04/09/2025
Hukumar Alhazai ta Jihar Gombe Ta Bukaci Masu Niyyar zuwa Haji Su Fara Biyan Kudin Ajiya Da Wuri, Yayin da Aka Ware Kujeru 1,631 Domin Aikin Hajjin 2026
Daga Abdulkadir Aliyu Shehu, Gombe
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe ta bukaci dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajjin shekarar 2026 da su fara biyan kudin ajiya tun da wuri, kafin ayyyna ciakken kudin gaba ɗaya a watan Oktoba.
Sakataren Hukumar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake jawabi ga jami’an aikin Hajji na kananan hukumomi a ofishinsa a ranar Alhamis da ta gabata.
Ya bayyana cewa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta ware kujeru 1,631 ga jihar Gombe domin aikin Hajjin mai zuwa.
“Za a fara karɓar kuɗin ajiya nan da nan, kuma za a rufe ranar 5 ga Oktoba, 2025,” in ji Alhaji Hassan.
“Muna kira ga duk masu niyyar tafiya su biya akan lokaci domin shirye-shiryen su tafi daidai da umarnin hukumomin Saudiyya.”
Ya bayyana cewa NAHCON ta sanya kuɗin farko na aikin Hajjin 2026 akan naira miliyan 8 da dubu 400 (₦8,400,000). Duk da cewa za a fitar da cikakken kudin a watan Oktoba, ya jaddada cewa biyan kuɗi da wuri na da matuƙar muhimmanci wajen samun sauƙin gudanar da shirye-shirye.
Sakataren ya yi nuni da cewa dole a biya ta hannun jami’an aikin Hajji na kananan hukumomi, Bankin Ja’iz, ko Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe kawai.
Ya ce, biyan kuɗi tun da wuri zai baiwa Hukumar damar tabbatar da masauki, sufuri, da abinci tun kafin lokaci. Ya ƙara da cewa shirye-shiryen aikin Hajji dole ne su kasance cikin jadawalin da hukumomin Saudiyya s**a tanada, wanda hakan zai yiwu ne kawai idan alhazai s**a biya kuɗaɗensu da wuri.
Alhaji Hassan ya tabbatar wa masu niyyar tafiya cewa Hukumar za ta ci gaba da zama masu gaskiya da bayyana duk abin da ta ke gudanarwa da kuɗaɗen ajiya.
Ya ƙara da cewa shirye-shirye tun da wuri za su baiwa Hukumar da NAHCON damar samun mafi ingancin hidima a ƙasar Saudiyya, wanda hakan zai taimaka wajen kyautata jin daɗi da walwalar alhazai daga jihar Gombe.
“Burinmu shi ne mu sanya tafiyar ta kasance mai sauƙi da kuma cike da lada na ibada,” in ji shi. “Wannan kuwa ba zai yiwu ba sai idan alhazai s**a tallafa wa tsarin ta hanyar biyan kuɗaɗensu akan lokaci.”
Sakataren ya kuma yi kira ga masu rike da sarautun gargajiya, shugabannin addini, da sauran jagororin al’umma da su taimaka wajen wayar da kan al’umma game da muhimmancin biyan kuɗi cikin wa’adin da aka kayyade.
Ya yaba da haɗin kai da masu aikin Hajji s**a nuna a baya, tare da bayyana fatansa cewa Gombe za ta ci gaba da riƙe martabarta na yin aikin Hajji cikin nasara.
“Jihar Gombe ta dade tana samun yabo wajen tsare-tsaren aikin Hajji.
Muna son mu ci gaba da wannan daraja a shekarar 2026 tare da goyon bayan alhazai,” in ji shi.
Alhaji Hassan ya jaddada cewa Hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da NAHCON da kuma hukumomin Saudiyya domin tabbatar da an kammala dukkan shirye-shiryen tafiya cikin tsari.
Ya bayyana cewa kula da lafiya, masauki, abinci da sufuri sune manyan abubuwan da Hukumar ta fi mai da hankali akai, tare da tabbatar wa masu niyyar tafiya cewa ba za a bar wani abu a baya ba wajen ganin an samu aikin Hajji mai sauƙi da kwanciyar hankali a shekarar 2026.
A ƙarshe, Sakataren ya roƙi albarkar Allah ga duk masu niyyar tafiya, tare da jan hankalinsu da su shirya ba kawai ta fuskar kuɗi ba, har ma da ta fuskar ruhaniya domin gudanar da wannan ibada mai tsarki.
“Sakonmu yana da sauƙi: ku biya da wuri, ku shirya da wuri, mu yi aiki tare domin samun nasarar aikin Hajji,” in ji shi.