa ne sau daya cikin mutum miliyan 10, kuma sun jinjina al'amarin sosai.

Dr. Bello Idris, ce jaririn na da kai daya, fuska biyu, idanu hudu, hanci biyu, baki biyu, kunne biyu, hannaye biyu da ƙafafu biyu.

Sai dai duka baki biyu da ya ke da su sun zo a tsage, saboda haka ana shan wahala wajen shayar da shi yadda ya kamata.

Dr. Idris ya bayyana cewa bayan mahaifiyar ta samu sauki, za a tura su zuwa Babban Asibitin Koyarwa na Tarayya (FUHSTA) da ke Azare domin ci gaba da duba lafiyar jaririn da gudanar da bincike kan yanayinsa.

Da Dumi-Dumi: Gwamnan Abba Kabir Ya Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Ya Kori Kwamishinan 'Yan Sandan KanoGwamnan Kano, Alhaji A...
01/10/2025

Da Dumi-Dumi: Gwamnan Abba Kabir Ya Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Ya Kori Kwamishinan 'Yan Sandan Kano

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabiru Yusuf, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da ya sauke kwamishinan ‘yan sandan jihar daga mukaminsa bisa zargin rashin da’a.

Jaridar Alkiblah ta rahoto cewa Gwamnan ya yi wannan kiran ne a ya yin bikin cikar Najeriya shekaru 65 da samun ‘yancin kai a ranar Laraba, a filin wasa na Sani Abacha dake kofar Mata.

Aiki Ya Jika; An Tsige Mataimakin Shugaban Makaranta Saboda Taɓa Wa Ɗaliba ƙirjiDaga: Abbas Yakubu Yaura An kori mataima...
30/09/2025

Aiki Ya Jika; An Tsige Mataimakin Shugaban Makaranta Saboda Taɓa Wa Ɗaliba ƙirji

Daga: Abbas Yakubu Yaura

An kori mataimakin shugaban makarantar sakadire ta Kwame Nkrumah da ke a Jami’ar Kimiyya da fasaha ta Kwame Nkrumah a kasar Ghana Charles Akwasi Aidoo, bayan wani bidiyo da ya bazu a shafukan sada zumunta da ke nuna yana taɓa wa wata ɗaliba mace ƙirjinta a wani wuri da ake ganin ofishinsa ne.

A cikin wani bidiyon mai tsawon dakika 16 da ɗalibar ta ɗauka, an ga Aidoo yana sanya kansa a kafadar ɗalibar.

Korar dai ta biyo bayan matakin da Hukumar Ilimi ta kasar Ghana (GES) ta dauka kan mataimakin Shugaban Makarantar.

A cikin wata sanarwa, hukumar ta ce: “Gwamnati, a cikin ƙudurinta na kare martabar aikin koyarwa da jin daɗi da kare lafiyar ɗalibai, ta cire mataimakin shugaban makarantar daga muƙaminsa.”

Haka kuma, hukumar ta ƙara da cewa: “Mun haramta wa Charles Akwasi Aidoo shiga makarantar ya yin da bincike ke gudana bisa ka’idojin hukumar.”

Sanarwar ta bayyana cewa hukumar za ta bi dukkan matakai na doka don tabbatar da cewa an hukunta shi bisa ga ka’idojinta.

Hukumar ta ƙara da cewa suna ƙin duk wani aiki da zai kawo barazana ga lafiya da mutunci da kuma jin daɗin ɗalibai.

Ba wannan ne karo na farko da hukumar ke ɗaukar mataki kan malamai ko shugabannin makarantu da s**a aikata “aikin rashin ɗa’a” ga ɗalibansu ba.

A watan Nuwambar shekarar 2018, hukumar ta kori malamai tara da wasu manyan ma’aikata a wasu makarantu sakamakon aikata batsa da rashin ɗa’a.

Wata Sabuwa; Mata Masu Zaman Kansu Zasu Fara Biyan Haraji -- Gwamnatin Tarayya Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za a fa...
30/09/2025

Wata Sabuwa; Mata Masu Zaman Kansu Zasu Fara Biyan Haraji -- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa za a fara karɓar haraji daga hannun mata masu zaman kansu da kuma sauran hanyoyin samun kuɗi, ba tare da la’akari da halal ko haram ba.

