NBC HAUSA

NBC HAUSA Domin Samar da ingantattun labarai

Da Ace wannan Abun ya tabbata da yanzu muna cikin lukutar masifa A garin nan.Allah ya ƙara raba Tsakani a Siyasa 🤲🏽Amma ...
23/09/2025

Da Ace wannan Abun ya tabbata da yanzu muna cikin lukutar masifa A garin nan.

Allah ya ƙara raba Tsakani a Siyasa 🤲🏽
Amma da yanxun NNPP a kano ta rabu gida biyu tare da rigima mai karfi

~cewComr Abdussamad Umarar
Dan Jamiyyar Nnpp kwankwasiyya dake Jihar kano

YANZU-YANZU: Shehi Ahmad Mai Tajil-Izzi ya amsa gayyatar da hukumar tace finafinai da dab'i ta Jihar Kano ta yi musu aka...
18/09/2025

YANZU-YANZU:

Shehi Ahmad Mai Tajil-Izzi ya amsa gayyatar da hukumar tace finafinai da dab'i ta Jihar Kano ta yi musu akan mukabatar da s**a yi da Malam Usman Mai Dubun Isa.

Shehi ya samu rakiyar Barr Abba Hikima.

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano Kwana biyu ba...
18/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta Kaddamar da Aikin samar da wutar sola na Naira Biliyan 12 a asibitin Malam Aminu Kano

Kwana biyu bayan rikicin wutar lantarki tsakanin Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO), gwamnatin tarayya ta kaddamar da aikin samar da megawatt bakwai (7MW) na wutar sola a asibitin.

Yayin bikin kaddamar da aikin a Kano a jiya Laraba, Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi na Majalisar Wakilai, kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Bichi, Abubakar Bichi, ya bayyana cewa an ware fiye da naira biliyan 12 domin aikin, wanda ake sa ran zai baiwa asibitin wutar lantarki ba tare da dogaro da tsarin wutar lantarki ta kasa ba.

Bichi, wanda shi ne ya kawo aikin, ya ce wannan shiri ne na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na samar da sola ga dukkan manyan makarantu da asibitocin koyarwa a fadin kasar, inda aka fara da AKTH.

Ya nuna godiya ga Shugaba Tinubu bisa amincewa da kuma goyon bayan wannan aiki.

A nasa jawabin, Ministan Kimiyya, Fasaha da Kirkire-kirkire, Uche Nnaji, ya ce wannan aiki farkon mataki ne na aiwatar da shirin Sabon Fata da gwamnatin Tinubu ta zo da shi.

Ya kuke kallon lissafin Alassan Ado Doguwa a shekarar 2027 ? Anya kuwa kuna ganin zai iya kwatar kansa a hannun Algone?
17/09/2025

Ya kuke kallon lissafin Alassan Ado Doguwa a shekarar 2027 ? Anya kuwa kuna ganin zai iya kwatar kansa a hannun Algone?

Dubban Musulmai Sun Gudanar da Babban Zagayen Maulidi a Anantnag, India. Dubban Musulmai sun fito kan tituna a garin Jam...
16/09/2025

Dubban Musulmai Sun Gudanar da Babban Zagayen Maulidi a Anantnag, India.

Dubban Musulmai sun fito kan tituna a garin Jammu & Kashmir, India, domin gudanar da babban zagayen Maulidi ƙarƙashin jagorancin Sheikh Abdur-Rasheed Dawoodi Sahab (HH). Wannan zagaye na musamman ya kasance don nuna farin ciki da murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S.A.W), inda aka shaida taron ibada, addu’o’i da kuma nuna ƙaunar Manzon Allah (S.A.W).

Wasu Matasa Sun Bankawa Masallacin Izalah Wùťa A Yayin Bikin Takutaha A KanoDaga Abdulrashid Abdullahi, Kano Lamarin da ...
16/09/2025

Wasu Matasa Sun Bankawa Masallacin Izalah Wùťa A Yayin Bikin Takutaha A Kano

Daga Abdulrashid Abdullahi, Kano

Lamarin da ya faru ne a yau Asabar a garin Yalwar Dan Ziyal dake maramar hukumar Rimin Gado a jihar Kano, inda guggun wasu Matasa masu zagayen Takutaha s**a bankawa Masallacin Izalah na harin wùtà, sakamakon wa'azozin da ake yi a masallacin ba ya yi musu dadi, inda s**a yi amfani da ranar bìkin na Takutaha don huce haushinsu ta hanyar Kone masaĺlacin ķùrmùs.

Limamin masalĺacin Sheikh Dr. Nuhu Abubakar Rimin Gado, wanda shine shugaban majalisar malamai na Kungiyar Izalah Nhq Jos, reshen karamar hukumar Rimin Gado, ya bayanna lamarin a matsayin wata jarrabawa wacce za ta zamo nasara, inda ya yi addu'ar Allah Ya tona asirin wadanda s**ayi aika-aikar.

