Arewa Times Hausa

Arewa Times Hausa News/Media Website
(2)

Sanatan Amurka, Riley Moore, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa Amurka na shirin raba Najeriya gida biyu. A cikin wat...
07/02/2026

Sanatan Amurka, Riley Moore, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa Amurka na shirin raba Najeriya gida biyu.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Moore ya bayyana cewa duk da kasancewarsa a Najeriya inda ya yi ganawa da manyan jami’an gwamnati, batun raba ƙasar bai taɓa tasowa a tattaunawar ba.

Adawa Ko Gaskiya?Tsohon ɗan wasan baya na Liverpool, Jamie Carragher, ya soki Cristiano Ronaldo kan yadda yake yin hira ...
07/02/2026

Adawa Ko Gaskiya?

Tsohon ɗan wasan baya na Liverpool, Jamie Carragher, ya soki Cristiano Ronaldo kan yadda yake yin hira da kafafen yaɗa labarai, yana mai cewa hakan “abin kunya ne” ga ɗan wasa irinsa.

Carragher ya ce idan Ronaldo, a shekarunsa, yana shirya hirarraki da abokansa domin yin magana kan wasu lig-lig, masu horaswa da ’yan wasa, hakan na nuna rashin kwanciyar hankali.

Ya ƙara da cewa Ronaldo na daga cikin manyan ’yan wasa a tarihi kuma ba sai yana yin hirarraki akai-akai domin tabbatar da hakan ba, yana zargin cewa tambayoyin da ake yi masa a irin waɗannan hirarrakin an riga an tsara su.

Carragher ya kuma kwatanta hakan da Lionel Messi, yana mai cewa a hirarrakinsa, Messi yakan fi mayar da hankali kan iyalinsa, ƙungiyarsa da kuma ƙasarsa.

EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M. Inuwa, kan zargin wulakanta NairaHukumar Yaki da Cin Hanci da Rasha...
03/02/2026

EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M. Inuwa, kan zargin wulakanta Naira

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa EFCC ta cafke fitacciyar jarumar Kannywood, Samha M Inuwa, bisa zargin wulakanta kudin Najeriya (Naira), bayan wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta.

Rahotanni sun nuna cewa jami’an EFCC daga reshen Kano ne s**a k**a jarumar, kuma a halin yanzu tana tsare a hannun hukumar yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.

Mai magana da yawun EFCC, Dele Oyewale, ya tabbatar da kamen a Abuja, inda ya bayyana cewa an dauki matakin ne bayan bayyanar bidiyon da ke nuna Samha Inuwa tana goge majina daga hancinta da takardun kudi na Naira.

Oyewale ya kara da cewa da zarar an kammala bincike, EFCC za ta gurfanar da jarumar a gaban kotu domin ta fuskanci hukunci bisa laifin da ake zarginta da aikatawa.

Lamarin ya janyo cece-kuce a tsakanin al’umma, inda jama’a ke jiran matakin da kotu za ta dauka.

Yadda dubban al'umma s**a halarci jana'izar Sheik Usman Kusfa Zaria wato Rigi-Rigi.An gudanar da jana'izar da yammacin y...
02/02/2026

Yadda dubban al'umma s**a halarci jana'izar Sheik Usman Kusfa Zaria wato Rigi-Rigi.

An gudanar da jana'izar da yammacin yau Litinin a filin Low-cost da ke Zaria.

Daga Umar Idris ShuaibuTsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Hukumar Kula da Filayen...
02/02/2026

Daga Umar Idris Shuaibu

Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya karɓi Kakakin Gwamnan Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, tare da wasu shugabannin APC daga jihar a gidansa da ke Abuja.

Taron, wanda ya gudana a ƙarshen mako, na daga cikin jerin tuntuba da ake yi da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano, k**ar yadda wata sanarwa da Mohammed Garba, Shugaban Ma’aikata ga tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya fitar ta bayyana.

A cewar sanarwar, tawagar ta haɗa da Shugaban Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa, Hon. Anas Mukhtar Bello Dan Maliki, da kuma sauran fitattun shugabannin APC daga yankin.

Cikin hotuna: Rahotonni yanzu haka sun tabbatar da cewa an samu tashin gobara a kasuwar Singa, Bello Road da ke Kano.
02/02/2026

Cikin hotuna: Rahotonni yanzu haka sun tabbatar da cewa an samu tashin gobara a kasuwar Singa, Bello Road da ke Kano.

’Yan ta’adda sun banka wa ofishin ’yan sanda wuta, sun sace mutum 6 a NejaWasu gungun ’yan ta’adda sun banka wa ofishin ...
01/02/2026

’Yan ta’adda sun banka wa ofishin ’yan sanda wuta, sun sace mutum 6 a Neja

Wasu gungun ’yan ta’adda sun banka wa ofishin ’yan sanda wuta da ke garin Agwara, a hedikwatar Ƙaramar Hukumar Agwara da ke Jihar Nijar.

