
02/10/2025
Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo Ya Jagoranci Taron Lafiya, Ya Bada Kayan Aiki
Daga: Abbas Yakubu Yaura
Shugaban Karamar Hukumar Gwarzo, Hon. Dakta Mani Tsoho (PhD), yau Alhamis ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki kan harkokin lafiya a karamar hukumar Gwarzo.
Taron, wanda ya haɗa shugabanni, ma’aikatan lafiya, da sauran manyan masu ruwa da tsaki, ya mayar da hankali kan inganta walwalar jama’a da tabbatar da cewa al’umma suna samun ingantattun ayyukan lafiya.
A wani gagarumin mataki na tallafa wa sashen lafiya, Shugaban ya sayawa motar Ambulance ta Asibitin Gwarzo sabbin tayoyi tare da wasu kayayyakin aikin lafiya domin ƙara sauƙaƙa ayyuka da kuma inganta hidimar jinya ga marasa lafiya.
Dakta Mani Tsoho ya jaddada cewa lafiya ita ce ginshikin ci gaban al’umma, don haka gwamnatin karamar hukumar za ta ci gaba da zuba jari wajen kyautata asibitoci da samar da kayan aikin zamani domin sauƙaƙa wa jama’a.
Ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da haɗa kai da gwamnati wajen kare lafiyar jama’a da tsaftace muhalli domin tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga kowa da kowa.