Jaridar Alkiblah

Jaridar Alkiblah •Jaridar Al-Kiblah... (Mahangar Al'umma) Jarida ce da aka Samar da ita a Harshen Hausa Domin Kawo Muku Sahihan labarai.

An Ceto Daliban Da Aka Sace a KebbiAn sake samun sabon labari mai dadi daga Jihar Kebbi, inda rahotanni s**a tabbatar da...
25/11/2025

An Ceto Daliban Da Aka Sace a Kebbi

An sake samun sabon labari mai dadi daga Jihar Kebbi, inda rahotanni s**a tabbatar da cewa dalibai mata 24 da aka sace daga Makarantar Government Girls Secondary School Maga, a Karamar Hukumar Danko/Wasagu, sun kubuta.

Tuni dai gwamnatin tarayya ta tabbatar da ceto su a ranar Talata, 25 ga Nuwamba 2025.

Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara Kan Bayanai da Tsare-Tsare, Bayo Onanuga, shi ne ya tabbatar da kubutar daliban cikin sanarwar da ya fitar.

A cewar sanarwar jami’an tsaro sun gudanar da aikin hadin gwiwa domin ganin an dawo da su cikin koshin lafiya.

Har yanzu ba a bayyana ko an biya kudin fansa ba ko kuma an k**a wadanda s**a yi garkuwa da su ba.

An tattaro cewa har yanzu iyaye da al’ummar yankin na jiran karin bayani daga hukumomi, musamman game da yadda aka ceto daliban da kuma matakan da gwamnati ke shirin dauka don dakile irin wannan lamari anan gaba.

A kwanakin baya an yi ta korafe-korafe kan karuwar hare-haren ‘yan bindiga a yankunan Arewa maso Yamma, wanda ke haifar da tsoro da katse harkokin ilimi.

Sai dai ana sa ran gwamnatin jiha da ta tarayya za su fitar da cikakken bayani nan gaba, yayin da al’umma ke nuna godiya bisa kubutar daliban ba tare da samun rahoton mutuwa ba.

Wannan dai na zuwa ne a dai-dai lokacin da ake ci gaba da kira ga gwamnati ta kara kaimi wajen kare makarantu da dalibai a yankunan da ke fuskantar barazana

Labarai Cikin Hotuna: Mataimakin Shugaban Kasa Shettima Ya Dawo 𝗔𝗯𝘂𝗷𝗮 Bayan Halartar Taron Koli na 𝗚20, 𝗔𝗨–𝗘𝗨Mataimakin ...
25/11/2025

Labarai Cikin Hotuna: Mataimakin Shugaban Kasa Shettima Ya Dawo 𝗔𝗯𝘂𝗷𝗮 Bayan Halartar Taron Koli na 𝗚20, 𝗔𝗨–𝗘𝗨

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya dawo Abuja bayan ya wakilci shugaba Tinubu a taron koli na G20 da AU-EU, inda ya yi kira da a yi wa Majalisar Tsaron Majalisar Dinkin Duniya garambawul.

25/11/2025

"Ba a Taba Jam'iyyar da Ta Azabtar da 'Yan Najeriya k**ar APC ba" Cewar Atiku

Sashen Kariya na Musamman na Rundunar 'Yan Sandan Najeriya ya umarci dukkan jami'an da ke aiki a matsayin manyan jami'an...
25/11/2025

Sashen Kariya na Musamman na Rundunar 'Yan Sandan Najeriya ya umarci dukkan jami'an da ke aiki a matsayin manyan jami'an dake bada kariya ga manyan mutane wato VIPs a duk fadin kasar da su koma sansaninsu

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya sanar cewa gwamnati za ta fara kwace duk gidaje da kadarorin da masu su s**a gaza biyan ...
25/11/2025

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya sanar cewa gwamnati za ta fara kwace duk gidaje da kadarorin da masu su s**a gaza biyan kudin ƙasa daga gobe Laraba.

Ya ce ba za a ƙara wani lokaci ba, kuma ba za a saurari uzuri ba, An fara tantance sunayen masu bashi, domin a tura musu takardun kwace kadarori.

Wannan sanarwa ta jefa wasu mazauna Abuja da masu manyan kadarori cikin damuwa, suna neman hanyoyin biyan bashin kafin hukunci ya gabata.

ASUU ta bayyana lokacin yanke hukunci kan tafiya sabon yajin aiki**********Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU) ta s...
25/11/2025

ASUU ta bayyana lokacin yanke hukunci kan tafiya sabon yajin aiki

**********

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU) ta shirya gudanar da taron Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) a ranar Laraba domin yanke matsaya kan matakin da za ta ɗauka, bayan kammala sabbin tattaunawa da kwamitin sulhu na Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Yayale Ahmed.

