Arewa Times Hausa

Arewa Times Hausa News/Media Website
(2)

Hukumar kiyaye afkuwar haɗɗura ta ƙasa FRSC ta tura  ƙarin jami ai a babban titin Abuja zuwa Lokoja don saukaka cunkoson...
23/12/2025

Hukumar kiyaye afkuwar haɗɗura ta ƙasa FRSC ta tura ƙarin jami ai a babban titin Abuja zuwa Lokoja don saukaka cunkoson ababen hawa bayan da a ka samu cunkoso tsawon kwana biyu.

Matafiyan a kan titin da ya haɗa da arewaci da kudancin ƙasar sun maƙale a titin har tsawon kwanaki biyu saboda rashin kyan hanya da kuma ƙarin yawan tafiye-tafiye da a ke samu sak**akon karshen shekara.

Wani daga cikin matafiyan ya ce lalacewar titin da kuma rashin haƙurin masu ababen hawan ne ya janyo toshewar hanyar.

Tsaikon da ya dauki tsawon sa'o'i 48 ya fi tsanani a hanyar Katon Ƙarfe da ya janyo tsaiko ga matafiya.

Kazalika akwai rahotanni da su ka bayyana cewar wasu manyan motoci ne biyu su ka faɗi su ka toshe hanyar titin da su ka ta azzara cunkoson hanyar matafiyan.

Don tabbatar da an warware cunkoson kan titin shugaban hukumar Shehu Muhammad ya ba da umarnin tura ƙarin jami'an.

Kuma ya yi kira ga masu ababen hawan da matafiya da su baiwa jami an hukumar haɗin kai wajen warware matsalar.

Rundunar sojin Najeriya ƙarƙashin operation Haɗin Kai sun fatattaki yan boko haram da ƴan kungiyar ISWAP a jihar Borno, ...
23/12/2025

Rundunar sojin Najeriya ƙarƙashin operation Haɗin Kai sun fatattaki yan boko haram da ƴan kungiyar ISWAP a jihar Borno, tare da kashe yan ta adda 21 a yayin sumamen da su ka kai a garin Sojiri da Kayamla.

A wata sanarwa da rundunar sojin ta fitar yau Lahadi ta ce sumamen ya biyo bayan wata hikima da rundunar ta yi wa da ƴan boko haram sama da 100 wanda su ka shiga cikin unguwar da nufin kar hari.

Jami'an tsaron haɗin gwiwa da yan sa kai sun far wa yan Boko Haram din yayin da su ka zagayesu bayan samun bayanan sirri kan shirin harin da su kw ƙoƙarin kaiwa.

An yi musayar wuta a tsakai, kuma a yayin musayar wutar yan ta addan sun yi ƙoƙarin kai wa Rundunar sojin farmaki, wanda rundunar su ka yi nasara a kansu.

Biyo nasarar tasu antabbatar da sun kashe yan ta addan 21 da ragowar da a ke tunanin sun gudu da raunuka a jikinsu.

Daga cikin kayayyakin da su ka kwato akwai kekuna, kayayyakin abinci, magunguna, sabulai, kayan sawa, mak**ai da sauran su.

Jami'an sun ce za su ci gaba da aikin tabbatar da tsaro da kawar da ayyukan ta'addanci a jihar.

‎Dangote Ya Yi Barazanar Shigar Da Ƙarar Bisa Zargin Batanci Tare Da Neman Diyyar Bilyan 100 kan Ɗan Kasuwa A Kaduna‎‎‎S...
21/12/2025

‎Dangote Ya Yi Barazanar Shigar Da Ƙarar Bisa Zargin Batanci Tare Da Neman Diyyar Bilyan 100 kan Ɗan Kasuwa A Kaduna


‎Shugaban rukunin kamfanonin Dangote Group, Aliko Dangote, ya bai wa wani ɗan kasuwa da ke jihar Kaduna, Kailani Mohammed, wa’adin kwanaki 7 domin ya janye wata wallafa da ake zargin ta ɓata suna tare da neman afuwa a bainar jama’a.

