Vanguard Hausa

Vanguard Hausa Domin samun ingantattun labaran hausa. Don tallan kasuwanci da siyasa 09067298607 Whatsapp kaɗai

02/06/2026

Rundunar Tsaron Kasar Iran Tace Cigaba Da Hare-haren Izraela a Gaza da Lebanon Zai Jawo Matakin da Zai Shafin Mashigar hormus 👇

ZAGIN SARDAUNA: Jigo a Kwankwasiyya Ya Fice Bayan Shekaru 17 Yana Hidintamata.Wani  ɗan tafiyar Kwankwasiyya, Engr. Muha...
01/06/2026

ZAGIN SARDAUNA: Jigo a Kwankwasiyya Ya Fice Bayan Shekaru 17 Yana Hidintamata.

Wani ɗan tafiyar Kwankwasiyya, Engr. Muhammad, ya bayyana ficewarsa daga tafiyar bayan shafe shekaru 17 yana cikinta.
A cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce duk da irin alherin da ya amfana da su a ƙarƙashin jagorancin Rabiu Musa Kwankwaso, ciki har da samun ilimi kyauta, ya yanke shawarar barin tafiyar ne saboda rashin gamsuwarsa da rahotannin da ke cewa Kwankwaso ya amince da matsayin mataimakin shugaban ƙasa.
Engr. Muhammad ya bayyana cewa wannan mataki ya sa ya ji an rage darajar siyasar Arewa, yana mai cewa Kwankwaso mutum ne da ya horar da manyan 'yan siyasa, sanatoci, gwamnoni da 'yan majalisa a Najeriya.
Sai dai duk da ficewarsa, ya yaba da gudummawar Kwankwaso wajen ilimi da ayyukan alheri, tare da yi masa addu'ar Allah Ya saka masa da alheri kuma Ya ba shi Aljannar Firdausi.

Lamarin ya jawo muhawara a tsakanin magoya bayan siyasa, musamman a Arewa, kan makomar tafiyar Kwankwasiyya da kuma sabbin sauye-sauyen da ke faruwa a siyasar ƙasar nan.

Yaudarar POS: Yadda Wani Matashi Ya Tafi da Naira Dubu 86,400 Cikin DabaraWata matashiya mai sana’ar POS ta shiga cikin ...
01/06/2026

Yaudarar POS: Yadda Wani Matashi Ya Tafi da Naira Dubu 86,400 Cikin Dabara

Wata matashiya mai sana’ar POS ta shiga cikin tashin hankali bayan wani saurayi ya yi amfani da dabara wajen karɓar kuɗi fiye da yadda ya cire daga asusunsa.
Rahotanni sun nuna cewa saurayin ya je wajen POS domin cire kuɗi har Naira dubu casa’in da shida (₦96,000). Matashiyar ta karɓi katin ATM ɗinsa, ta saka adadin kuɗin a na’urar POS sannan ta miƙa masa domin ya saka lambar sirrinsa (PIN).

Yayin da yarinyar ke ƙirga kuɗin da za ta ba shi, saurayin ya yi amfani da damar da ya samu wajen sauya adadin kuɗin daga ₦96,000 zuwa ₦9,600 bayan ya saka PIN ɗinsa.
Ba tare da ta lura da abin da ya faru ba, ta kammala ƙirga kuɗin ta ba shi Naira dubu casa’in da shida (₦96,000). Bayan ya tafi ne ta sake duba bayanan cinikin (transaction) inda ta gano cewa a zahiri an cire Naira dubu tara da ɗari shida (₦9,600) kacal daga asusun saurayin.

Hakan ya sa ta yi asarar Naira dubu tamanin da shida da ɗari huɗu (₦86,400) sak**akon wannan dabara da ake zargin saurayin ya yi amfani da ita.

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce tare da zama darasi ga masu sana’ar POS da su riƙa tabbatar da adadin kuɗin da aka saka a na’ura kafin da bayan abokin ciniki ya kammala saka PIN ɗinsa.

01/06/2026

"Mijina Baya Iya Barci Saboda Halin Da Nijeriya take ciki" ~ Oluremi Tinubu

Malaman Makarantu a Jahar  Oyo Sun Yi Barazanar Tsayawa Aiki Har Sai An Ceto Dalibai 46 Da Aka SaceWani rubutu da ya baz...
01/06/2026

Malaman Makarantu a Jahar Oyo Sun Yi Barazanar Tsayawa Aiki Har Sai An Ceto Dalibai 46 Da Aka Sace

Wani rubutu da ya bazu a kafafen sada zumunta ya jawo muhawara bayan ya bayyana cewa kungiyar malamai ta jihar Oyo (NUT) ta bukaci malamai su daina zuwa aiki har sai an kubutar da yara 46 da masu garkuwa da mutane s**a sace.
Marubucin sakon, Salisu Yakubu RN RNT, ya nuna takaicinsa kan yadda yake ganin al'ummomin Arewa ke mayar da martani ga matsalolin tsaro idan aka kwatanta da yadda wasu yankuna ke hada kai wajen neman hakkokinsu.