A yunkurin dakile yiwuwar sabon yajin aiki, gwamnatin tarayya ta sake komawa teburin tattaunawa da ASUU a ranar Litinin, inda aka ci gaba da tattaunawar a daren jiya kuma ake sa ran kammala ta yau Talata.

Wani mamba na ASUU da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa tattaunawar ta ranar Litinin da Talata ita ce za ta fayyace matakin da ƙungiyar za ta ɗauka.

NNPP na Neman Jika Wa Kwankwaso Aiki, Ta Rubuta Wasika ga Hukumar INECBangaren jam'iyyar NNPP ta kayan marmari da ke ada...
25/11/2025

NNPP na Neman Jika Wa Kwankwaso Aiki, Ta Rubuta Wasika ga Hukumar INEC

Bangaren jam'iyyar NNPP ta kayan marmari da ke adawa da Rabiu Musa Kwankwaso ya rubuta wasika zuwa ga hukumar zabe mai zamanta kanta (INEC)

A wasikar, tsagin NNPP ya bukaci INEC da ta yi watsi da shirin 'yan Kwankwasiyya na gudanar da babban taro na kasa

Hakan dai na zuwa ne bayan bangaren da ke goyon bayan jagoran NNPP, Rabiu Kwankwaso ya fara shirin zaben shugabanni

Jam’iyyar NNPP ta Kayan marmari ta bukaci Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da ‘yan Najeriya su yi watsi da zaben shugabanni da tsagin Kwankwasiyya ke shirin yi.

Bangaren NNPP ya roki INEC da kar ta amince da shirin 'yan Kwankwasiyya karkashin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, tana mai bayanin cewa hakan ya karya doka.

Jaridar Punch ta rawaito cewa hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Bangaren Jam’iyyar NNPP, Mista Ogini Olaposi, ya fitar ranar Litinin.

Tsagin Kwankwaso na shirin babban taro

Ogini Olaposi ya ce NNPP ta riga da ta kammala zaben shugabanni k**ar yadda kotu ta umurta a gudanar.

Kamfanin dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattaro cewa bangaren da Kwankwaso ke jagoranta ya rubuta wa INEC takarda son sanar da ita shirinta na gudanar da zaben shugabanni da taro na kasa daga 25 ga Nuwamba zuwa Janairu 2026.

Sai dai Ogini Olaposi ya ce tsagin 'yan Kwankwasiyya ba shi da hurumin gudanar da zaben shugabanni a madadin NNPP domin yarjejeniyar da aka kulla tsakaninsu tun kafin zaben 2023 ta riga ta kare.

Tsagin NNPP ya sake taso Kwankwaso a gaba

Ya kuma jaddada korar da NNPP ta yi wa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa a 2023, da wasu daga cikin yan Kwankwasiyya saboda aikata ayyukan da s**a saba wa jam’iyya.

“Har yanzu muna mamakin yadda mutum irin Kwankwaso zai nace sai ya kwace jam’iyyar da ta ba shi dama kyauta ya tsaya takarar shugaban kasa a 2023.”

Bangaren NNPP ya yi kira ga INEC da ta cika aikinta na bin dokokin kotu da kuma sabunta sahihin jagorancin jam’iyyar a shafinta.

Ana zargin Kwankwaso da raina kotu

“Babbar Kotun Abia da Babbar Kotun Abuja sun tabbatar da korar Kwankwaso da magoya bayansa daga dukkan harkokin cikin gida na NNPP.

“Abin bakin ciki ne yadda Kwankwaso ya ki mutunta hukuncin kotu tare da yin watsi da shi," in ji Olaposi.

Jam’iyyar ta zargi tsohon shugabancin INEC da gazawa, tana mai bayyana fatan cewa sabon shugabanci zai nisanta kansa daga saba dokokin kasa, cewar rahoton Gazettengr.

Jira Ya Kare: Atiku Ya Sa Lokacin Zama Dan Jam'iyyar ADC bayan Ya Dade da Barin PDPAna sa ran Atiku Abubakar zai yi raji...
24/11/2025

Jira Ya Kare: Atiku Ya Sa Lokacin Zama Dan Jam'iyyar ADC bayan Ya Dade da Barin PDP

Ana sa ran Atiku Abubakar zai yi rajistar zama cikakken mamban ADC yau, wanda zai sauya siyasar Najeriya gabanin 2027

'Dan takarar shugaban kasar ya ce sabon burin sauya Najeriya ne ya kai su ADC, inda ya nemi al’umma su shiga jam'iyyar

A watan da ya wuce, kakakin ADC, Bolaji Abdullahi, ya bayyana dalilin da ya jawo jinkirin Atiku na zama mamban jam'iyyar

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, yana shirin zama cikakken mamban jam’iyyar ADC a yau Litinin.