‎Dangote ya bayyana cewa idan har Engr. Kailani Mohammed bai janye kalaman da ya yi ba, kuma bai gyara zargin da ya shafi shi da harkokin kasuwancinsa ba, to ba zai yi ƙasa a gwiwa ba wajen shigar da ƙarar batanci (libel) a kotu, inda zai nemi diya ta naira biliyan 100 (₦100bn).

‎A cewar sanarwar da aka fitar daga lauyoyin Dangote, zargin da aka wallafa ba shi da tushe, kuma yana da illa ga mutunci da martabar sa da kuma sunan kamfanoninsa a idon jama’a da kasuwanci.

Gwamnatin Nijeriya ta ce an saki ragowar ɗalibai 130 na makarantar sakandaren St Mary da ke Papiri a Jihar Neja, waɗanda...
21/12/2025

Gwamnatin Nijeriya ta ce an saki ragowar ɗalibai 130 na makarantar sakandaren St Mary da ke Papiri a Jihar Neja, waɗanda s**a rage a hannun waɗanda s**a yi garkuwa da su a ranar 21 ga watan Nuwamba.

Mai bai wa Shugaban Nijeriya shawara na musamman kan harkokin watsa labarai Bayo Onanuga ya wallafa hotuna ɗaliban biyu a cikin motoci a shafinsa na X, inda ya ce ana sa ran za su ƙarasa Minna babban birnin Jihar Neja ranar Litinin.

Ya ce dama tuni aka saki 100, abin da ya kai adadin ɗaliban da aka saki zuwa 230.

Onanuga ya ce an saki ɗaliban ne sak**akon aikin ɓangaren tattara bayanan sirri na rundunar sojin Nijeriya.

‎Jami’an NAFDAC Sun Yi Gargadi A Daina Cin  Indomie Mai Ɗanɗanon Kayan Lanbu‎‎‎‎Jami’an Hukumar Kula da Abinci da Magung...
21/12/2025

‎Jami’an NAFDAC Sun Yi Gargadi A Daina Cin Indomie Mai Ɗanɗanon Kayan Lanbu



‎Jami’an Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) sun ayyana taliyar Indomie mai dandanon ganyayyaki (Vegetable Flavour) a matsayin abinci mai hadadri ga lafiyar mutane, ta umarci a bi kasuwanni a kwashe su kaff don kiyaye lafiyar mutane,

‎A cikin Sanarwa mai Lamba 041/2025 da aka wallafa a ranar Juma’a, NAFDAC ta ce hukumar kare lafiyar masu saye ta Faransa, Rappel Conso, ta bayar da umarnin janye Indomie mai ɗanɗanon kayan lambu bayan gwaje-gwaje sun tabbatar da kasancewar sinadaran da ba a bayyana ba, musamman madara da ƙwai, a cikin samfurin.


‎Waɗannan sinadaran ba a ambace su a jikin lakabin samfurin ba, lamarin da ke haifar da barazana ga lafiyar mutanen da ke da samun matsala da wasu abinci (allergy) ko matsalar jure wasu sinadarai, inda hakan ka iya jawo mummunan lahani ga lafiyarsu.

Gwamnatin Kano ta umarci jami'an tsaro su dakatar da masu yunkurin kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta  Gwamnatin Jihar ...
13/12/2025

Gwamnatin Kano ta umarci jami'an tsaro su dakatar da masu yunkurin kafa hukumar Hisbah mai zaman kanta

Gwamnatin Jihar Kano ta fitar da umarnin zartarwa da ya haramta wata kungiya da ke aiki da sunan “Independent Hisbah Fisabilillahi”.

