Haji Ayarin Allah

Haji Ayarin Allah Mun samar da wannan kafa ne domin kawo muku labaran harkokin ayyukan Haji da Umrah

05/10/2025

Sakon Shugaban NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Usman ga 'yan Jaridu

Shugaban  Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Sale Usman tare da tawagarsa sun gana da Darakta Janar na ...
25/09/2025

Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Sale Usman tare da tawagarsa sun gana da Darakta Janar na Harkokin Alhaji a Ma’aikatar Hajj da Umrah a Jeddah domin gabatar da wasu bukatu da za su taimakawa Najeriya wajen shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji mai zuwa.

Shugaban ya nemi goyon bayan Ma’aikatar wajen tsara komai tun da wuri.

A nasa jawabin, Darakta Janar, Abdallah As-Sheehri ya yi alkawarin gabatar da wasu daga cikin bukatun ga hukumomin da s**a dace. Sai dai ya shawarci shugabancin hukumar Alhazai ta Najeriya da su kiyaye sabbin manufofin Saudiyya musamman wajen cika wa’adin da aka gindaya

NAHCON Ta Bayyana Manyan Nasarori Da Ta Cimma a Ayyukan Hajji a Zamanin Gwamnatin Renewed HopeShugaban Hukumar Kula da A...
17/09/2025

NAHCON Ta Bayyana Manyan Nasarori Da Ta Cimma a Ayyukan Hajji a Zamanin Gwamnatin Renewed Hope

Shugaban Hukumar Kula da Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana muhimman nasarorin da hukumar ta samu a karkashin gwamnatin Renewed Hope ta shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, tare da tabbatar da cewa jin daɗin maniyyata na ci gaba da kasancewa a sahun gaba.

Farfesa Usman ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma a Katsina, inda ya yi cikakken bayani kan gyare-gyare da matakan da aka ɗauka wajen inganta gudanar da aikin Hajji a Najeriya.

A cewarsa, duk da ƙalubalen tattalin arziki da ake fuskanta, hukumar tare da goyon bayan shugaban ƙasa, ta aiwatar da muhimman matakai da s**a tabbatar da nasarar aikin Hajjin 2024 tare da kawo sauƙi ga maniyyatan Najeriya.

Shugaban hukumar ya bayyana cewa shugaban ƙasa ya amince da naira biliyan 90 domin rage tasirin hauhawar darajar kuɗin waje a kuɗaɗen aikin Hajjin 2024, da kuma ƙarin naira biliyan 24 domin biyan bashin da ya rage daga kamfanonin jiragen sama na 2023. Wannan mataki, a cewarsa, ya ceci kamfanonin jiragen sama na cikin gida daga rugujewa kuma ya tabbatar da gudanar da jigilar maniyyata cikin nasara.

Haka kuma, ya bayyana cewa shugaban ƙasa ya umurci dukkan kamfanonin jiragen sama da ke da hannu a aikin Hajji da su karɓi kuɗi a naira, wanda hakan ya kare maniyyata daga ƙarin radadin hauhawar darajar kuɗin waje.

Dangane da gyare-gyare, Farfesa Usman ya ce hukumar ta dakatar da tsarin katin kuɗin (credit card) na babban bankin ƙasa (CBN) wajen bayar da kuɗin tafiya (BTA), wanda ya jefa maniyyata da dama cikin wahala, sannan aka faɗaɗa tsarin Hajj Saving Scheme domin baiwa masu niyyar zuwa Hajji damar tara kuɗaɗensu a hankali.

A kan gaskiya da nuna riƙon amana, hukumar ta mayar da naira biliyan 5.3 ga hukumomin kula da alhazai na jihohi bisa sabis ɗin da ba a samu ba a lokacin Hajjin 2023.

Game da jin daɗi da tsare-tsare, shugaban hukumar ya bayyana cewa NAHCON ta samu nasarar samar da VIP Tent ‘A+’, ta daidaita kwangiloli daidai da adadin maniyyata, tare da tabbatar da cewa kusan kashi 98% na magunguna an samar da su, yayin da aka tura jami’an lafiya cikakke zuwa ƙasar Saudiyya.

Farfesa Usman ya jaddada cewa maniyyata na Najeriya sun sami gagarumar ragi a kuɗaɗen da s**a kashe a wannan shekarar. Ya ce akwai ragin Riyal 720 a sabis na Mashair, Riyal 200 a masaukin Madina, Riyal 303 a sufuri, da kuma rage farashin jiragen sama a dukkan yankuna.

“Wadannan nasarorin,” in ji shi, “na nuna hangen nesa na shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da kuma goyon bayan shugabanni kamar Gwamna Dikko Umar Radda. Tare da ci gaba da haɗin kai, NAHCON za ta ci gaba da inganta waɗannan nasarori tare da tabbatar da ƙarin jin daɗin maniyyata.”

Masu lura da jawabin sun ce wannan rahoto na shugaban NAHCON ya tabbatar da jajircewar hukumar wajen gudanar da aikin Hajji bisa ƙa’idojin duniya tare da rage wa maniyyatan Najeriya nauyin kuɗi.

Tsohon Alhaji Ya Kare Shugaban NAHCON, Ya Yaba da Hajjin 2025Wani Alhaji, Muhammad Suleman Gama, ya kare Shugaban Hukuma...
10/09/2025

Tsohon Alhaji Ya Kare Shugaban NAHCON, Ya Yaba da Hajjin 2025

Wani Alhaji, Muhammad Suleman Gama, ya kare Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman ,kan abin da ya bayyana a matsayin “tuhume-tuhumen banza” daga wasu mutane masu neman biyan buƙatun kansu.