Ya bayyana cewa an sha fuskantar hare-hare, kashe-kashe da sace-sacen mutane a Arewacin Najeriya, amma bai ga irin tsauraran matakan matsin lamba ga gwamnati da ake dauka a wasu wurare ba.

Sakon ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin masu amfani da kafafen sada zumunta, inda wasu s**a goyi bayan ra'ayin marubucin, yayin da wasu s**a ce ya k**ata a guji kalaman da za su iya haifar da rarrabuwar kawuna, a maida hankali wajen nemo mafita ga matsalolin tsaro da s**a addabi kasa.

"Tsaro da kare rayukan jama'a hakki ne na kowa, kuma ya k**ata al'umma su hada kai wajen neman mafita cikin lumana da fahimtar juna," in ji wasu daga cikin masu sharhi kan lamarin.

Sak**akon Zaben Gwajin Da Jaridar Vanguard Hausa ta Gudanar na awa 24, Kowanne Dan Takara Ga Abunda Yan comment Section ...
01/06/2026

Sak**akon Zaben Gwajin Da Jaridar Vanguard Hausa ta Gudanar na awa 24, Kowanne Dan Takara Ga Abunda Yan comment Section S**a zabeshi
An Kada Kuria 1600
Atiku Abubakar Ya samu 1043
Peter obi ya samu 480
Asiwajo Bola Tinubu ya samu 36
Kuriu Marasa kyau 77

An Gudanar da Zaben ne Bisa raayin Yan comment Section Domin bibiyar Yadda Zaben ya Gudana Ga link👇
https://www.facebook.com/share/p/1bN1e4TZE8/

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Ƙarfafa Tsaron Dazuzzuka: Jihohi 10 Na Arewa Sun Riga Sun Dauki Masu Tsaron Daji 1,000-1,000Ba...
01/06/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Ƙarfafa Tsaron Dazuzzuka: Jihohi 10 Na Arewa Sun Riga Sun Dauki Masu Tsaron Daji 1,000-1,000

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yada Labarai ga Shugaban Ƙasa, Abdulaziz Abdulaziz, ya yi karin haske kan shirin ɗaukar masu tsaron daji (Forest Guards) 1,000 a Jihar Oyo, yana mai bayyana cewa wannan ba wani tsari ne na musamman ga yankin Kudu maso Yamma ba.

A cewarsa, tun kafin shirin na Oyo, jihohi 10 sun riga sun kafa rundunar masu tsaron daji, kuma mafi yawansu jihohin Arewa ne. Ya ce kowace jiha ta dauki kusan mutum 1,000 domin taimakawa wajen magance matsalolin tsaro, musamman satar mutane da hare-haren da ke faruwa a dazuzzuka.

Jihohin da s**a riga s**a kafa rundunar Forest Guards sun hada da Borno, Yobe, Adamawa, Kwara, Sokoto, Kebbi, Niger, Plateau da Benue.
Haka kuma, ya bayyana cewa jihohin Kaduna, Edo, Kogi da Bauchi suna kan hanyar aiwatar da irin wannan shiri.

Malam Abdulaziz ya jaddada cewa manufar shirin ita ce ƙarfafa tsaro a dazuzzuka da kuma taimakawa jami’an tsaro wajen dakile ayyukan masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka.

01/06/2026

Zamu Bayanna Wanda Yayi Nasara a Zaben Shugaban Kasa na Gwaji da mukayi a jiya
Wanda Bai yi Zabe Ba Ga link 👇

Matashi Ya Kashe Ɗan Uwansa Ɗan Okada Domin Ya Kwace Babur, Ya Danganta Lamarin Da TalauciAuchi, Edo State – Wani matash...
01/06/2026

Matashi Ya Kashe Ɗan Uwansa Ɗan Okada Domin Ya Kwace Babur, Ya Danganta Lamarin Da Talauci

Auchi, Edo State – Wani matashi ɗan asalin Jihar Bauchi ya shiga hannun jami’an tsaro bayan zarginsa da kashe wani ɗan acaba (okada) domin ya mallaki babur ɗinsa, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’umma.
A cewar bayanan da ake yaɗawa, matashin ya bayyana cewa yana gudanar da aikin babur ne a garin Auchi, inda yake kula da iyalinsa – matarsa da ɗansa – ta hanyar biyan kuɗin babur a hankali ga mai shi.
Ya ce matsalarsa ta fara ne bayan rasuwar mahaifiyarsa a Bauchi, wanda ya sa ya miƙa babur ɗin ga mai shi kafin ya tafi jana’izar. Bayan dawowarsa, ya yi ikirarin cewa an hana shi karɓar babur ɗin domin ci gaba da aikinsa.
Matashin ya ƙara da cewa bayan ya rasa hanyar samun abin dogaro, har ma ya kasa samun rancen kuɗin komawa gida, sai ya shiga cikin damuwa da neman mafita.

