02/02/2026
Daga Umar Idris Shuaibu
Tsohon Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Gudanarwa na Hukumar Kula da Filayen Jiragen Sama ta Ƙasa (FAAN), Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya karɓi Kakakin Gwamnan Jihar Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa, tare da wasu shugabannin APC daga jihar a gidansa da ke Abuja.
Taron, wanda ya gudana a ƙarshen mako, na daga cikin jerin tuntuba da ake yi da manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano, k**ar yadda wata sanarwa da Mohammed Garba, Shugaban Ma’aikata ga tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya fitar ta bayyana.
A cewar sanarwar, tawagar ta haɗa da Shugaban Ƙaramar Hukumar Dawakin Tofa, Hon. Anas Mukhtar Bello Dan Maliki, da kuma sauran fitattun shugabannin APC daga yankin.