19/05/2026
Duk da ya na da fayil a EFCC, Yahaya Bello ya samu tikitin takarar Sanata a Kogi
Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello, ya lashe zaben fidda gwani na jam’iyyar APC domin takarar Sanatan Kogi ta Tsakiya, duk kuwa da yana da fayil a hukumar EFCC.
Jami’in tattara sakamakon zaben, Dr. Sadiq Mohammed, ne ya sanar da hakan a ranar Litinin, inda ya ce tsohon gwamnan ya samu kuri’u 72,349, lamarin da ya ba shi nasara a kan abokan hamayyarsa mafi kusa, Ibrahim Yakubu Adoke wanda ya samu kuri’u 315 da kuma Momoh Yusuf Obaro da ya samu kuri’u 188.
A yankin Sanatan Kogi ta Yamma kuwa, rahotanni sun nuna cewa Sanata mai ci, Sunday Karimi, na kan gaba yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben.
Hakan ya biyo bayan janyewar wasu manyan masu neman tikitin takarar, ciki har da Sanata Smart Adeyemi da Samuel Bamidele Aro, gabanin kammala zaben, lamarin da ya kara bai wa Sunday Karimi damar samun nasara.
A Kogi ta Gabas kuma, rahotanni sun nuna cewa Sanata mai ci, Jibrin Isah Echocho, na baya a sakamakon da aka fitar kawo yanzu.
An ce ya sha kaye a karamar hukumarsa ta Dekina inda ya samu kuri’u biyu kacal, yayin da babban abokin hamayyarsa, Dr. Joe Erico Ameh, ya samu kuri’u 19,805.
Majiyoyin jam’iyyar sun bayyana Dr. Joe Erico a matsayin dan takarar da manyan masu ruwa da tsaki a jihar ke goyon baya.
A halin da ake ciki, wasu daga cikin manyan ‘yan takarar da s**a hada da Muritala Ajaka da Jibrin Echocho sun soki yadda aka gudanar da zaben fidda gwanin, suna masu cewa bai bi ka’idoji da tsarin jam’iyyar yadda ya kamata ba.