Arewa Times Hausa

Arewa Times Hausa News/Media Website
(2)

23/06/2026

Jarumin Kannywood Sadiq Sani Sadiq Ya Jaddada Aniyarsa Ta Gudanar Da Zanga-Zangar Lumana

Fitaccen jarumin masana’antar Kannywood, Sadiq Sani Sadiq, ya sake jaddada aniyarsa ta gudanar da zanga-zangar lumana domin bayyana damuwa kan matsalolin tsaro, hauhawar farashin kayayyaki, garkuwa da mutane da kuma kalubalen tattalin arziki da ke addabar al’ummar Najeriya.

Jarumin ya bayyana cewa ya saurari ra’ayoyi da shawarwari daga bangarori daban-daban, ciki har da masu goyon bayan shirin da kuma wadanda ke adawa da shi, amma ya ce hakan ba zai sa ya yi watsi da kudurinsa ba.

A wata sanarwa da ya fitar, Sadiq ya tabbatar da cewa za a gudanar da zanga-zangar cikin tsari da lumana, yana mai jaddada cewa manufarta ita ce isar da sakon al’umma cikin bin doka da oda.

“Na saurari dukkan shawarwarinku kuma ina matukar godiya da gudunmawar da kuka bayar. Sai dai ba zan fasa gudanar da zanga-zangar ba, In Sha Allah. Za mu gudanar da ita cikin lumana,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa nan gaba kadan za a fitar da cikakken bayani kan yadda za a gudanar da zanga-zangar, tare da bayyana matakan da za a bi domin tabbatar da zaman lafiya da kauce wa duk wani tashin hankali.

Shirin zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da nuna damuwa kan matsalolin tsaro da matsin rayuwa da ke fuskantar al’umma a sassa daban-daban na kasar nan.

23/06/2026

Fitaccen malamin Addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Tijjani Yusuf Guruntum, ya garhaɗi Al'ummar kasa masu karbar kuɗi kafin Zabe, a cewar malamin “ Ku tanadin kudin Fansa kafin karbar kudin kaɗa kuri'a” inji Malamin

23/06/2026

"Kafafen yaɗa labarai na da muhimmiyar rawa wajen bayyana ƙalubalen da ke addabar Arewa tare da taimakawa wajen nemo mafita mai ɗorewa."

NDLEA ta yi gargaɗin cewa shan miyagun ƙwayoyi na  zama barazana ga ƙasaHukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun Ƙwayoyi ...
23/06/2026

NDLEA ta yi gargaɗin cewa shan miyagun ƙwayoyi na zama barazana ga ƙasa

Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun Ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) ta bayyana cewa matsalar dogaro da miyagun ƙwayoyi na ƙara zama babbar barazana a Najeriya, tare da kira ga masu yawan amfani da magunguna da su nemi taimakon hukumar.

Sakataren hukumar, Shadrach Haruna, ya bayyana haka a Abuja yayin bikin ranar yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi da fataucinsu ta majalisar ɗinkin duniya ta 2026.

Ya ce hukumar ta samar da layin waya na sa’o’i 24 domin ba da shawarwari da tura masu fama da matsalar zuwa cibiyoyin jinya da gyaran hali mafi kusa da su.

Haruna ya ce duk wanda ya kira lambar taimakon hukumar zai samu amsa cikin harsuna daban-daban da s**a haɗa da Hausa, Yarbanci, Igbo, Turancin Pidgin da Ingilishi.

Ya ƙara da cewa jinya da gyaran hali na daga cikin muhimman hanyoyin da NDLEA ke amfani da su wajen yaƙi da matsalar shaye-shaye tare da wayar da kan jama’a da kuma aiwatar da doka.

Sakataren ya kuma bayyana cewa hukumar na haɗa kai da ƙungiyoyin addini da coci-coci domin ƙarfafa yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi ta hanyar wa’azi, shawarwari da tallafa wa iyalai masu fama da matsalar.

15/05/2026

“Cikin girmamawa da fatan alheri, Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya raka maniyyata rukuni na farko 560 zuwa ƙasa mai tsarki, yayin da s**a tashi daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a daren Juma’a zuwa Madina.

