Arewa Times Hausa

Arewa Times Hausa News/Media Website
(2)

‎Ronaldo Ya Zama Dan Wasan Kwallo Na Farko Da Ya Mallaki Dala Biliyan Ɗaya A Duniya ‎‎‎Tauraron ɗan wasan ƙwallo ɗan asa...
08/10/2025

‎Ronaldo Ya Zama Dan Wasan Kwallo Na Farko Da Ya Mallaki Dala Biliyan Ɗaya A Duniya


‎Tauraron ɗan wasan ƙwallo ɗan asalin Portugal, Cristiano Ronaldo ya kafa sabon tarihin zama biloniya na farko a fagen ƙwallon ƙafa a duniya.

‎Wannan cigaban ya zo wa ɗan wasan mai shekaru 40, sakamakon sabuwar kwantiragin da ya samu daga ƙungiyarsa ta Al-Nassr a Saudiyya a watan Yuni.

‎Sabon rahoton mujallar Bloomberg ta Amurka ya bayyana cewa Ronaldo na da arziƙin dala biliyan 1.4, saboda kwantiragin shekaru biyu da ya tsawaita da Al-Nassr.

‎Rahotanni na cewa Ronaldo zai samu albashin dala miliyan 230 duk shekara, wanda ya kai dala 650,000 duk rana, baya ga dala miliyan 32 da ya samu ta rattaba hannu kan kwantiragi.

‎Da ma dai shiga sahun gwaraza a tarihi ba sabon abu ne ga Cristiano Ronaldo a tsawon rayuwarsa ta ƙwararren ɗan ƙwallo.

‎Bayan lashe kofuna da dama ga ƙungiyoyin Turai kamar su Manchester United, Real Madrid, da Juventus, Ronaldo ya kasance wanda ya fi buga wa ƙasarsa wasa a tarihi.

‎Zuwa yanzu, ya zura ƙwallaye 946, sama da duk wani ɗan wasa a duniya.

‎Duk da cewa cikin 'yan ƙwallon ƙafa, Cristiano Ronaldo ne na farko da ya zama biloniya, a fannin wasannin motsa-jiki akwai waɗanda s**a riga shi cim ma wannan mataki.

‎Cikinsu akwai Roger Federer ɗan wasan tanis, da Tiger Woods ɗan wasan gwaf, da Michael Jordan da LeBron James ‘yan wasan ƙwallon kwando.

‎A halin yanzu dai, babban burin da ya ragewa gwarzon ɗan ƙwallon shi ne cika cin adadin ƙwallaye 1000 kafin ya yi ritaya daga ƙwallon ƙafa, inda yanzu ya rage masa ƙwallaye 54.

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shan Sh**ha‎‎‎‎Gwamnatin Kano ta sanar da haramta shan Sh**ha musamman wanda ya ƙunshi sanya ƙ...
08/10/2025

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shan Sh**ha



‎Gwamnatin Kano ta sanar da haramta shan Sh**ha musamman wanda ya ƙunshi sanya ƙwayoyin maye a ciki kafin a shan ta, tana mai ambata dalilai na kiyaye lafiyar al’umma da tarbiyarsu.


‎Hukumar shari’a ta jihar Kano ce ta sanar da hakan biyo bayan rahotonni da ke nuna matasa na amfani da Sh**ha wajen shan miyagun ƙwayoyi da sauran abubuwa da s**a saɓa da koyarwar addinin Musulunci.

‎A cewar hukumar, wannan mataki ya zama wajibi ne bayan rahotanni da Muhasa Radio ta haɗa wanda ya fito da yadda matasa ke cakula Sh**ha da ƙwayoyi da sauransu.


‎“Mun fahimci matasa na amfani da Sh**ha wajen yin abubuwa da s**a saɓa wa addini da al’ada. Wasu har suna cakuɗa ta da miyagun ƙwayoyi wanda ke illa ga jikinsu da ƙwaƙwalwarsu. Wannan ne abu da ba za mu lamunta ba,” a cewar wani babban jami’an hukumar shari’a.


‎Kano a baya ta haramta shan Sh**ha a ƙarƙashin gyaran wata doka ta hukumar yawon buɗe ido wadda tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, ya sanya wa hannu a shekarar 2021.


Jami'an tsaro sun Cafke wasu mutane biyu da suke kai wa ƴan bindigar daji kayan masarufi a jihar Kogi.
08/10/2025

Jami'an tsaro sun Cafke wasu mutane biyu da suke kai wa ƴan bindigar daji kayan masarufi a jihar Kogi.

