Muhammad sale evt

Muhammad sale evt politics and enjoyments with respect of law

08/04/2025

Sakon wani Dan Nigeria mazaunin kasar Qatar

Har Yanzu Bamuga Hukunci Ko Cikakken Rahoto Dake Nuna An Dauki Mataki Akan Kisan Mutane 16 a Edo Ba.
Amma sai gashi jiya muna ganin yadda aka gayyato Sarkin Kano zuwa Abuja domin kawai yayi hawan Sallah — alhali har yanzu ana yi masa barazana saboda siyasa.

Ina jami’an tsaro musamman AIG Me ya hana shi gayyato Gwamnan Edo ko Sarkin Edo domin tattauna yadda za a shawo kan lamarin kisan mutane 16 da aka yi? Ko kuwa rayuwar 'yan Edo bata da daraja ne?

Yak**ata AIG ya mayar da hankali kan aikinsa, ba kokarin rage kimar masarauta ba. Masarautu al’adun mu ne, alfarma ce kuma tushen zaman lafiya.

Gwamnatin tarayya ta daina amfani da rundunar ‘yan sanda wajen cimma manufofinta na siyasa. Subar al’ummar Kano su zauna lafiya. Kuma a tabbatar da adalci ga wadanda aka kashe a Edo Mutanen Kano.

Abdoull Elberla...

08/04/2025
08/04/2025

Yau kwana 12 da kisan yan uwanmu a Uromi, Edo State.

1. Ina wadanda aka k**a?
2. Su nawa ne?
3. Me ake shirin yi da su?
4. Ina rahoton yan sanda na kwarya-kwarya (Public Situation/ incident report)
5.Ina kwamitin da aka nada daga Kano domin ziyartar garin?
6. Ina ma sunayen wadanda aka kashe?
7. Su nawa ne?
8. A wane hali iyalinsu suke?
9. Ina aka kwana?
10. Ina? Ina? Ina?

Da haka da haka fa bincike yake lalacewa a kasar nan.

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu a jam'iyyar APC, wanda ya shafe sama da shekaru 20 yana majalisa, y...
08/04/2025

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar mazabar Borno ta Kudu a jam'iyyar APC, wanda ya shafe sama da shekaru 20 yana majalisa, ya bayyana cewa nade-naden da Shugaba Bola Tinubu ya yi zuwa yanzu sun saba da tsarin raba madafun iko na kasa (Federal Character) kuma ya k**ata a gyara hakan.

Ndume ya bayyana cewa, a matsayinsa na dan Najeriya, yana da hakkin bayyana ra'ayinsa, duk da cewa yana tsammanin wasu za su kai masa hari kan wannan batu, amma ya jaddada cewa ba wani abu ne na kashin kai ba.

Ya kuma nuna damuwarsa kan cewa wasu masu ba da shawara ga shugaban kasa suna ba shi shawarwari marasa kyau, wanda hakan ke kara jefa kasar cikin mawuyacin hali. Ndume ya bukaci Shugaba Tinubu da ya mayar da hankali wajen zabar mutane masu kwarewa da cancanta a nade-nadensa.

Da dumi'dumi: Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya bayar da umarnin a sakin Naira biliyan 3.8 domin biyan 'yan Fansho da G...
08/04/2025

Da dumi'dumi: Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya bayar da umarnin a sakin Naira biliyan 3.8 domin biyan 'yan Fansho da Gratutu

Gwamna mal Uba sani Ya yanke hukuncin ne bisa dalilai na jin kai bayan korafe-korafe daga ‘yan fansho da iyalan ma’aikatan gwamnatin da s**a rasu dangane da yanayin rayuwarsu sak**akon aikin tantancewar da ake yi.

Gwamnan ya jaddada cewa tantancewar na da nufin kawar da ‘yan fansho na bogi da kuma kare dukiyar jihar tare da tabbatar da biyan kudaden fansho na gaskiya kan lokaci.

Ya kuma tabbatar wa ‘yan fansho da jajircewarsa wajen kyautata rayuwarsu da kuma gaggauta kammala aikin tantance kudaden fansho ba tare da katsewa ba.

- Tun daga watan Mayun 2023, an riga an biya jimillar Naira biliyan 6.6 a matsayin kuɗin yan fansho da s**a rasu.

Dream is not reality
31/01/2025

Dream is not reality

https://tbta.top/70770409735202
26/12/2024

https://tbta.top/70770409735202

TaskCash is the #1 marketing network. With over $14 million paid to 300k members, TaskCash lets regular users make money with social media and friends!

Address

Bennie International School Kano
Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muhammad sale evt posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share