NBC HAUSA

NBC HAUSA Domin Samar da ingantattun labarai

02/05/2025
Ƴan Nijeriya su kare kan su don gwamnati kaɗai ba za ta iya ba - TY Danjuma Theophilus Danjuma, tsohon ministan tsaro, y...
20/04/2025

Ƴan Nijeriya su kare kan su don gwamnati kaɗai ba za ta iya ba - TY Danjuma



Theophilus Danjuma, tsohon ministan tsaro, ya bukaci ƴan Najeriya da su dauki nauyin kare kan su a yanayin rashin tsaro da ke addabar ƙasar.

TheCable ta rawaito cewa da ya ke magana a karamar hukumar Takum ta jihar Taraba, Danjuma ya ce abubuwan da s**a faru na sace-sacen mutane da kuma hare-hare na baya-bayan nan sun kara nuna cewa ba za a iya dogaro da gwamnati kadai ba wajen kare ‘yan kasa.

"Na san muna da matsaloli da dama, ciki har da tsaro, kamar kwana biyu ko uku da s**a wuce," in ji shi.

“Mun fuskanci satar mutane kuka barazanar satar mutane za ta ci gaba da kasancewa har sai mun tashi tsaye mu kare kanmu.

“A bayyane ya ke cewa gwamnati ita kadai ba za ta iya ba. Na yi gargadi tun da dadewa, a wani jawabi da na yi a Wukari, cewa dole ne mutanenmu su shirya don kare kansu.

"Wannan gargaɗin ya kasance kamar yau na yi shi."

YANZU-YANZU: Ana sa Ran Tinubu Zai Naɗa Kwankwaso a Matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya. Wata Majiya Mai Tushe ta ce, S...
20/04/2025

YANZU-YANZU: Ana sa Ran Tinubu Zai Naɗa Kwankwaso a Matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya. Wata Majiya Mai Tushe ta ce, Shugaba Tinubu na tunanin naɗa Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin sakataren Gwamnatin tarayya (SGF).

DA DUMI-DUMINSA: Yan Bindiga Sun kaiwa Sanata Natasha Akpoti Hari a gidanta Dake Jahar Kogi.Wane fata kuke Mata?
20/04/2025

DA DUMI-DUMINSA: Yan Bindiga Sun kaiwa Sanata Natasha Akpoti Hari a gidanta Dake Jahar Kogi.

Wane fata kuke Mata?

An samu tashin Gobara a wani gidan Gas da ke Rijiyar Zaki a Kano.
20/04/2025

An samu tashin Gobara a wani gidan Gas da ke Rijiyar Zaki a Kano.

DA DUMI-DUMI: Sojoji sun hana Kashim Shettima shiga Villa?Rahotanni dake yawo a kafafen sada zumunta sun nuna cewa Sojoj...
19/04/2025

DA DUMI-DUMI: Sojoji sun hana Kashim Shettima shiga Villa?

Rahotanni dake yawo a kafafen sada zumunta sun nuna cewa Sojoji dake aiki a fadar shugaban kasa sun hana mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima shiga fadar shugaban kasa, inda s**a umurce shi cewa ya cigaba da aiki daga gida har sai Shugaba Tinubu ya kammala hutun da yaje yi a kasar Faransa ya dawo Najeriya

Kodayake dai fadar shugaban kasa ta karyata labarin to amma rahoton ya nuna cewa Sojojin sun ce umurni ne s**a samu daga sama

Me za ku ce?

Rahoton jaridar A Yau

ALLAH SARKI: Kwanansa Biyar Da Fara Aiki A Wani Kamfani Hannayensa Biyu S**a Gutsure A Wajen AikinHasbunallahu Wani'imal...
12/04/2025

ALLAH SARKI: Kwanansa Biyar Da Fara Aiki A Wani Kamfani Hannayensa Biyu S**a Gutsure A Wajen Aikin

Hasbunallahu Wani'imal Wakil.

Sunansa Aliyu Ahmad, yana zaune a Shagari Lowcost dake Katsina. Ya samu jarafta ta gutsurewar hannuwa duka guda biyu, sakamakon wani aikin da ya samu a wani kamfani mai suna Jinyuan Recycling Resources Company Limited dake Kano.

Duka kwanansa biyar da fara aiki a kamfanin ya samu wannan jarabawar. Ku saka shi a addu'a Allah ya bashi ikon cin wannan jarabawar.

Tabbas mutumin kirki ne wallahi.

Daga Kabir Abdullahi Kbshow

DA ƊUMI-ƊUMINSA: An Sace Motar Nuhu Ribadu A Wani Masallacin Juma'aAn sace mota kirar Toyota Hilux, mallakin ofishin mai...
12/04/2025

DA ƊUMI-ƊUMINSA: An Sace Motar Nuhu Ribadu A Wani Masallacin Juma'a

An sace mota kirar Toyota Hilux, mallakin ofishin mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro a masallacin juma'a.

YANZU-YANZU: Atiku Abubakar Ya fice Daga Jamiyyar PDP.Wane fata kuke masa?
04/04/2025

YANZU-YANZU: Atiku Abubakar Ya fice Daga Jamiyyar PDP.

Wane fata kuke masa?

YANZU-YANZU: Rikici ya ɓarke a Unguwar jahun dake nan cikin Garin Bauchi, yayin da wani limami ya faɗi wasu maganganu da...
04/04/2025

YANZU-YANZU: Rikici ya ɓarke a Unguwar jahun dake nan cikin Garin Bauchi, yayin da wani limami ya faɗi wasu maganganu da basu dace ba akan Dr Idriss Abdul'aziz.

Matasan Unguwar s**ayi kukan kura s**a tunƙari masallacin akan sai sun yi duka wa limamin, yanzu dai an kulle masallacin limamin yana ciki matasan kuma suna waje suna jiran fitowar sa.

Daga Buhari Baba Ali

Nan bada jimawa ba zan fitar da ƙwararan hujjoji akan Akpabio na yunƙurin yin lalata da ni Sanata Natasha Akpoti-Uduagha...
04/04/2025

Nan bada jimawa ba zan fitar da ƙwararan hujjoji akan Akpabio na yunƙurin yin lalata da ni

Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya ta ce nan ba da jimawa ba za ta gabatar da hujjoji na cin zarafi ta hanyar lalata da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya yi mata.

"A lokacin da ya dace kuma a wurin da ya dace, zan gabatar da hujjojin da nake da su," in ji sanatar a shirin Politics Today na gidan Talabijin na Channels a ranar Alhamis.

Ta kuma ce, ko da yake matakin Hukumar Zaɓe ta Kasa (INEC) na kin karɓar takardar koke na neman yi mata kiranye daga kujerarta ya zo da a kurace, amma ya yi daidai.

"Ina lauya. Ina sanata kuma na fahimci yadda Najeriya ke tafiya. Abu mafi muhimmanci a gare ni shi ne cewa an dakatar da wannan yunƙurin tunbuke ni daga majalisa.

"Ina yabawa INEC duk da cewa na yi imani ya kamata su yi watsi da wannan koke tun farko," in ji ta.

Jigo a jam’iyyar PDP ta ce yawancin adireshin da aka bayar a cikin takardar neman tunbuke ta daga majalisa ba su inganta ba, domin mafi yawan gidaje a yankinta ba su da alamomin adireshi.

Daily Nigeria ✍🏻

Address

Sharada Jaen
Kano
2021

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NBC HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to NBC HAUSA:

Share