Farashin Gas Ya Yi Tashin Gwauron Zabi A KanoMazauna birnin Kano sun bayyana ƙorafi da damuwa kan yadda farashin gas ɗin...
08/10/2025

Farashin Gas Ya Yi Tashin Gwauron Zabi A Kano

Mazauna birnin Kano sun bayyana ƙorafi da damuwa kan yadda farashin gas ɗin girki (LPG) ke ƙara tashin gwauron zabi, tare da ƙara tsananta karancin samunsa a kasuwa, lamarin da ke jefa su cikin ƙalubale wajen gudanar da ayyukan yau da kullum.

Rahoton da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya tattara a ranar Laraba ya nuna cewa, tashoshin sayar da gas da dama sun ƙare da kayayyaki, yayin da waɗanda ke buɗe kuma suke aiki ke cika da dogayen layukan masu saye.

A cikin kwanaki biyar kacal da s**a gabata, farashin gas ya ƙaru da kusan kashi 25%, inda kilogram ɗaya yanzu ke sayarwa tsakanin N1,800 zuwa N2,000, sabanin tsohon farashin da yake N1,200.

Haka kuma, cikon gas mai nauyin 12.5kg yanzu ya kai tsakanin N20,000 zuwa N25,000, sabanin N14,000 da ake biya a baya — lamarin da ya ƙara ɗora wa al’umma matsin tattalin arziki a lokaci da rayuwa ke ta tsada a sassa daban-daban naƙasar.

Ƙungiyar Shugabannin Jam’iyyun Siyasa a Najeriya (IPAC) ta ce lokaci ya yi da za a cire ikon naɗa shugaban Hukumar Zaɓe ...
07/10/2025

Ƙungiyar Shugabannin Jam’iyyun Siyasa a Najeriya (IPAC) ta ce lokaci ya yi da za a cire ikon naɗa shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) daga hannun shugaban ƙasa, domin ƙarfafa sahihanci da cin gashin kai na hukumar.

Shugaban ƙungiyar, Dakta Yusuf Mamman Ɗantalle, ne ya bayyana haka a yayin taron da kungiyar ta yi da kwamitin Majalisar Wakilai da ke nazarin kundin tsarin mulki a birnin Abuja.

Ɗantalle ya ce tsarin da ake amfani da shi yanzu wanda ke bai wa shugaban ƙasa ikon naɗa shugaban INEC, kwamishinoni da sakatare, na iya rage amincewar jama’a da sahihancin hukumar.

Za mu jajirce wajen tabbatar da kawo ƙarshen jinkirin shari’a a Jihar Kano.~Abdulkarim Kabir Maude, SANKwamishinan Shari...
07/10/2025

Za mu jajirce wajen tabbatar da kawo ƙarshen jinkirin shari’a a Jihar Kano.

~Abdulkarim Kabir Maude, SAN
Kwamishinan Shari’a na Jihar Kano

Mahmood Yakubu ya sauka daga kujerar Shugaban hukumar zaɓe ta INECFarfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga kujerar Shugaban ...
07/10/2025

Mahmood Yakubu ya sauka daga kujerar Shugaban hukumar zaɓe ta INEC

Farfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga kujerar Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).

Yakubu, wanda aka nada a shekarar 2015, ya yi wa’adin shekaru biyar sau biyu a ofis.

A ranar Talata, ya mika ragamar shugabanci ga May Agbamuche, kwamishina a hukumar, wacce za ta rike mukamin a matsayin mai rikon kwarya.

Tsohon shugaban hukumar ya roƙi tsofaffin abokan aikinsa da su ba wa mai rikon kwaryar cikakken hadin kai har zuwa lokacin da za a nada sabon shugaban hukuma na dindindin.

Ana sa ran Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai sanar da sabon shugaban hukumar zabe a kowanne lokaci daga yanzu.

Nadin sabon shugaban INEC na daga cikin muhimman batutuwan da ake sa ran za a tattauna a taron Council of State da aka shirya gudanarwa daga nan zuwa karshen mako.

Tsarin bashin kuɗin karatu ya haifar da tsadar kuɗin rijistar ɗalibai--RahotoHukumar bayar da tallafin kuɗin karatu ta N...
07/10/2025

Tsarin bashin kuɗin karatu ya haifar da tsadar kuɗin rijistar ɗalibai--Rahoto

Hukumar bayar da tallafin kuɗin karatu ta Najeriya (NELFUND) ta bayyana damuwa kan yadda wasu jami’o’i ke ƙara kuɗin makaranta da ya kai tsakanin kashi 20 zuwa 521 cikin ɗari.