Wata majiya da ke kusa da shi ta tabbatar da cewa an kammala dukkan shirye-shirye domin Atiku ya yi rajistar shiga ADC a Jada Ward 1, jihar Adamawa, inda ya fito.

A wata ganawa da ya yi da shugabannin ADC na Adamawa a Yola, Atiku ya yi karin haske kan matakin, yana mai cewa burin kawo sauyi a Najeriya ya kai su ga kaddamar da ADC, in ji rahoton Daily Trust.

Da yake jawabi ga shugabannin jam’iyyar, Atiku ya ce: “A yau, a Najeriya, akwai sabuwar gwagwarmayar siyasa, ko ba haka ba? Yau wannan gwagwarmayar ina ta kai mu? Ta kai mu ADC. Don haka mutanen Adamawa da Najeriya, sabuwar jam’iyyarmu ita ce ADC.”

Tsohon dan takarar shugaban kasar ya nemi shugabannin ADC su shirya karɓarsa, inda ya ce: “Gobe zan zama cikakken mamba. Kun shirya karɓa ta?”

Wannan tambaya ta jawo babbar amsa ta “Eh!” daga mahalarta taron.

Abin da ya jawo jinkirin shigar Atiku ADC

Tun bayan da hadakar adawa da Atiku da Peter Obi ke jagoranta ta amince da ADC a watan Yuli domin takarar shugaban kasa a 2027, mutane da dama na tambaya ko shugabannin biyu za su shiga jam’iyyar a ko a'a.

A watan da ya wuce, kakakin jam'iyyar, Bolaji Abdullahi, ya bayyana cewa ba su da katunan mambobi da s**a dace, shi ya jawo jinkirin shigar su Atiku ADC.

Ya ce: “Katunan da muka zo muka tarar ba su da inganci. Sababbin katunan da shugaban jam’iyya David Mark da sakataren jam’iyya Rauf Aregbesola s**a sanya hannu su ne kadai ingantattu.”

Aregbesola ya fara sabuwar rajista a Osun

A ranar 19 ga Nuwamba, 2025, Aregbesola ya sanar da fara sabuwar rijista ta jam’iyyar, yana mai cewa shi ma ya yi rajistarsa a Ward 8, Unit 1, Ifofin, Ilesa ta Gabas, jihar Osun.

Ya yi kira ga tsofaffin mambobin jam'iyyar da su sabunta rajistarsu, sababbi kuma su shiga jam’iyyar yanzu, in ji rahoton Punch.

Shigowar Atiku yau, k**ar yadda majiyoyi s**a tabbatar, na iya zama daya daga cikin manyan abubuwan da za su girgiza siyasar Najeriya kafin 2027.

Ko Me Ya Yi Zafi; Yar Jarida Hajiya Binta Faruk Tayi Ridda Daga Musulunci Zuwa Addinin KiristaHajiya Binta Faruk kwararr...
24/11/2025

Ko Me Ya Yi Zafi; Yar Jarida Hajiya Binta Faruk Tayi Ridda Daga Musulunci Zuwa Addinin Kirista

Hajiya Binta Faruk kwararriyar Yar jarida ce Tana aiki a NTA Yola jihar Adamawa, a ranar Lahadi 23 ga watan Nuwamban 2025 ta yi Ridda ta fita daga addinin musulunci zuwa addinin kiristanci.

Abin mamaki saboda zamanta cikakkiyar musulma hadda aikin hajji ta je ba sau daya ba, Amman daga karshe tayi Ridda.

Allah ya tsare mana imanin mu, yasa mu cika muna musulmai muyi kyakkyawan karshe.

Mai Martaba Sarkin Katsina ya amince da daga darajar  Mai girma sarki noman Gaya Alhaji Yakubu Tagahu A matsayin Sarki N...
24/11/2025

Mai Martaba Sarkin Katsina ya amince da daga darajar Mai girma sarki noman Gaya Alhaji Yakubu Tagahu A matsayin Sarki Noman Kasar Hausa.

A ranar 21 ga watan Nuwamban 2025 ne mai martaba sarkin Katsina ya mikawa sarki noman Gaya Alhaji Yakubu Tagahu takarda k**a aiki a matsayi sarkin Noman Kasar Hausa.