Gwamnan ya buƙaci alhazan da su yi wa jihar Kano da Najeriya addu’o’in zaman lafiya, wadata da ɗorewar ci gaba a yayin gudanar da ibadunsu.”

Sanatan Amurka, Riley Moore, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa Amurka na shirin raba Najeriya gida biyu. A cikin wat...
07/02/2026

Sanatan Amurka, Riley Moore, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa Amurka na shirin raba Najeriya gida biyu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Moore ya bayyana cewa duk da kasancewarsa a Najeriya inda ya yi ganawa da manyan jami’an gwamnati, batun raba ƙasar bai taɓa tasowa a tattaunawar ba.

Adawa Ko Gaskiya?Tsohon ɗan wasan baya na Liverpool, Jamie Carragher, ya soki Cristiano Ronaldo kan yadda yake yin hira ...
07/02/2026

Adawa Ko Gaskiya?

Tsohon ɗan wasan baya na Liverpool, Jamie Carragher, ya soki Cristiano Ronaldo kan yadda yake yin hira da kafafen yaɗa labarai, yana mai cewa hakan “abin kunya ne” ga ɗan wasa irinsa.

Carragher ya ce idan Ronaldo, a shekarunsa, yana shirya hirarraki da abokansa domin yin magana kan wasu lig-lig, masu horaswa da ’yan wasa, hakan na nuna rashin kwanciyar hankali.

Ya ƙara da cewa Ronaldo na daga cikin manyan ’yan wasa a tarihi kuma ba sai yana yin hirarraki akai-akai domin tabbatar da hakan ba, yana zargin cewa tambayoyin da ake yi masa a irin waɗannan hirarrakin an riga an tsara su.

Carragher ya kuma kwatanta hakan da Lionel Messi, yana mai cewa a hirarrakinsa, Messi yakan fi mayar da hankali kan iyalinsa, ƙungiyarsa da kuma ƙasarsa.

EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M. Inuwa, kan zargin wulakanta NairaHukumar Yaki da Cin Hanci da Rasha...
03/02/2026

EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M. Inuwa, kan zargin wulakanta Naira

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M Inuwa, bisa zargin wulakanta kudin Najeriya (Naira), bayan wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta.

Rahotanni sun nuna cewa jami’an EFCC daga reshen Kano ne s**a k**a jarumar, kuma a halin yanzu tana tsare a hannun hukumar yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Mai magana da yawun EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da kamen a Abuja, inda ya bayyana cewa an dauki matakin ne bayan bayyanar bidiyon da ke nuna Samha Inuwa tana goge majina daga hancinta da takardun kudi na Naira.

Oyewale ya kara da cewa da zarar an kammala bincike, EFCC za ta gurfanar da jarumar a gaban kotu domin ta fuskanci hukunci bisa laifin da ake zarginta da aikatawa.

Lamarin ya janyo cece-kuce a tsakanin al’umma, inda jama’a ke jiran matakin da kotu za ta dauka.

Yadda dubban al'umma s**a halarci jana'izar Sheik Usman Kusfa Zaria wato Rigi-Rigi.An gudanar da jana'izar da yammacin y...
02/02/2026

Yadda dubban al'umma s**a halarci jana'izar Sheik Usman Kusfa Zaria wato Rigi-Rigi.

An gudanar da jana'izar da yammacin yau Litinin a filin Low-cost da ke Zaria.

Daga Umar Idris ShuaibuTsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Hukumar Kula da Filayen...
02/02/2026

Daga Umar Idris Shuaibu

Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya karɓi Kakakin Gwamnan Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, tare da wasu shugabannin APC daga jihar a gidansa da ke Abuja.

Taron, wanda ya gudana a ƙarshen mako, na daga cikin jerin tuntuba da ake yi da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano, k**ar yadda wata sanarwa da Mohammed Garba, Shugaban Ma’aikata ga tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya fitar ta bayyana.

A cewar sanarwar, tawagar ta haɗa da Shugaban Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa, Hon. Anas Mukhtar Bello Dan Maliki, da kuma sauran fitattun shugabannin APC daga yankin.

Address

No. A1 Dantsoho Plaza, Abdullahi Bayero Road
Kano
700101

Telephone

+2348022400739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Times Hausa:

Shortcuts

Share