21/11/2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Tarayya 41 Saboda Barazanar Tsaro
Gwamnatin Tarayya ta bayar da umarnin rufe makarantun 41 na tarayya (Federal Unity Colleges) nan take saboda ƙarin barazanar tsaro da aka samu a wasu sassan ƙasar nan.
Umarni na ƙunshe ne cikin wata takarda mai ɗauke da kwanan wata 21 ga watan Nuwamba, 2025, da Ma’aikatar Ilimi ta fitar, wace Babbar Daraktar Makarantun Sakandare, Hajiya Binta Abdulkadir, ta sanya wa hannu a madadin Ministan Ilimi.
Ta bayyana cewa an ɗauki matakin ne duba da ƙalubalen tsaro da ake samu a wasu yankuna, tare da buƙatar daƙile duk wata matsalar tsaro da ka iya shafar rayuwar ɗalibai da ma’aikata, musamman a wuraren da ake ganin suna da rauni.
Takardar ta kuma umarci shugabannin makarantun da abin ya shafa da su tabbatar da bin wannan umarni yadda ya k**ata.
Makarantun da aka rufe sun haɗa da FGGC Minjibir, FGC Ilorin, FTC Ganduje, FGGC Zaria, FTC Kafanchan, FGGC Bakori, FTC Dayi, FGC Daura, FGGC Tambuwal, FSC Sokoto, FTC Wurno, FGC Gusau, FGC Anka, FGGC Gwandu, FGC Birnin Yauri, FTC Zuru, FGGC Kazaure.
Sauran kuma su ne: FGC Kiyawa, FTC Hadejia, FGGC Bida, FGC New-Bussa, FTC Kuta-Shiroro, FGGC Omuaran, FTC Gwanara, FGC Ugwolawo, FGGC Kabba, FTC Ogugu, FGGC Bwari, FGC Rubochi, FGGC Abaji, FGGC Potiskum, FGC Buni Yadi, FTC Gashua, FTC Michika, FGC Ganye, FGC Azare, FTC Misau, FGGC Bajoga, FGC Billiri, da FTC Zambuk.
Sai dai ma’aikatar ilimin ba ta bayyana ranar da za a sake buɗe makarantun ba, amma ta ce an ɗauki matakin ne da zummar kare rayukan ɗaliban da sauran ma’aikata.