23/12/2025
Hukumar kiyaye afkuwar haɗɗura ta ƙasa FRSC ta tura ƙarin jami ai a babban titin Abuja zuwa Lokoja don saukaka cunkoson ababen hawa bayan da a ka samu cunkoso tsawon kwana biyu.
Matafiyan a kan titin da ya haɗa da arewaci da kudancin ƙasar sun maƙale a titin har tsawon kwanaki biyu saboda rashin kyan hanya da kuma ƙarin yawan tafiye-tafiye da a ke samu sak**akon karshen shekara.
Wani daga cikin matafiyan ya ce lalacewar titin da kuma rashin haƙurin masu ababen hawan ne ya janyo toshewar hanyar.
Tsaikon da ya dauki tsawon sa'o'i 48 ya fi tsanani a hanyar Katon Ƙarfe da ya janyo tsaiko ga matafiya.
Kazalika akwai rahotanni da su ka bayyana cewar wasu manyan motoci ne biyu su ka faɗi su ka toshe hanyar titin da su ka ta azzara cunkoson hanyar matafiyan.
Don tabbatar da an warware cunkoson kan titin shugaban hukumar Shehu Muhammad ya ba da umarnin tura ƙarin jami'an.
Kuma ya yi kira ga masu ababen hawan da matafiya da su baiwa jami an hukumar haɗin kai wajen warware matsalar.