Arewa Times Hausa

Arewa Times Hausa News/Media Website
(2)

‎Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Tarayya 41 Saboda Barazanar Tsaro‎‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da ...
21/11/2025

‎Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Tarayya 41 Saboda Barazanar Tsaro


‎Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun 41 na tarayya (Federal Unity Colleges) nan take saboda ƙarin barazanar tsaro da aka samu a wasu sassan ƙasar nan.

‎Umarni na ƙunshe ne cikin wata takarda mai ɗauke da kwanan wata 21 ga watan Nuwamba, 2025, da Ma’aikatar Ilimi ta fitar, wace Babbar Daraktar Makarantun Sakandare, Hajiya Binta Abdulkadir, ta sanya wa hannu a madadin Ministan Ilimi.

‎Ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne duba da ƙalubalen tsaro da ake samu a wasu yankuna, tare da buƙatar daƙile duk wata matsalar tsaro da ka iya shafar rayuwar ɗalibai da ma’aikata, musamman a wuraren da ake ganin suna da rauni.


‎Takardar ta kuma umarci shugabannin makarantun da abin ya shafa da su tabbatar da bin wannan umarni yadda ya k**ata.

‎Makarantun da aka rufe sun haɗa da FGGC Minjibir, FGC Ilorin, FTC Ganduje, FGGC Zaria, FTC Kafanchan, FGGC Bakori, FTC Dayi, FGC Daura, FGGC Tambuwal, FSC Sokoto, FTC Wurno, FGC Gusau, FGC Anka, FGGC Gwandu, FGC Birnin Yauri, FTC Zuru, FGGC Kazaure.

‎Sauran kuma su ne: FGC Kiyawa, FTC Hadejia, FGGC Bida, FGC New-Bussa, FTC Kuta-Shiroro, FGGC Omuaran, FTC Gwanara, FGC Ugwolawo, FGGC Kabba, FTC Ogugu, FGGC Bwari, FGC Rubochi, FGGC Abaji, FGGC Potiskum, FGC Buni Yadi, FTC Gashua, FTC Michika, FGC Ganye, FGC Azare, FTC Misau, FGGC Bajoga, FGC Billiri, da FTC Zambuk.

‎Sai dai ma’aikatar ilimin ba ta bayyana ranar da za a sake buɗe makarantun ba, amma ta ce an ɗauki matakin ne da zummar kare rayukan ɗaliban da sauran ma’aikata.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin sa na kammala dukkan shirye-shirye da s**a dace don  gabata...
15/11/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ce gwamnatin sa na kammala dukkan shirye-shirye da s**a dace don gabatar da kasafin kuɗi na farko a tarihin jihar mai darajar Naira triliyan 1 na shekarar 2026.

A yayin bude Taron Majalisar Zartaswa ta Musamman ta Biyu, Gwamna Yusuf ya ce girman wannan kasafi yana nuna azancin gwamnati wajen aiwatar da manyan ayyuka, gyaran birane, da fadada ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Ya bayyana cewa karuwar kasafin kuɗin na 2026 ta samo asali ne daga inganta hanyoyin samun kudaden shiga na cikin gida da kuma dakile duk wata asarar kudade, wanda hakan zai ba gwamnati damar aiwatar da manyan ayyuka masu sauyi a jihar.

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na kan gaba wajen kafa wani kwalejin kimiyy...
15/11/2025

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa na kan gaba wajen kafa wani kwalejin kimiyya da Fasaha a karamar hukumar Gaya, a matsayin wani ɓangare na yunkurin fadada damar samun ilimi na fasaha da sana’o’i a jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Laraba, gwamnan ya bayyana wannan ne yayin kaddamar da rukunin biyu na shirin tallafin karatu ga daliban digiri na biyu daga gida da ƙasashen waje a Fadar Gwamnatin Jihar Kano.

Gwamna Yusuf ya ce kafa wannan kwalejin wani muhimmin mataki ne da zai ƙarfafa ilimi na fasaha da sana’o’i, yana mai jaddada muhimmancin koyon ƙwarewa da kirkire-kirkire wajen samar da ayyukan yi da habaka tattalin arziki.

Gwamnatin Amurka na shirin tarbar Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman (MBS), a wata ziyara ta aiki da za ta gudana a b...
15/11/2025

Gwamnatin Amurka na shirin tarbar Yariman Saudiyya, Mohammed bin Salman (MBS), a wata ziyara ta aiki da za ta gudana a birnin Washington a ranar 18 ga Nuwamba.

Bayanai sun nuna cewa za a yi ganawa ta musamman tsakanin MBS da Donald Trump a Fadar White House, kafin a ci gaba da liyafa da tarukan kasuwanci a babban birnin.

Rahotanni sun ce manyan ’yan kasuwa, shugabannin kamfanoni, ’yan majalisar dokoki da jami’an gwamnati za su halarci liyafar, wadda ake ganin za ta kasance ɗaya daga cikin manyan tarukan diflomasiyya na wannan shekara.

