Arewa Hausa News

Arewa Hausa News Barka da Zuwa Shafin AREWA HAUSA NEWS, wato MATATAR LABARAI domin samun sahihai da kuma ingantattun

24/01/2026

Wesley Tafida mai shekara 106 yana daga cikin ragowar tsofaffin ’yan mazan jiya a Nijeriya da s**a yi aiki da turawan mulkin mallaka kuma s**a halarci Yaƙin Duniya na Biyu.

Dattijon, wanda a halin yanzu yake gidansa da ke garin Jalingo, hedikwatar Jihar Taraba ya shiga aiki a Rundunar Sojin Nijeriya a shekarar 1963, inda ya yi ritaya bayan ya kai matsayin RSM.

Haka kuma ya samar da iri a gidan soja, domin kuwa daga cikin ’ya’yansa akwai wanda ya gaje shi a aikin soja—Manjo-Janar HT Wesley mai ritaya—wanda sai da ya kai matakin Janar kafin ya yi titaya daga gidan soja.

Ƙarin bayani 👇 https://aminiya.ng/yadda-ya%c6%99in-basasar-nijeriya-ya-kasance-soja-%c9%97an-shekara-106/

06/01/2026

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa kuma mai neman takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC, Alhaji Atiku Abubakar, ya sha alwashin ba zai janye daga neman takarar a zaɓen shugaban ƙasa na 2027 ba.

Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Talata, wadda mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu.

06/01/2026
Innalillahi Wa'inna Ilaihir-rajiun. Wannan Baiwar Allah Mai Suna Hauwa Muhammed Ibrahim, ta tashi daga Damaturu Zataje K...
29/12/2025

Innalillahi Wa'inna Ilaihir-rajiun.
Wannan Baiwar Allah Mai Suna Hauwa Muhammed Ibrahim, ta tashi daga Damaturu Zataje Kano Sunyi Hatsarin a bayan gari Allah Ya Mata Rasuwa.

A halin da ake ciki, Gawanta Yana ( Specialist Hospital ) na garin Damaturu kusan Kwana uku gawanta Yana Mutuware domin ba'asamu Yan uwanta ba.

Ga duk Wanda Sukasan Yan'uwanta Zasu iya Sanar musu domin Suje Sukarbi Gawanta.

Yan uwa a Yada wanan posting din har yakai ga Yan uwanta.

Allah Ya jikanta da Rahama.

LABARIN GAGGAWA: Trump ya ce Amurka ta kai hare-hare masu yawa masu kisa kan ‘yan ta’adda a NajeriyaShugaban Amurka Dona...
26/12/2025

LABARIN GAGGAWA: Trump ya ce Amurka ta kai hare-hare masu yawa masu kisa kan ‘yan ta’adda a Najeriya

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana a ranar Alhamis cewa sojojin Amurka sun kai hare-hare masu muni kan ‘yan ta’addan kungiyar Islamic State a yankin Arewa maso Yammacin Najeriya, kuma ya yi alkawarin ci gaba da kai hari idan ‘yan bindigar s**a ci gaba da kashe Kiristoci.

daga Idris Shafiu Aliyu

24/11/2025

MUHAWAR: A Cikin Waɗannan Shuwagabannin Wa Arewa Tafi Buƙata A Halin Yanzu ?

“Za mu sace Shugaba Tinubu a kwanaki masu zuwa” — Inji wani kwamandan ’yan ta’adda, bayan sun sace dalibai a Kebbi da Ni...
24/11/2025

“Za mu sace Shugaba Tinubu a kwanaki masu zuwa” — Inji wani kwamandan ’yan ta’adda, bayan sun sace dalibai a Kebbi da Niger

Wani jagoran ’yan ta’adda ya fito a bidiyo yana shelar cewa su ne s**a yi garkuwa da dalibai a Kebbi da Niger, tare da yin barazanar cewa nan badaɗewa ba za su kai ga gwamnoni har ma Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Lamarin ya biyo bayan yawaitar sace-sacen dalibai da malamai a makarantun yankin Arewa, abin da ya sake tayar da hankalin al’umma game da tabarbarewar tsaro.

maganin ka kenan
23/11/2025

maganin ka kenan

Ƴan bindigar da s**a sace ɗalibai sun fara fuskantar fushin mu--Rundunar sojin ƙasaShugaban Rundunar Hadin Gwiwa ta Arew...
23/11/2025

Ƴan bindigar da s**a sace ɗalibai sun fara fuskantar fushin mu--Rundunar sojin ƙasa

Shugaban Rundunar Hadin Gwiwa ta Arewa-Masataki (JTF North West), Manjo Janar Warrah Idris, ya bayyana cewa ’yan bindiga sun fara jin matsin lambar da dakarun s**a tsananta domin ceto ɗaliban makarantar St. Mary’s Catholic School da aka sace a Papiri, ƙaramar hukumar Agwara, Jihar Neja.

Janar Idris ya fadi hakan ne bayan ya kai ziyarar duba halin da ake ciki a yankin da lamarin ya faru, inda ya samu cikakken bayani daga Manjo Janar CR Nnebiefe, kan yadda ake gudanar da atisayen hadin gwiwa da sauran hukumomin tsaro.

A cewar mai magana da yawun Operation Fansan Yamma, Kyaftin David Adewusi, rundunar ta kuduri aniyar ganin an kubutar da dukkan ɗalibai cikin koshin lafiya.

Janar Idris ya jaddada cewa babu inda ’yan bindigar za su samu mafaka, yana mai umartar dakarun su ci gaba da matsa kaimi ba tare da sassauci ba har sai an ceto kowace ɗaliba.

Ya kuma tabbatar wa sojojin da cewa ana samar da dukkan kayan aiki da tallafi da ake bukata domin tabbatar da nasarar aikin ceton.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share