Wannan umarni da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu, mai dauke da ranar 8 ga Disamba, 2025, ya bayyana cewa gwamnati ta gano cewa ana ci gaba da daukar ma’aikata, horaswa da tura matasa cikin kungiyar ba tare da wata doka ko izini ba, kana kuma cikin sabawa dokar Hukumar Hisbah ta Jihar Kano.

Yayin da yake mika sakon ga manema labarai, Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana cewa Hukumar Hisbah ce kadai hukuma ta doka da ke da ikon jagorantar dukkan ayyukan Hisbah a fadin jihar.

Gwamnati ta ce bullar wannan kungiya ta daban wani yunkuri ne na kafa wata hukuma ba bisa ka’ida ba, lamarin da zai iya haifar da tashin hankali da kuma take matsayin hukumar Hisbah ta jihar.

Gwamnan ya kuma bayyana dukkan ayyukan kungiyar a matsayin “haramtattu, ba bisa doka ba kuma babu inganci,” yana gargadin cewa duk wani kaya da ya yi k**anceceniya da alamomi ko ikon Hukumar Hisbah zai fuskanci hukunci.

Gwamna Yusuf ya umarci Rundunar ‘Yansanda ta Najeriya, Hukumar DSS, NSCDC da sauran hukumomin tsaro da su binciki wadanda ke goyon bayan kungiyar, su dakatar da duk wani ci gaba da ake yi na daukar ma’aikata ko horaswa, sannan su dauki matakan da s**a dace don hana tabarbarewar tsaro.

Cif Jojin Jihar Filato, Mai Shari’a David Mann, ya yanke wa  wani ɗan sanda, Sajan Ruya Auta, hukuncin kisa bayan ya sam...
10/12/2025

Cif Jojin Jihar Filato, Mai Shari’a David Mann, ya yanke wa wani ɗan sanda, Sajan Ruya Auta, hukuncin kisa bayan ya same shi da laifin kashe wani ɗalibin jami’ar Jos mai karatu a matakin shekara ta uku, Rinji Bala.

Kotun ta ce hukuncin ya biyo bayan shaidun da aka gabatar da kuma nazarin yanayin lamarin, domin tabbatar da doka da hukunta amfani da karfin bindiga ba bisa ka’ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa a ranar 12 ga Mayu, 2020, Bala da abokansa biyu sun gamu da jami’an tsaro a lokacin kulle Korona ko COVID-19 a unguwar Hwolshe, Jos.

Duk da babu wani abin zargi da aka samu a kansu, an k**a su, aka yi musu duka, sannan aka sallame su tare da umurtan su da su gudu. A lokacin ne Auta ya harbi Bala a bayansa, wanda ya yi sanadin mutuwarsa nan take.

Lauyan gwamnati, Dr. Garba Pwul (SAN), ya ce hukuncin ya tabbatar da adalci, yayin da mahaifin marigayin, Peter Bala, yace duk da ba a murna da mutuwar wani, amma dole a bar doka ta yi aikinta.

Ya kuma yi fatan hukuncin zai zama izina ga jami’an tsaro masu sakaci a cikin aikin su.

Gwamnatin Nijeriya ta karɓo ɗalibai 100 cikin waɗanda aka sace daga makarantar St. Mary’s Private Catholic Primary and S...
08/12/2025

Gwamnatin Nijeriya ta karɓo ɗalibai 100 cikin waɗanda aka sace daga makarantar St. Mary’s Private Catholic Primary and Secondary School da ke ta ƙauyen Papiri ƙaramar hukumar Agwara a Jihar Neja.

Kafofin watsa labaran Nijeriya ne s**a ambato majiyoyin tsaro da hukumomin Nijeriya suna tabbatar da sakin ɗaliban ranar Lahadi.

Sojoji a Jamhuriyar Benin sun sanar da kifar da gwamnati kasar, tare da kwace iko da duk ma'aikatu da hukumomin gwamnati...
07/12/2025

Sojoji a Jamhuriyar Benin sun sanar da kifar da gwamnati kasar, tare da kwace iko da duk ma'aikatu da hukumomin gwamnati.