Shugaban kwamitin shugaban ƙasa kan manufofin kuɗi da gyaran dokokin haraji, Taiwo Oyedele, ne ya sanar da hakan a wani faifen bidiyo da ya wallafa a shafin X a ranar Litinin.

Ya ce duk wata hanya da ake samun kuɗi ta hanyar aiki ko sayar da kaya za ta kasance ƙarƙashin tsarin biyan haraji, kamar yadda Daily Nigerian ta rahoto.

A cewarsa, dokokin haraji ba sa tambaya ko hanyar samun kuɗi halal ce ko haram, abin da ake dubawa kawai shi ne samun kuɗi.

Sannan ya kawo misali da cewa idan wani ko wata tana yin karuwanci ko wani irin aiki da ake biya, to za a ɗauki haraji daga kuɗaɗen da aka samu.

Oyedele ya jaddada cewa manufar sabon tsarin ita ce tabbatar da cewa duk wanda ke da hanyar samun kuɗi yana biyan haraji cikin gaskiya da adalci.

Sai dai ya bayyana cewa kyaututtuka ko kuɗaɗen kulawa da ake aika wa ’yan uwa, abokai ko baƙi ba za a ɗauke su a matsayin abin da ake cire haraji a kai ba.

Ya ce "Wannan nau’in ba a ɗaukar sa a matsayin musayar kaya ko aiki, don haka yana ficewa daga tsarin biyan haraji.

Oyedele ya tabbatar da cewa matakin zai taimaka wajen tsabtace tsarin kuɗi da kuma kawo karin kudaden shiga ga gwamnati.

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Gudanar Da Fareti a Ranar Samun Ƴancin Kai Daga: Abbas Yakubu Yaura Gwamnatin tarayya ta bayya...
30/09/2025

Gwamnatin Tarayya Ta Soke Gudanar Da Fareti a Ranar Samun Ƴancin Kai

Daga: Abbas Yakubu Yaura

Gwamnatin tarayya ta bayyana soke faretin da
aka shirya gudanarwa domin murnar zagayowar cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yancin kai, a ranar Laraba, 1 ga watan Oktoba, 2025.

Sanarwar ta fito ne daga ofishin sakataren
gwamnatin tarayya a ranar Litinin.

A cewar sanarwar, wannan mataki ba zai rage darajar nmuhimmancin ranar ba, kasancewar
ita ce rana ta tarihi ga 'yan Najeriya baki daya.

Gwamnati ta kuma nemi afuwar al'umma kan
wannan canjin da aka yi a shirin bukukuwan.

Duk da soke faretin, sauran shirye -shiryen da
aka tsara domin bikin za su ci gaba kamar yadda aka tsara tun farko. Wannan ya hada da jawabin shugaban kasa ga al'umma, bukukuwan al'adu da kuma wasu taruka na
musamman.

Hakan na zuwa ne yayin da gwamnatin tarayya ta jaddada bukatar gudanar da bikin cike da natsuwa da kuma nuna hadin kai tsakanin al'umma.

An kuma yi kira ga 'yan kasa da su ci gaba da tunawa da darajar ranar da ta kafa harsashin dimokuradiyya da 'yancin kai a kasar.

Gwamnatin Kano Ta Kuduri Aniyar Samar Da Ruwan Fanfo A Unguwanni 10 A Karamar Hukumar GwarzoDaga: Abbas Yakubu Yaura Gwa...
27/09/2025

Gwamnatin Kano Ta Kuduri Aniyar Samar Da Ruwan Fanfo A Unguwanni 10 A Karamar Hukumar Gwarzo

Daga: Abbas Yakubu Yaura

Gwamnatin Jihar Kano, ta hannun Ma’aikatar Albarkatun Ruwa karkashin jagorancin Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Hon. Umar Haruna Doguwa, ta kaddamar da wani gagarumin shiri na samar da ruwan famfo ga unguwanni goma (10) a Karamar Hukumar Gwarzo.

Unguwannin da za su amfana sun haɗa da: Riji Tsauni,Kwarbai,Salihaw,Kakarya,Unguwar Dorawa.

Sauran sun hada da Unguwar Gaude,Riga/Buremawa,Kayyu,Daminawa,Kogon Kura.

Wajen yin aikin za a yi amfani da manyan bututun ruwan famfo da s**a ratsa daga tashoshin ruwa na Fada da Kusalla, wanda hakan zai sauƙaƙa haɗin ruwan zuwa wadannan unguwanni cikin hanzari.