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya jagoranci wasu manyan jagororin jam’iyyar zuwa zauren Majal...
14/11/2025

Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya jagoranci wasu manyan jagororin jam’iyyar zuwa zauren Majalisar Wakilai domin shaida sauya shekar wasu ‘yan majalisa biyu daga jam’iyyar NNPP zuwa APC.

Taron, wanda aka gudanar a ranar Alhamis, ya samu halartar tsohon shugaban APC na ƙasa kuma shugaban kwamitin gudanarwa na Hukumar Filayen Jiragen Sama (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje; Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Hon. Femi Gbajabiamila; da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin.

‘Yan majalisar da s**a sauya shekar sun haɗa da Hon. Abdulmumin Jibrin, mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji, da Hon. Sagir Koki, mai wakiltar mazabar Kano Municipal, dukkansu daga Jihar Kano.

Hukumar kula da harkokin man fetur ta ƙasa, Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), t...
14/11/2025

Hukumar kula da harkokin man fetur ta ƙasa, Nigerian Midstream and Downstream Petroleum Regulatory Authority (NMDPRA), ta sanar da dakatar da shirin fara karɓar harajin kashi 15 cikin 100 kan man fetur da dizel da ake shigowa da su ƙasar nan daga waje.

Mai magana da yawun hukumar, George Ene-Ita, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Alhamis.

A ranar 29 ga Oktoba, Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya amince da saka wannan haraji, wanda zai ƙara farashin man da ake saukewa a defo-defo.

Majalisar Matasan Arewa (NYA), ƙungiyar matasa daga jihohi 19 na Arewa masu ra’ayin ci gaba, ta bayyana rashin jin daɗin...
12/11/2025

Majalisar Matasan Arewa (NYA), ƙungiyar matasa daga jihohi 19 na Arewa masu ra’ayin ci gaba, ta bayyana rashin jin daɗinta kan yadda Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya nuna rashin girmamawa ga wani matashi soja a Abuja.

A cewar NYA, wannan lamari da ya yadu a kafafen yada labarai na gargajiya da na zamani, yana nuna girman kai, amfani da iko ba yadda ya k**ata ba, da rashin mutunta ɗabi’un shugabanci daga wani jami’in gwamnati da ya k**ata ya zama abin koyi.

Majalisar ta ce, wulakancin da Ministan ya yi wa matashin soja, wanda ke gudanar da aikinsa na doka, ba kawai rashin ɗabi’a bane, har ma ya tauye darajar aikin gwamnati da kuma dubban matasan Najeriya da ke kallon jami’an gwamnati a matsayin abin koyi.

An sace motar mataimakin gwamnan Kano a gidan gwamnatiWani da ake zargin barawo ne ya shiga Gidan Gwamnatin Kano da asub...
12/11/2025

An sace motar mataimakin gwamnan Kano a gidan gwamnati

Wani da ake zargin barawo ne ya shiga Gidan Gwamnatin Kano da asuba a ranar Litinin, inda ya yi awon gaba da wata motar Toyota Hilux dake cikin ayarin motocin dake rakiyar mataimakin gwamnan jihar.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru da kimanin ƙarfe 5 na safe, bayan wanda ake zargin ya samu damar shiga ta Kofa ta 4 dake gidan gwamnatin sannan ya fice ta babbar ƙofa ba tare da an lura da shi ba.

Majiyoyi daga Gidan Gwamnatin sun tabbatar cewa hoton na'urar CCTV da aka duba ya nuna barawon yana tuƙa motar yayin da yake fita daga harabar gidan gwamnati.

Direban motar, wanda aka bayyana da suna Shafiu Sharp-Sharp, ya sha tambayoyi kuma aka tsare shi na ɗan lokaci domin bincike.

Majiyar jaridar Kano Times, ta rawaito cewa an kaddamar da bincike kan wannan lamari.

Jaridar tace kokarin samun mai magana da yawun Gwamna Abba Kabir Yusuf, wato Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya ci tura, domin bai ɗaga waya ba kuma bai amsa sakonni da aka tura masa ba.

An rasa inda aka kai Naira triliyan 210 daga asusun NNPC--MajalisaMajalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewa dole ne Ka...
12/11/2025

An rasa inda aka kai Naira triliyan 210 daga asusun NNPC--Majalisa

Majalisar Dattawan Najeriya ta bayyana cewa dole ne Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) ya mayar da kuɗaɗen da ba a bayyana yadda aka yi da su ba, waɗanda s**a kai naira tiriliyan 210, zuwa Asusun Tarayya.

