20/05/2026
Obi ya ziyarci Kwankwaso bayan an tantance shi a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa daya tilo na NDC
Tsohon gwamnan jihar Anambra, Peter Obi, ya kai ziyarar girmamawa ga tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, a gidansa da ke Maitama a Abuja.
Ziyarar ta zo ne bayan kwamitin tantance ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Nigerian Democratic Congress ya tantance Obi tare da amincewa da shi domin zaben fidda gwani na shekarar 2027.
Kwankwaso ya tabbatar da ganawar ta cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda ya bayyana Obi a matsayin “dan uwana” tare da nuna kwarin gwiwa kan makomar jam’iyyar.
Rahotanni sun ce Obi da Kwankwaso sun shiga jam’iyyar NDC ne a farkon watan Mayun 2026 bayan ficewarsu daga jam’iyyar African Democratic Congress.
Ana kuma ci gaba da rade-radin cewa shugabannin biyu na iya hada tikitin takarar shugaban kasa gabanin zaben 2027 domin kalubalantar jam’iyyar APC mai mulki.