Rahotanni sun nuna cewa daga bisani ya kai hari ga wani ɗan okada, inda ake zarginsa da kashe shi domin kwace babur ɗinsa da nufin amfani da shi wajen neman kuɗi.

Jami’an tsaro sun k**a wanda ake zargin, kuma ana ci gaba da bincike kan lamarin domin tabbatar da gaskiyar abubuwan da s**a faru.

Lamarin ya sake jawo hankalin jama’a kan matsalolin talauci da rashin aikin yi, yayin da masu sharhi ke jaddada cewa duk wani ƙalubalen rayuwa ba hujja ba ne ta aikata laifi ko zubar da jinin wani.

Allah Ya jikansa wanda ya rasu, Ya kuma kare matasa daga fadawa cikin ayyukan da za su lalata rayuwarsu.

WATA SABUWA: Rikicin Izalah Da Masarautar Zazzau Bayan An kulle Massalatai Guda 9 na Kungiyar Ban yi mamaki ba don Zazza...
01/06/2026

WATA SABUWA: Rikicin Izalah Da Masarautar Zazzau Bayan An kulle Massalatai Guda 9 na Kungiyar

Ban yi mamaki ba don Zazzau Emirate ta kulle masallatan Jibwis Nigeria guda wajen 9 na jihar Kaduna! Ko kaɗan ban yi mamaki ba saboda hakan na da alaƙa da ƙarfafawar da Izalar ta yi a lokacin rikicin Albani Zaria da Sarkin Zazzau wanda ya rasu!

Albani Zaria yana ji yana gani Izalar Kaduna da ɗaya ɓangaren Izalar Jos s**a goyi bayan Fadar Zazzau da malamanta wanda kusan duka na ɗariƙu ne, s**a rabu da Albani Zaria, da a ce tun wancan lokacin sun haɗa kai kuma sun tabbatar da adalci ga Albani Zaria da wannan cin-kashin bai zo kansu ba a yau. Wannan ita ce gaskiyar magana! Gaskiya ce mai ɗaci. Mu karɓa da haƙuri dukanmu!

Abin da Albani ya so ya tabbatar kuma ya yi kafiya a kai shi ne, ƙin amincewa da katsalandan ɗin da masarautar ke yi– sai dai kash, su malaman Izalan Kaduna da Jos don haushin Albani da suke ji na dalilin kansu ya sa s**a kasa mara masa baya. To yàƙin da ya ci Albani shi ne yanzu yake cin Izalar Kaduna! Tun da sun ƙi haɗa kai a baya su kashe yaƙin! Ga shi ya biyo su. Tarihi ai ba ya rahama! Ƙwarai kuwa!

Na ga wasu malamai na Jibwis Kaduna suna ta wa'azi har suna furta kalmomi masu zafi a kan masarautar, gaskiya hakan ba zai magance ba. Abin da ya fi shi ne, su kai wa Shugaba Abdullahi Bala Lau matsalar, shugaba shi ya san yadda zai yi ya tattauna da Sarki daga sama don a magance matsalar, zafin-kai a wannan matsala ba za ta haifar da gyara ba! Ba a san Izala da haka ba! Izalar jihar Kaduna ta riga ta yi kuskure wajen goyon bayan su Shek Sani Khalifa tun farko a lokacin Albani kuma shi ne matsalar da s**a samu har fadar Zazzau ta samu wannan dama na abubuwan da take yi ta samu ƙarfi matuƙa gaya!

Kawai Izalar Kaduna su ɗauki darasi su kwantar da hankali sannan su kai matsalar gaba in sun tabbatar ta fi ƙarfinsu, wannan shi ne kawai. Kuskure ne an yi shi tun lokacin Albani Zaria. Shi ɗan bidi'a ba ya wasa da damarsa a kan malaman sunnah, abin da ya faru da Dr. Idris a Bauchi ya ishi kowa ishara a kan waɗannan mutanen!

Allah ƙara tsarewa.

Yakubu sani

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Vanguard Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Vanguard Hausa:

Share