Kwamitin Majalisar Dattawa kan Lissafin Kuɗaɗen gwamnati ƙarƙashin jagorancin Sanata Aliyu Wadada ne ya yanke wannan hukunci, bayan shugaban kamfanin, Bayo Ojulari, ya gaza bayyana a zaman kwamitin domin ya fayyace amsoshin tambayoyi da aka aika masa ba.

A binciken da aka gudanar kan ayyukan NNPCL daga shekara ta 2017 zuwa 2023, kwamitin ya gano kuɗaɗe da ba a iya bayyana yadda aka yi da su ba da s**a kai naira tiriliyan 103 a matsayin kuɗin kashewa da kuma naira tiriliyan 107 a matsayin abin da ake bin kamfanin bashi.

Sanata Wadada ya ce bayanan da kamfanin ya bayar suna cike da sabani da rashin daidaito.

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙwaryar birnin Kano ya fice daga jam'iyyar NNPPDan majalisar tarayya mai wakiltar bir...
12/11/2025

Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar ƙwaryar birnin Kano ya fice daga jam'iyyar NNPP

Dan majalisar tarayya mai wakiltar birnin Kano Hon. Injiniya Sagir Ibrahim Koki, ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar NNPP.

A cikin wata wasiƙar da ya aikawa Shugaban jam’iyyar NNPP na mazabar sa ta Zaitawa a ranar 11 ga Nuwamba, 2025, Koki ya bayyana cewa ya yanke shawarar barin jam’iyyar saboda rikicin cikin gida da ke addabar shugabancin jam’iyyar a matakin ƙasa.

Koki, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Kwamitin Majalisar Wakilai kan Albarkatun Man Fetur, ya gode wa jam’iyyar NNPP bisa damar da ta ba shi ya yi aiki a ƙarƙashin ta, inda ya bayyana goyon baya da kwarewar da ya samu a matsayin “abin da ba za a manta da shi ba.”

Sai dai bai bayyana jam’iyyar da zai koma ba ko matakin da zai ɗauka nan gaba.

Babu gwamnan da zai yi kukan rashin kuɗi a mulkin Tinubu, inji gwamnan LegasGwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya ...
12/11/2025

Babu gwamnan da zai yi kukan rashin kuɗi a mulkin Tinubu, inji gwamnan Legas

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya ce a ƙarƙashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, babu wani gwamna ko shugaban ƙaramar hukuma da zai ce gwamnati na fama da ƙarancin kuɗi.

Sanwo-Olu ya bayyana haka ne a Kaduna yayin wani taron bita na kwana ɗaya da ƙungiyar Arewa Think Tank (ATT) ta shirya don tunawa da cikar Najeriya shekara 65 da samun ‘yancin kai.

Ya ce an samu ƙaruwa mai yawa a rabon kudaden gwamnatin tarayya, wanda hakan ya bai wa jihohi da ƙananan hukumomi damar aiwatar da muhimman ayyukan raya kasa.

A cewar gwamnan, daga 2023 zuwa 2024, rabon jihohi ya ƙaru da kashi 62%, yayin da na ƙananan hukumomi ya tashi da kashi 47%.

Sanwo-Olu ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa tabbatar da ’yancin cin gashin kai na ƙananan hukumomi, wanda kotun koli ta tabbatar. Ya ce wannan ci gaba ne babba a tarihin dimokuraɗiyyar Najeriya.

Ya ƙara da cewa mataki na gaba da shugaba Tinubu ke shirin ɗauka shi ne ƙirƙirar ’yan sandan jihohi, domin inganta tsaro a ƙasar nan.

A nasa jawabin, tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Pius Anyim, ya ce tattaunawa tsakanin gwamnati da jama’a muhimmin abu ne don nasarar manufofin gwamnati.

Shi ma mai shirya taron, Muhammad Yakubu, ya nuna tabbacin cewa gwamnatin Tinubu za ta kai Najeriya ga ci gaba, musamman a fannoni k**ar ilimi, noma, da gine-gine.

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa EFCC ta ayyana tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa kuma tsohon Ministan Albarkatun...
11/11/2025

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa EFCC ta ayyana tsohon Gwamnan Jihar Bayelsa kuma tsohon Ministan Albarkatun Man Fetur, Timipre Sylva, ana neman sa bisa zargin hada baki da karkatar da kudi har dala miliyan $14.8.

Mai magana da yawun EFCC, Dele Oyewale, ya bayyana cewa kudin da ake magana a kansu na cikin jarin da Hukumar Kula da Cigaban Cikin Gida ta Masana’antar Man Fetur (NCDMB) ta zuba a kamfanin Atlantic International Refinery and Petrochemical Limited domin gina matatar mai.

Kotun Babbar Jiha ta Legas ta bayar da sammacin k**a Sylva a ranar 6 ga watan Nuwamba, 2025.

Address

No. A1 Dantsoho Plaza, Abdullahi Bayero Road
Kano
700101

Telephone

+2348022400739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Times Hausa:

Share