YANZU-YANZU: Kungiyar Manoma Albasa Ta Nemi Yan Nijeriya Su Sanyata Acikin Addu'a Sakamakon Farashin Albasa Da Yayi Rugu...
16/09/2025

YANZU-YANZU: Kungiyar Manoma Albasa Ta Nemi Yan Nijeriya Su Sanyata Acikin Addu'a Sakamakon Farashin Albasa Da Yayi Rugu-Rugu Inda Ake Siyarda Bahun Albasa 12,000 Maimakon 300,000 Da Aka siyar Bara.

An kammala gina katafariyar Makarantar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci Sheik Imam Junaidu Abubakar. Makarantar mai su...
16/09/2025

An kammala gina katafariyar Makarantar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci Sheik Imam Junaidu Abubakar. Makarantar mai suna Al'irfan Integrated Academy da ke Bauchi, wadda za a koyar da Ilimin Addini da na Boko.

Bayan Gwamnatin Niger ta tallafawa malam Nata'ala da miliyoyin kudade na jinyar sa.Yaɗinka riga tare da Ɗaga tutar Niger...
16/09/2025

Bayan Gwamnatin Niger ta tallafawa malam Nata'ala da miliyoyin kudade na jinyar sa.

Yaɗinka riga tare da Ɗaga tutar Niger ɗin, na nuna soyayyar sa agareta

Kunga laifinsa kuwa?

Sabuwar Doka: Ba za a iya buɗe ko amfani da asusun banki ba tare da Tax ID ba daga Janairu 2026Daga ranar 1 ga Janairu, ...
16/09/2025

Sabuwar Doka: Ba za a iya buɗe ko amfani da asusun banki ba tare da Tax ID ba daga Janairu 2026

Daga ranar 1 ga Janairu, 2026, gwamnati ta kafa doka a Najeriya wadda ta tanadi cewa duk wani ɗan ƙasa ba zai iya buɗe ko gudanar da asusun banki ba idan bai mallaki Lambar Shaida ta Haraji (Tax Identification Number – TIN/Tax ID) ba.

Wannan sabon tanadi ya shafi:

Bankuna

Kamfanonin inshora

Dillalan hannayen jari

Da sauran cibiyoyin kuɗi a ƙasar.

Hukumar haraji ta bayyana cewa, duk wanda bai nemi Tax ID da kansa ba, hukumar na da ikon yi masa rajista ta ba shi lambar ta hanyar da ta dace.

Abubuwan da za su faru:

Ba za a buɗe sabon asusun banki ba idan babu Tax ID.

Masu asusun banki da ke akwai yanzu, za a buƙaci su haɗa su da Tax ID kafin su ci gaba da yin mu’amala.

Bankuna da sauran cibiyoyin kuɗi za su sabunta tsarin ayyukansu don bin wannan doka.

Gwamnati ta ce wannan mataki zai taimaka wajen inganta tsarin biyan haraji da tsabtace mu’amalar kuɗi a ƙasar.

Allah ya kawo sauƙi ga al’umma.

Gwamnatin Saudiyya Ta Amince Da Bakukuwan Mauludi A wata sanarwar da aka samu kai tsaye da gwamnatin kasar cewar ta amin...
16/09/2025

Gwamnatin Saudiyya Ta Amince Da Bakukuwan Mauludi

A wata sanarwar da aka samu kai tsaye da gwamnatin kasar cewar ta amince a fara gudanar da zagayen murnar haihuwar fiyayyen halitta Annabi (SAW) a duk fadin kasar.

A karon farko da gwamnatin ta amince da hakan, Inda tayi umarni da a fara shgaulgulan taron a biranen Makkah, Madina, da kuma babban birin nata na Riyad.

Sai dai a hukumance Gwamnatin Saudiyya din, bata kira wannan dama data bayar kai tsaye da sunan maulidi ba, sai don taya murna da zagayowar watan da aka haifi Manzon Rahma (SAW).

Yau matatar man Dangote za ta fitar da sabbin motoci sama da 1,000 masu amfani da gas ɗin CNG domin fara rarraba fetir k...
15/09/2025

Yau matatar man Dangote za ta fitar da sabbin motoci sama da 1,000 masu amfani da gas ɗin CNG domin fara rarraba fetir kyauta ga dillalan man a faɗin Najeriya.

Matakin ana sa ran zai taimaka wajen rage tsadar man fetir tare da samar da sauƙi wajen rarraba shi.

Address

Sharada Jaen
Kano
2021

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when NBC HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to NBC HAUSA:

Share