17/02/2026
"Ba za mu bari kowa ya zalunce mu ba, ko ya haɗa baki da wasu domin cutar da mu ko tauye haƙƙin mutanenmu a Doguwa da Tudun Wada".
"Idan akwai wani yanki kai tsaye na jam’iyyar APC a Jihar Kano, to Doguwa da Tudun Wada ne. Saboda haka babu dalilin da zai sa wani munafuki, komai girmansa, ya je ya haɗa baki da wasu domin hana mu haƙƙin ƙaramar hukumar Tudun Wada a hannun ’yan asalin jam’iyyar APC".
"Za mu yi duk mai yiwuwa wajen tabbatar da Mai Girma Gwamna Engr. Abba Kabir Yusuf ya cika alkawarin da ya yi wa kowa na zama shugaba mai adalci. Kuma tabbas Mai Girma Gwamna zai same mu masu aminci tare da tabbatar da nasararsa a zaɓe mai zuwa, Insha Allah", in ji Hon. Alhassan Ado Doguwa.