Jagoran sojojin Laftanar Kanar Pascal Tigri ne sanar da hakan a wani shiri na kai tsaye da aka yada a gidan talabijin na ƙasar, a safiyar yau Lahadi.

Rahotanni sun bayyana cewa tun da sanyin safiya sojoji s**a mamaye gidan shugaban kasar Patrice Talon, tare da wasu muhimman wurare a Cotonou.

Jirgin sojojin Najeriya ya yi hatsari a jihar NejaRahotanni daga jihar Neja sun tabbatar da cewa wani jirgin yaki na run...
06/12/2025

Jirgin sojojin Najeriya ya yi hatsari a jihar Neja

Rahotanni daga jihar Neja sun tabbatar da cewa wani jirgin yaki na rundunar sojin saman Najeriya (NAF) ya yi hatsari a kusa da kauyen Karabonde, cikin ƙaramar hukumar Borgu.

Wani shafin kafar yaɗa Labarai na cikin jihar, Lapai TV, ya wallafa cewa matukan jirgin biyu sun samu damar ficewa daga cikin jirgin kafin ya faɗi. Wannan na cikin wani gajeren bidiyo mai tsawon daƙiƙa 57 da aka saki a daren Asabar.

Wani ganau ya bayyana cewa jirgin na iya kasancewa ya tashi ne daga sansanin sojin saman Kainji kafin faruwar lamarin.

Ya ce: “Mun samu labarin cewa rundunar sojin sama ta tura jami’anta zuwa wurin da hatsarin ya faru.”

Wani mazaunin yankin, Lukman Sulaiman, ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 4:10 na yamma.

Hukumar da ke yi wa Kamfanonin Rajista a Nijeriya ta yi gargaɗi game da masu gudanar da sana'ar POS ba tare da rajista b...
06/12/2025

Hukumar da ke yi wa Kamfanonin Rajista a Nijeriya ta yi gargaɗi game da masu gudanar da sana'ar POS ba tare da rajista ba inda ta ce daga Janairun 2026, jami'an tsaro za su fara rufe duk wani wurin sana’ar POS maras rajista.

Gwamnatin Kano ta yi Alla-Wadai da k**a  Muhuyi Magaji da ƴansanda s**a yiGwamnatin Jihar Kano ta nuna damuwa kan k**a t...
05/12/2025

Gwamnatin Kano ta yi Alla-Wadai da k**a Muhuyi Magaji da ƴansanda s**a yi

Gwamnatin Jihar Kano ta nuna damuwa kan k**a tsohon shugaban Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta jihar Kano PCACC, Muhuyi Magaji Rimin Gado, da rundunar ‘yansanda ta yi ba tare da gabatar da takardar kamu ko umarnin kotu ba.

A wata sanarwa da Antoni Janar na Jihar ya fitar, rahotanni sun ce an k**a Muhyi a ofishinsa na aikin lauya da ke kan titin Zaria kafin a tafi da shi zuwa Abuja, duk da cewa akwai umarnin kotu da ya hana hakan.

Gwamnati ta bayyana lamarin a matsayin barazana ga tsarin mulki da hakkin dan Adam, tana zargin cewa wasu ‘yan siyasa na kokarin amfani da hukumomin tsaro don haifar da matsala a jihar.

Sanarwar ta ce ana ganin kamen na da alaka da wasu manyan bincike da shari’o’in cin hanci da Magaji ke da muhimman bayanai a kansu.

Gwamnatin Kano ta bukaci ‘yansanda su bayyana dalilin k**a shi, tare da jaddada bukatar bin doka da kare hakkin jama’a, tana kuma kiran jama’a da su zauna lafiya yayin da ta ci gaba da bibiyar lamarin.

Address

No. A1 Dantsoho Plaza, Abdullahi Bayero Road
Kano
700101

Telephone

+2348022400739

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Times Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Times Hausa:

Share