Harin wanda ya auku da asubahin ranar Lahadin ya rutsa da wasu mutum akalla shida da aka yi garkuwa da su.

Majiyoyi sun shaida wa Aminiya cewa maharan sun isa yankin da misalin ƙarfe 4:00 na asuba, inda s**a yi artabu da jami’an ’yan sanda da manyan mak**ai, lamarin da ya tilasta wa jami’an tserewa.

‘Dalilin da ya sa gwamnonin APC ba su damu da barazanar tsige Fubara ba’Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce sa...
30/01/2026

‘Dalilin da ya sa gwamnonin APC ba su damu da barazanar tsige Fubara ba’

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya ce sam gwamnonin APC ba su damu da yunkurin tsige Gwamnan Ribas, Siminalayi Fubara ba, saboda batun na gaban kotu.

Sule ya yi wannan bayani ne a ranar Alhamis a cikin shirin siyasa na Politics Today da tashar talabijin ta Channels ta watsa.

Gwamnatin Tarayya Za ta kashe Tiriliyan 1 a Aikin Titin Jirgin Kasa a birnin KanoGwamnatin Tarayyar Najeriya karkashin j...
30/01/2026

Gwamnatin Tarayya Za ta kashe Tiriliyan 1 a Aikin Titin Jirgin Kasa a birnin Kano

Gwamnatin Tarayyar Najeriya karkashin jagorancin Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ta shirya samar da katafaren aikin Titin Jirgin Kasa da zaa yi a birnin Kano.
Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya bayyana haka a yayin da yake tarbar tawagar wakilan jihar Kano a gasar AlKur'ani mai girma da aka yi a jihar Borno

Ministan Tsaron Najeriya ya kai ziyara kamfanin ƙera na’urorin tsaro na ASELSAN a TurkiyyaA yayin ziyarar da Shugaban Ƙa...
29/01/2026

Ministan Tsaron Najeriya ya kai ziyara kamfanin ƙera na’urorin tsaro na ASELSAN a Turkiyya

A yayin ziyarar da Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu ke yi a ƙasar Turkiyya, Ministan Tsaro Janar Christopher Musa (mai ritaya) tare da rakiyar Shugaban Hafsan Sojojin Sama, Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, sun kai ziyara zuwa kamfanin ASELSAN, wanda shi ne fitaccen kamfani na ƙera kayan tsaro a Turkiyya.

Sun samu tarba daga Shugaban Harkokin Tsaron Ƙasa na Turkiyya, Haluk Görgün, inda s**a gudanar da tattaunawa kan batutuwan haɗin gwiwa tsakanin Najeriya da Turkiyya a fannin tsaro.

Kamfanin ASELSAN na daga cikin manyan cibiyoyin ƙera na’urorin sadarwa na soji irin rada, kayan leƙen asiri, da na’urorin lantarki da ake amfani da su a ga sojojin ƙasa, sama da da ruwa.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Janar Musa da tawagarsa ya ce sun kuma gudanar da binciken aikace na wasu daga cikin na’urorin tsaron da kamfanin ke ƙerawa tare da nazartar sabbin hanyoyin haɗin kai domin ƙarfafa dangantakar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

Babu abin da aka sauya a cikin sabbin dokokin haraji — Akpabio Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya musanta ...
29/01/2026

Babu abin da aka sauya a cikin sabbin dokokin haraji — Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya musanta iƙirarin cewa an sauya sabbin dokokin haraji bayan Majalisar Tarayya ta amince da su.

Ya ce dokokin da Shugaba Bola Tinubu ya sanya wa hannu kuma aka wallafa a jaridar gwamnati su ne waɗanda ’yan majalisa s**a amince da su.

Akpabio, ya bayyana haka ne bayan wani ɗan Majalisar Tarayya, Abdussamad Dakuku, ya ce dokokin harajin da aka fitar sun bambanta da waɗanda majalisa ta amince da su.

Rundunar Sojin ƙasar nan ta ce Sojojinta na Operation WHIRL STROKE (OPWS) suna gano wata masana’antar ƙera mak**ai ba bi...
27/01/2026

Rundunar Sojin ƙasar nan ta ce Sojojinta na Operation WHIRL STROKE (OPWS) suna gano wata masana’antar ƙera mak**ai ba bisa ƙa’ida ba a yankin Agwatashi, ƙaramar hukumar Doma a Jihar Nasarawa.

Sojojin sun gano wurin ne yayin da suke gudanar da sintiri a yankin domin hana masu aikata laifuka yin kutse da samun ‘yancin motsi.

Sanarwar da rundunar ta fitar a shafinta na X ta bayyana cewa wurin an ɓoye shi ne domin ƙera mak**ai da ake bai wa masu aikata laifuka a cikin jihar da ma wajen ta.

Address

No. A1 Dantsoho Plaza, Abdullahi Bayero Road
Kano
700101

Telephone

+2348022400739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Times Hausa:

Share