A ranar Laraba, 24 ga watan Satumba, 2025, Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Hon. Umar Haruna Doguwa, ya tura injiniyoyi daga ma’aikatar domin gudanar da binciken fasaha da gwajin tazarar nisan da ke tsakanin bututun ruwa da unguwannin da za su amfana.

Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Hon. Dr. Mani Tsoho (PhD), wanda Sakatarensa na Karamar Hukuma, Hon. Sunusi Abdullahi Getso ya wakilta, ya tarbi injiniyoyin a madadinsa. Ya bayyana farin cikinsa tare da godiya ga Gwamnatin Kano bisa wannan gagarumin mataki na inganta jin daɗin rayuwar al’ummar Gwarzo.

Kazalika, Hakimin Riji, Alhaji Yusuf Riji, tare da shugabannin al’umma na Salihawa da Kakarya, da kuma malamai da dattawan yankunan da za su amfana, sun yi jinjina da godiya ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da Mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, bisa fifita al’ummominsu a cikin wannan muhimmin shiri na ci gaba.

Sun kuma yi addu’o’i domin samun nasarar aikin da kuma cigaban Jihar Kano baki ɗaya.

Yadda Kwankwaso zai Yi Alaka da Ganduje idan Ya Koma APC da Wasu Abubuwa 2Ana hasashen siyasar Kano za ta canza sosai id...
27/09/2025

Yadda Kwankwaso zai Yi Alaka da Ganduje idan Ya Koma APC da Wasu Abubuwa 2

Ana hasashen siyasar Kano za ta canza sosai idan Rabiu Musa Kwankwaso ya amince da komawa jam’iyyar APC mai mulki

Hakan na iya tayar da sabuwar dambarwa tsakaninsa da tsohon abokinsa kuma abokin hamayyarsa a yau, Abdullahi Umar Ganduje

Ana hasashen jam’iyyar NNPP da ke mulkin Kano na iya shiga cikin rikice-rikice masu tsanani har ma ta rasa tasiri gaba ɗaya

Siyasar jihar Kano na ci gaba da zama jigon tattaunawa a Najeriya sakamakon rade-radin yiwuwar komawar jagoran NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Kwankwaso, wanda aka shaida da samun dimbin mabiya a Kano, ya jagoranci nasarar NNPP a babban zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da sauran wakilai.

BBC Hausa ta hada wani rahoto kan abubuwa da ake hasashen za su iya faruwa a siyasar Kano idan har Kwankwaso ya koma APC

An yi hasashen ne bayan maganganunsa na baya-bayan nan sun sake tunzura hasashe cewa ya na iya yin sulhu da APC kafin 2027, lamarin da ka iya juyar da taswirar siyasa a jihar.

Alaka tsakanin Kwankwaso da Ganduje

Daya daga cikin manyan abubuwan da ake dubawa shi ne yadda dangantakar Kwankwaso da Abdullahi Ganduje za ta kasance idan s**a hadu a jam’iyya daya.

A baya, sun yi aiki tare tsawon shekaru a matsayin gwamna da mataimaki, kafin rikici ya raba su bayan zaben shekarar 2015 lokacin da Ganduje ya karɓi mulki.

Tun daga lokacin, adawar su ta yi tsami, inda kowanne ya shiga jam’iyyar daban.

Masana sun yi nuni da cewa idan Kwankwaso ya dawo APC, sabuwar dambarwa za ta tashi tsakaninsu.

Makomar 'yan adawa a jihar Kano

NNPP ta karɓi ragamar gwamnati a Kano a 2023 bayan ta doke APC.

Wannan ya bai wa jam’iyyar ƙarfin zama babbar 'yar adawa a matakin ƙasa .

Sai dai idan Kwankwaso ya bar ta, tambaya ita ce wace jam’iyya za ta ci gaba da rike tafiyar adawa a Kano?

Wasu masu sharhi kan siyasa na ganin ADC na iya zama madadin, muddin ta samu jagora mai ƙarfi a jihar.

Haka kuma ana ganin PDP da ta taɓa zama babbar 'yar adawa za ta iya farfadowa idan manyan ‘yan siyasa s**a dawo cikinta, musamman idan shugaba Goodluck Jonathan ya tsaya takara.