Wani rahoton hukumar ya nuna cewa karin kuɗin karatu, musamman a fannoni irin su likitanci, malaman jinya, da lauya, yana jefa ɗalibai cikin wahala tare da kawo cikas ga aikin hukumar.

A cewar rahoton mai taken “Tsarin rage illar ƙarin kuɗin makarantu,” jami’o’in da abin ya shafa sun haɗa da:

Jami’ar Ilesha ta Osun

Jami’ar Jihar Ekiti

Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta Ondo

Jami’ar Edo

Jami’ar Fasaha ta Ladoke Akintola (LAUTECH), Oyo

Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta David Umahi (DUFUHS), Ebonyi

Wannan na zuwa ne watanni kaɗan bayan rahoton jaridar The Guardian da ya bayyana cewa jami’o’i 51 sun shiga cikin zargin cire kuɗi ba bisa ka’ida ba daga tsarin tallafin karatun.

A watan Yuli, rahoton ya kuma nuna cewa hukumar ta ki amincewa da buƙatun rance daga jami’o’i 10 saboda ƙarin kuɗin makaranta da ya kai har kashi 900 cikin ɗari.

Rahoton ya nuna misalan karin kuɗin kamar haka:

Jami’ar Ilesha: Kuɗin karatun ma'aikatan jinya ya tashi daga ₦825,000 zuwa ₦1.276m — ƙarin kashi 55%. Haka kuma fannin lauya ya tashi daga ₦1.276m zuwa ₦1.526m — ƙarin kashi 20%.

Jami’ar Jihar Ekiti: Fannin likitanci ya tashi daga ₦797,000 zuwa ₦1.132m — ƙarin kashi 42%.

Jami’ar Edo: Kuɗin likitanci ya tashi daga ₦3.25m zuwa ₦4.25m — ƙarin kashi 31%.

Wannan na nufin cewa ɗalibin likitanci a jami’ar Edo zai iya kammala karatu da bashin da ya kai sama da ₦51 miliyan.

Haka zalika, rahoton ya nuna cewa Jami’ar Kimiyyar Lafiya ta Ondo ta ƙara kuɗin karatu a wasu fannoni uku da ƙarin da ya kai tsakanin kashi 40 zuwa 149 cikin ɗari.

Rahoto Ya Bayyana Cewa Kananan Hukumomi 751 Cikin 774 A Najeriya Na Cikin Hadarin Cin Hanci Da Rashin GaskiyaWani sabon ...
07/10/2025

Rahoto Ya Bayyana Cewa Kananan Hukumomi 751 Cikin 774 A Najeriya Na Cikin Hadarin Cin Hanci Da Rashin Gaskiya

Wani sabon rahoto da Cibiyar Binciken Gaskiya da Tsabtace Harkokin Kudi (CFTPI) ta wallafa ya gano cewa mafi yawan kananan hukumomi a Najeriya na fama da matsalolin rashin gaskiya, boye bayanai, da kuma hadarin cin hanci da rashawa.

Rahoton mai taken “Nigerian Local Government Integrity Index (NLGII)” ya nuna cewa daga cikin kananan hukumomi 774 da ake da su a fadin kasar, 751 — wato kashi 85 cikin 100 — suna cikin rukuni mai “hadari sosai” ko “mai matuƙar hadari.” Rahoton ya danganta wannan mummunan matsayi da rashin bude bayanan kudi ga jama’a da kuma raunin aiwatar da dokokin da s**a shafi gaskiya da kulawa da kudaden jama’a.

Cikin kananan hukumomin da aka sanya cikin rukuni mafi hadari sun haɗa da Port Harcourt, Southern Ijaw, Ohaji/Egbema da Magu, yayin da kaɗan daga cikinsu kamar Nasarawa (Nasarawa LGA), Dutse, Ikeja da AMAC (FCT) s**a samu matsayin “mai kyau” bisa tsari da gudanarwa.

Shugaban CFTPI, Dr. Umar Yakubu, ya ce wannan shi ne rahoto na farko da ya gudanar da cikakken tantancewa kan gaskiya da hadarin cin hanci a matakin kananan hukumomi a Najeriya. Ya bukaci hukumomin yaki da cin hanci irin su EFCC da ICPC da su maida hankali kan kananan hukumomin da ke cikin rukuni mafi hadari domin dakile wannan matsala da wuri.

