MNN Media Hub

MNN Media Hub News Reporter • Digital Creator
Politics | Crimes Report | Security | Viral Stories
Based in Nigeria.

Tirkashi 🤔 Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Sadarwa da Manufofi, Daniel Bwala, ya ce kundin tsarin mulkin N...
20/05/2026

Tirkashi 🤔

Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Sadarwa da Manufofi, Daniel Bwala, ya ce kundin tsarin mulkin Najeriya ya bai wa ‘yan ƙasa damar kare kansu daga hare-haren ‘yan ta’adda ko masu neman kashe su.

Bwala ya bayyana haka ne yayin wata hira da gidan talabijin na Arise TV a ranar Laraba, inda yake tsokaci kan hare-haren da s**a faru a ƙauyen Esiele da ke Ƙaramar Hukumar Orire ta Jihar Oyo, da kuma sace malamai da ɗalibai a makarantar firamare ta LA Primary School.

A cewarsa, kundin tsarin mulki ya tanadi haƙƙin kare kai ga kowane ɗan Najeriya.
“Tsarin mulkin Najeriya ya bai wa kowane ɗan ƙasa damar kare kansa,” in ji Bwala.

“Idan aka haɗa haƙƙina da naka da na maƙwabci na, hakan ya zama haƙƙin gama-gari na kare kanmu, kuma ‘yan Najeriya suna da damar yin hakan.”

Ya ƙara da cewa, “Idan wani ya shigo gidana da niyyar kashe ni, duk wani makami da zan yi amfani da shi wajen kare kaina kundin tsarin mulki ya amince da shi.”

Sai dai Bwala ya yi gargaɗin cewa mallakar bindigogi da wasu makamai na ƙarƙashin dokar ƙasa ne, yana mai cewa ba kowane irin makami ne ɗan ƙasa zai iya mallaka ba sai wanda doka ta amince da shi.

Ya ce al’umma na iya haɗuwa su nemi izini daga gwamnati domin samar da tsarin tsaro na haɗin gwiwa don kare kansu.

Me zaku ce akan Maganar tasa??

Zaɓen Gwaji A Facebook 👌Bari Muga wa yafi Masoya⤵️Dan Allah ka bamu minti ɗaya ka rubuta mana waye zaɓinka muna bukatar ...
20/05/2026

Zaɓen Gwaji A Facebook 👌
Bari Muga wa yafi Masoya⤵️

Dan Allah ka bamu minti ɗaya ka rubuta mana waye zaɓinka muna bukatar muga acikin waɗannan Mutane wa yafi farin jini da karɓuwa agurin Al'ummar Nigeriya.

Let's Go 👇👇

Yanzu Yanzu 🔥 🔥 Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga ts...
18/05/2026

Yanzu Yanzu 🔥 🔥

Kotu ta bayar da belin El-Rufai kan Naira miliyan 100

Wata babbar kotu da ke Abuja ta bayar da beli ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan zargin karan tsaye ga tsaron kasa da ake yi masa.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana cewa an bayar da belin ne kan kudi Naira miliyan 100, tare da sharadin cewa wanda zai tsaya masa dole ne ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro da ke Abuja.

wanna fata kuke Masa a Gaba??

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da wasu 'yan Kannywood biyu mace da namijiHukumar tace finafinai ta Jihar Kano ta sanar ...
17/05/2026

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da wasu 'yan Kannywood biyu mace da namiji

Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano ta sanar da dakatar da jaruman masana'ntar shirya finafinai ta Kannywood biyu, Adam Garba (Raba-Gardama) da Amina Uba Hassan (wadda tsohuwar matar jarumi Adam A. Zango ce), daga gudanar da harkokin fim a Jihar Kano har tsawon shekara guda.

Sanarwar da hukumar ta fitar ta hannun jami'in hulda da jama'a Abubakar Sani ta ce an ɗauki matakin ne bayan bayyanar jaruman biyu a wani bidiyo da ta bayyana a matsayin wanda ya saɓa da tarbiyya, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’ummar Jihar Kano.

Me zaku ce Akai??

Ikon Allah 🤔 Hadiza Gabon Na ramewa Maryama kuma na Haɓaka 😂Wai da gaske Yanzu Maryam Yahaya haka ta koma??
13/05/2026

Ikon Allah 🤔 Hadiza Gabon Na ramewa Maryama kuma na Haɓaka 😂

Wai da gaske Yanzu Maryam Yahaya haka ta koma??

DA DUMI-DUMI:Bashi Na Shirin Durkusar Da Nigeriya jama'a🤔Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa rabin kuɗaɗen s...
13/05/2026

DA DUMI-DUMI:Bashi Na Shirin Durkusar Da Nigeriya jama'a🤔

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa rabin kuɗaɗen shiga da Najeriya ke sa ran samu a shekarar 2026 za su tafi ne wajen biyan bashin ƙasa.

Me za ku ce?

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki na Najeriya, Saleh Mamman hukuncin daurin sh...
13/05/2026

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki na Najeriya, Saleh Mamman hukuncin daurin shekaru 75 a gidan yari bisa laifukan almundahanar kuɗi da karkatar da sama da naira biliyan 33 da miliyan 800.

Hukumar EFCC ce ta gurfanar da shi a gaban kotu kan tuhume-tuhume guda 12 da s**a shafi wanke kuɗaɗe da zamba.

Mai shari’a James Omotosho ya same shi da laifi a dukkan tuhume-tuhumen da ake masa.

Kotun ta yanke masa hukuncin shekaru bakwai-bakwai a mafi yawan tuhume-tuhumen, yayin da wasu laifukan s**a jawo masa hukuncin shekaru biyu da uku.

Alƙalin ya bayyana cewa hukuncin zai kasance ne a jere, ma’ana dole sai ya gama ɗaya kafin a fara wani, kuma babu zaɓin biyan tara a mafi yawan laifukan.

Sai dai a ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen, kotun ta ba shi damar biyan tarar naira miliyan 10.
Haka kuma kotun ta bayar da umarnin ƙwace wasu kadarori da kuɗaɗen ƙasashen waje da aka gano suna da alaƙa da tsohon ministan.

Daga cikin kadarorin akwai wasu manyan gidaje guda huɗu da ke Abuja.

TIRKASHI SHEIKH MANSUR SOKOTO YAYI ZAZZAFAN GARGADI GA MALAMAI MASU  TALLATA TINUBU DA SUNAN MUSLIM-MUSLIM 😲👇Kar malamin...
12/05/2026

TIRKASHI SHEIKH MANSUR SOKOTO YAYI ZAZZAFAN GARGADI GA MALAMAI MASU TALLATA TINUBU DA SUNAN MUSLIM-MUSLIM 😲👇

Kar malamin da ya ƙara tallata mana Muslim-Muslim ticket, ku tallata mana ayyukansu da alkhairinsu ga talakawansu

Shin abunda aka zaɓesu domin shi, kwalliya ta biya kuɗin sabulu?

Sheikh Prof. Mansur Sokoto ya faɗi haka ne yayin da ya yi watau huɗuba mai zafi akan halin da ƙasa ke ciki a wajen sallar idi.

Me zaku Ce Akai?

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MNN Media Hub posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to MNN Media Hub:

Shortcuts

Share