Makomar jam’iyyar NNPP a jihar Kano

An yi hasashen cewa idan Kwankwaso ya fita daga NNPP tare da mabiyansa, jam’iyyar ka iya rushewa gaba ɗaya ko ta koma ƙarama mai tasiri a kananan matakai.

Yaura TV ta rahoto cewa yanzu ma akwai rikici a cikinta, inda aka samu ɓangarori biyu: na Kwankwaso da kuma na waɗanda ke cewa su ne ‘yan asali.

Masana sun ce saboda Kano ce jihar da NNPP ke da karfi sosai a Najeriya, ficewar Kwankwaso zai iya haifar da ƙarancin wakilci a majalisu da kuma rasa karfin ikon siyasa.

Mataimakin Gwamnan Kano Abdussalam Gwarzo Ya Ziyarci Wurin da Za'a Gina Kwalejin Fasaha ta GayaTawagar mataimakin Gwamna...
24/09/2025

Mataimakin Gwamnan Kano Abdussalam Gwarzo Ya Ziyarci Wurin da Za'a Gina Kwalejin Fasaha ta Gaya

Tawagar mataimakin Gwamnan jihar Kano Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo, Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi bisa jagorancin mataimakin gwamna sun kai ziyarar gani da ido wajen da za’a gina makarantar Kwalejin Fasaha ta Gaya Polytechnic a karamar hukumar Gaya.

Mataimakin gwamna Abdussalam Gwarzo ya sami tarba daga shugaban karamar hukumar Gaya Hon. Mahmoud Tajo Sani da Yan kwanitin samar da wannan makaranta da sauran yan jam’iyar NNPP kwankwasiyya da al’ummar gari.

Kazalika tuni aka fara da zuwa matsigunin Makarantar na dindin dake SIS Bangashe daga nan Kuma aka dunguma zuwa matsigunin Makarantar na wucin Gadi dake GTQSS Gaya a Saban Gari cikin ƙaramar Hukumar Gaya.

Bayan ziyarar wurin sai s**a dunguma zuwa gidan Mai martaba Sarkin Gaya inda Mai martaba sarkin Gaya Dr. Aliyu Ibrahim Abdulqadir ya yi addu’a da fatan alkhairi ga wannan makaranta.

A jawabin sa Shugaban ƙaramar Hukumar Gaya Hon. Mahmoud Tajo Gaya ya bayyana farin cikin sa bisa wannan ziyarar bazata da mataimakin gwamna ya kawo Dama sauran Yan kwamatin sa.

Sannan Kuma ya roki Gwamnan na Kano da idan za adebi ma aikatan wannan makarantar a kowanne fanni a saka da matasan mu na ƙaramar Hukumar Gaya.

Kazalika ya kara rokon gwamna Abba Kabir Yusuf da ya cigaba da samarwa wannan Karamar hukuma hanyoyin cigaba daga karshe yayi godiya ga gwamnan jihar Kano bisa wannan muhimmin aiki da ya kawo Wanda aka yi shekara da shekaru a nema.

A cewar sa tabbas Gwamna Abba ya cika Gwarzo, daga karshe ya yi musu addu'ar Allah maida su gida lafia.

Ni ban taba yunkurin neman mulkar Nigeria a Zango na uku ba – ObasanjoTsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya karyata ...
22/09/2025

Ni ban taba yunkurin neman mulkar Nigeria a Zango na uku ba – Obasanjo

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya karyata zargin da ake yi cewa ya taɓa neman wa’adi na uku a lokacin mulkinsa

Obasanjo ya bayyana hakan ne a taron tattaunawar dimokraɗiyya da aka shirya a birnin Accra dake kasar Ghana

Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya ce shugaban da ya gaza ya kamata a cire shi ta hanyar ingantaccen zaɓe

Tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ya karyata zargin cewa ya taɓa neman wa’adi na uku a lokacin mulkinsa.

Obasanjo ya bayyana hakan ne a taron tattaunawar dimokraɗiyya da aka shirya a Accra, Ghana ta gidauniyar Goodluck Jonathan.

Obasanjo ya ce babu wani ɗan Najeriya da yake rayayye ko mamaci, da zai iya gaskata cewa ya taɓa roƙon goyon bayansa don samun ya zarce wa’adi na uku.

Ya ce: “Ni ba wawa ba ne, idan na son wa’adi na uku, zan san yadda zan yi. Kuma babu wanda zai ce na taɓa kiran sa na ce ina son nayi wa’adi na uku.”