Shi ma shugaban ICPC, Dr. Musa Adamu Aliyu (SAN), ya yaba da rahoton, inda ya ce za su yi nazari kan sakamakon tare da amfani da shi wajen ƙarfafa shirin hukumar na Accountability and Corruption Prevention in Local Governments (ACCP-LG) domin ganin an inganta gaskiya da rage cin hanci a matakin ƙananan hukumomi.

Farashin gas ɗin girki yayi tashin gwaron zabiKamfanin mai na ƙasa, NNPCL, ya bayyana cewa tashin farashin gas na girki ...
06/10/2025

Farashin gas ɗin girki yayi tashin gwaron zabi

Kamfanin mai na ƙasa, NNPCL, ya bayyana cewa tashin farashin gas na girki da ake fuskanta a ƙasar nan ya samo asali ne daga yajin aikin ƙungiyar ma’aikatan man fetur (PENGASSAN).

Babban daraktan kamfanin, Bayo Ojulari, ne ya bayyana haka yayin ziyarar ban girma da ya kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar gwamnati.

A cewar Ojulari, yajin aikin ya haifar da tsaiko wajen jigilar kayayyaki, wanda ya janyo ƙarancin gas a kasuwa, sannan wasu dillalai s**a yi amfani da hakan wajen ƙara farashi.

> “Tashin farashin ya zama kamar na wucin gadi. Da zarar an kammala dawo da harkokin jigila yadda ya kamata, farashin zai dawo yadda yake a da,” in ji Ojulari.

Rahotanni sun nuna cewa a Lagos, kg ɗaya na gas ya kai ₦2,080, inda 12.5kg ke sayuwa a ₦26,000, yayin da a Iyana Ipaja ya kai ₦27,000.
A Abuja kuma, farashin ya tashi zuwa ₦20,000 don 12.5kg, wanda ke nufin ₦1,600/kg — ƙaruwa da fiye da kashi 48% daga tsohon farashin ₦17,500.

NNPC ta tabbatar da cewa yanzu da yajin aikin ya ƙare, farashin zai ragu a hankali yayin da dillalai ke ci gaba da karɓar sabon kaya daga cibiyoyin ajiya.

A ranar 1 ga Oktoba, ƙungiyar PENGASSAN ta dakatar da yajin aikin da ta shirya bayan sulhu da gwamnatin tarayya da kamfanin Dangote Refinery, inda aka amince da dawo da ma’aikatan da aka sallama.

Gwamnatin Jihar Kano ta yi gargadi ga iyaye da masu kula da yara wadanda ba sa son yi wa ‘ya’yansu alluran rigakafi, ind...
06/10/2025

Gwamnatin Jihar Kano ta yi gargadi ga iyaye da masu kula da yara wadanda ba sa son yi wa ‘ya’yansu alluran rigakafi, inda ta bayyana cewa za ta yi amfani da dokokin Najeriya don tabbatar da bin doka.

Kwamishinan Lafiya na Jihar, Dr. Abubakar Labaran Yusif, ne ya yi wannan gargadi, kafin a kaddamar da gaggamin yin rigakafin cututtuka biyu, wato kyanda da kyanda bi iska a jihar.

Dr. Labaran ya bayyana cewa cututtukan suna da matukar hadari, musamman kyanda bi iska, wadda ba a fiya gane yara ko mata masu ciki suna dauke da ita ba, amma na iya haifar da makanta, kurumta, ciwon zuciya da tabin hankali.

Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), Farfesa Adamu Ahmed, ya bayyana cewa jami’ar tana kashe sama da Naira biliya...
05/10/2025

Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello Zariya (ABU), Farfesa Adamu Ahmed, ya bayyana cewa jami’ar tana kashe sama da Naira biliyan 4 a duk shekara wajen samar da wutar lantarki, abin da ya bayyana a matsayin ba mai dorewa ba.

Da yake jawabi yayin bikin cika shekaru 63 da kafuwar jami’ar, Farfesa Ahmed ya ce Gwamnatin Tarayya ta bayar da gudunmawar Naira biliyan 1 ta hannun TETFund, domin tallafa wa jami’ar wajen samar da makamashi.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta amince da gina sabon shirin samar da wutar hasken rana mai ƙarfin megawatt 10.

Address

No. A1 Dantsoho Plaza, Abdullahi Bayero Road
Kano
700101

Telephone

+2348022400739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Times Hausa:

Share