Fitaccen Jarumin Fina-Finan Bollywood Dharam Ya RasuFitaccen jarumin finafinan masana'antar Bollywood ta Indiya, Dharmen...
24/11/2025

Fitaccen Jarumin Fina-Finan Bollywood Dharam Ya Rasu

Fitaccen jarumin finafinan masana'antar Bollywood ta Indiya, Dharmendra wanda ake kira da Dharam ya rasu a birnin Mumbai na Indiya yana da shekaru 89 a duniya.

Firaministan India Narendra Modi ya bayyana jajensa ga iyalan mamacin da ƴan ƙasar baki ɗaya, sannan ya bayyana rasuwar jarumin da "ƙarshen zangon jaruman sinima a Indiya."

Dharmendra, wanda ya kasance yana bayyana da "mutum mai sauƙin kai" ya daɗe yana jan zarensa a harkar fim, inda yake nishaɗantar da miliyoyin masoyansa a duniya.

Ya yi fice da sunan Veeru saboda rawar da ya taka a fim ɗin Sholay a shekarar 1975, sannan ya fito a finafinai sama da 300 a gomman shekaru da ya yi a masana'antar.

An haife shi ne a ranar 8 ga watan Disamban shekarar 1935 a ƙauyen Nasrali da ke lardin Punjab Ludhiana. Malaminsa a makaranta ne ya saka masa suna Dharam Singh Deol.

A tattaunawarsa da BBC a shekarar 2018, ya ce mahaifinsa karatu ya so ya yi, amma shi tun da farko fim yake sha'awa, wanda hakan ya sa ya fi mayar da hankali kan harkar nishaɗi.

Tinubu Ya Umarci Janye Ƴan Sanda da Ke Rakiyar Manyan Mutane, Za a Dauki Dubban Jami'aiShugaba Bola Tinubu ya ba da sabo...
24/11/2025

Tinubu Ya Umarci Janye Ƴan Sanda da Ke Rakiyar Manyan Mutane, Za a Dauki Dubban Jami'ai

Shugaba Bola Tinubu ya ba da sabon umarni kan jami'an yan sanda kan rakiyar manyan mutane a Najeriya

Tinubu ya umarci a janye dukkan ‘yan sanda daga manyan mutane nan take, a mayar da su kan aikin tsaro a yankuna

Gwamnati ta ce daga yanzu masu bukatar tsaro za su nemi jami’an NSCDC, yayin da Tinubu ya amince da daukar sababbin ‘yan sanda 30,000

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin gaggawa na janye dukkan ‘yan sanda da ke tsare manyan mutane (VIPs) a fadin kasar nan.

Tinubu ya bayar da wannan doka ne yayin wani muhimmin zaman tsaro da aka yi a fadar gwamnati tare da shugaban yan sanda, hafsan sojojin kasa da na sama, da shugaban DSS.

Hakan na cikin wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafin Facebook.

Umarnin da Tinubu ya ba yan sanda

Tinubu ya umarta a mayar da jami’an ‘yan sanda zuwa ainihin aikin su na kare al’umma a cikin yankunan da ake fama da karancin jami’ai.

A sabon tsarin, duk wani babban mutum da ke bukatar tsaro daga gwamnati zai nemi jami’an tsaron NSCDC, maimakon jami’an ‘yan sanda k**ar yadda ake yi a baya.

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa wannan mataki zai taimaka wajen karfafa samar da ‘yan sanda a yankunan karkara, inda rashin jami’an tsaro ya bar jama’a cikin hadari da hare-haren ‘yan bindiga.

Sanarwar ta kara da cewa: “Yawancin yankuna, musamman kauyuka, na fama da karancin ‘yan sanda, wanda hakan ke wahalar da aikin kare rayuka da dukiyoyi.

"Shugaba Tinubu na son jami’an su maida hankali kan ainihin aikin su na ‘yan sanda.”

Za a sake diban sababbin yan sanda

Don karfafa sabon tsari, shugaban kasa ya amince da daukar sababbin ‘yan sanda 30,000 a fadin kasa, tare da shirye-shiryen inganta cibiyoyin horarwa cikin hadin guiwa da gwamnatocin jihohi.

Wadanda s**a halarci taron sun hada da hafsan sojoji, Laftanar-janar Waidi Shaibu da na sojojin sama Air Vice Marshal, Sunday Kelvin Aneke.

Sauran sun hada da sufeta-janar na yan sanda, Kayode Egbetokun da kuma daraktan DSS, Tosin Adeola Ajayi.

Fadar shugaban kasa ta ce wannan umarni wani bangare ne na sabon tsari da aka kirkiro domin karfafa jami’an tsaro da inganta tsaron al’umma a duk fadin kasar nan.

Address

Guda Abdullahi Street Farm Center Kano
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Alkiblah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Alkiblah:

Share