Ya kuma ƙara da cewa samun yafiya ga bashin da Najeriya ta ciyo a lokacin mulkinsa ya fi wahala fiye da neman wa’adi na uku, amma ya cimma hakan.

Sannan ya gargadi shugabanni da ke yin dogon zama kan mulki, yana mai cewa tunanin cewa babu wani da zai iya maye gurbinsu babban zunubi ne ga Allah.

Obasanjo ya jaddada cewa shugabanci ya kamata ya kasance hidima ce, ba matsayin da za a riƙe da dole ba.

A nasa jawabin, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya ce shugaban da ya gaza ya kamata a cire shi ta hanyar ingantaccen zaɓe.

Kazalika ya yi gargadin cewa maguɗin zaɓe na daga cikin manyan barazana ga dimokuraɗiyya a nahiyar Afrika, yana mai cewa idan ba a sake tunani da gyara tsarin ba, dimokuraɗiyyar na iya durƙushewa.

Jonathan ya ce ’yan Afrika na buƙatar dimokuraɗiyya da ke tabbatar da ’yancinsu da sahihin zaɓe da tsaro da ilimi da aiki da lafiya da mutunci.

Kasafin Kuɗin 2026: Al’ummar Gwarzo Sun Bayyana Bukatunsu Ga GwamnatiKaramar Hukumar Gwarzo ta gudanar da taron tattauna...
17/09/2025

Kasafin Kuɗin 2026: Al’ummar Gwarzo Sun Bayyana Bukatunsu Ga Gwamnati

Karamar Hukumar Gwarzo ta gudanar da taron tattaunawa kan kasafin kuɗin shekarar 2026, inda aka bai wa al’umma dama su bayyana bukatun ayyukan raya ƙasa da suke ganin ya dace a saka a cikin kasafin kuɗin.

A jawabinsa, Shugaban Sashen Kasafin Kuɗi na Karamar Hukumar, Alhaji Muktar Muhammad Lamido, ya bayyana cewa a kowace shekara Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar Kano na bai wa al’umma damar gabatar da muhimman bukatunsu ta hannun zababbun kansiloli, Dagatai da sauran shugabannin al’umma domin a saka su cikin kasafin kuɗin shekara mai zuwa.

A nasa jawabin, Kwamishinan Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, Hon. Muhammad Tajudden Usman, wanda Daraktan Albashi da Alawus, Kwamarad Abdullahi Muhammad Gwarzo ya wakilta, ya shawarci al’umma da su zakulo muhimman bukatun da s**a fi tasiri ga ci gaban yankin su gabatar da su ga shugabanninsu.

Kazalika ya kuma bayyana cewa gwamnati ta bullo da wannan tsari ne domin a tabbatar da cewa ra’ayin jama’a ya samu muhimmin gurbi a tsarin kasafin kuɗi.

Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Dakta Mani Tsoho, ya gode wa Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, bisa bai wa kananan hukumomi cikakkiyar dama da ’yancin gudanar da ayyukan raya ƙasa.

Haka kuma ya gode wa Hakimin Gwarzo, Sarkin Dawaki Mai Tuta na Kano, Alhaji Bello Abubakar Gwarzo, bisa yadda ya umarci Dagatai da su zauna da jama’arsu domin tattara bukatun da suke so a saka a kasafin kuɗi.

Hakimin Gwarzo, tare da Daraktar Kuɗi da Gudanarwa ta Karamar Hukumar, Hajiya Zulaihat Sabo Usman (wanda Babban Jami’in Ma’aikata ya wakilta), sun yi jawaban yabo kan tsarin, suna bayyana shi a matsayin sabuwar hanya ta tunkarar jama’a a harkar kasafin kuɗi.

Taron ya samu halartar zababbun kansiloli, Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar masu ba wa shugaban karamar hukuma shawara, sakataren mulki, Dagatai da masu unguwanni, kungiyoyin ci gaban al’umma da jami’an tsaro, waɗanda s**a nuna jin daɗinsu da damar da aka ba su wajen bayyana bukatunsu a fili.

An kammala taron ne da gabatar da bukatun ayyukan raya ƙasa da jama’a suke so a saka a cikin kasafin kuɗin shekarar 2026.

Address

Guda Abdullahi Street Farm Center Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Alkiblah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Alkiblah:

Share