Gama, wanda ya ce ya yi aikin Hajji fiye da sau 20, ciki har da na bana, ya bayyana cewa Hajjin 2025 ƙarƙashin shugabancin NAHCON ya samu gagarumar nasara musamman wajen kula da walwalar alhazai da ingancin ayyuka.

A cewarsa, an tsara batun masauki, abinci, sufuri da kuma hulɗar diflomasiyya da hukumomin Saudiyya yadda ya dace, lamarin da ya sa wannan hajji ya zama ɗaya daga cikin mafi nasara a ‘yan shekarun nan.

“Abin takaici ne yadda wasu mutane marasa kishi ke ƙoƙarin bata sunan Shugaban NAHCON kawai don sun kasa samun mukamai ko kuma ba a amince da buƙatunsu na kai-tsaye ba,” in ji shi.

Ya zargi ɗaya daga cikin masu s**a da cewa shi ne ya taɓa yin lallami na neman aiki a NAHCON amma bai samu ba, daga bisani ya fara wallafa sharhi marasa inganci ba tare da ya halarci aikin Hajji ba.

“Idan dai wani daga cikin alhazan da s**a halarci aikin Hajji na bana ne ya yi s**a, za mu fahimta.

Amma wani da bai shiga aikin ba ya yi ƙarya yana bata suna, hakan ba adalci ba ne,” ya ƙara da cewa.

Dangane da ikirarin cewa Farfesa Sale ya yi watsi da gudunmawar wasu ƙungiyoyin addini, Gama ya ce wannan “ƙarya ce”, yana mai bayyana cewa a karon farko, NAHCON ta haɗa malamai daga kowane bangare don tallafa wa alhazai a Makka, Madina da Mina.

Haka kuma, ya yi kira ga masu s**a da su bari Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) da sauran hukumomi su kammala bincikensu kafin yanke hukunci, yana gargadi kan hare-haren son zuciya da ka iya lalata martabar hukumar.

“Farfesa Abdullahi yana fuskantar s**a marasa tushe ne kawai saboda wasu ba sa son shi a wannan kujera. Ya kamata su bar shi ya nuna kwarewarsa kafin su yanke hukunci,” in ji shi.

Wannan gogaggen Alhaji ya bukaci masu ruwa da tsaki da su gane nasarorin da aka samu a aikin Hajjin 2025, yana mai jaddada cewa duk wani jagora da ya ke da muhimmiyar alhakin ƙasa dole ya fuskanci yabo da s**a.

Hukumar Alhazai ta Jihar Gombe Ta Bukaci Masu Niyyar zuwa Haji Su Fara Biyan Kudin Ajiya Da Wuri, Yayin da Aka Ware Kuje...
04/09/2025

Hukumar Alhazai ta Jihar Gombe Ta Bukaci Masu Niyyar zuwa Haji Su Fara Biyan Kudin Ajiya Da Wuri, Yayin da Aka Ware Kujeru 1,631 Domin Aikin Hajjin 2026

Daga Abdulkadir Aliyu Shehu, Gombe

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe ta bukaci dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajjin shekarar 2026 da su fara biyan kudin ajiya tun da wuri, kafin ayyyna ciakken kudin gaba ɗaya a watan Oktoba.

Sakataren Hukumar, Alhaji Sa’adu Hassan, ya yi wannan kira ne a lokacin da yake jawabi ga jami’an aikin Hajji na kananan hukumomi a ofishinsa a ranar Alhamis da ta gabata.

Ya bayyana cewa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta ware kujeru 1,631 ga jihar Gombe domin aikin Hajjin mai zuwa.

“Za a fara karɓar kuɗin ajiya nan da nan, kuma za a rufe ranar 5 ga Oktoba, 2025,” in ji Alhaji Hassan.

“Muna kira ga duk masu niyyar tafiya su biya akan lokaci domin shirye-shiryen su tafi daidai da umarnin hukumomin Saudiyya.”

Ya bayyana cewa NAHCON ta sanya kuɗin farko na aikin Hajjin 2026 akan naira miliyan 8 da dubu 400 (₦8,400,000). Duk da cewa za a fitar da cikakken kudin a watan Oktoba, ya jaddada cewa biyan kuɗi da wuri na da matuƙar muhimmanci wajen samun sauƙin gudanar da shirye-shirye.

Sakataren ya yi nuni da cewa dole a biya ta hannun jami’an aikin Hajji na kananan hukumomi, Bankin Ja’iz, ko Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Gombe kawai.

Ya ce, biyan kuɗi tun da wuri zai baiwa Hukumar damar tabbatar da masauki, sufuri, da abinci tun kafin lokaci. Ya ƙara da cewa shirye-shiryen aikin Hajji dole ne su kasance cikin jadawalin da hukumomin Saudiyya s**a tanada, wanda hakan zai yiwu ne kawai idan alhazai s**a biya kuɗaɗensu da wuri.

Alhaji Hassan ya tabbatar wa masu niyyar tafiya cewa Hukumar za ta ci gaba da zama masu gaskiya da bayyana duk abin da ta ke gudanarwa da kuɗaɗen ajiya.

Ya ƙara da cewa shirye-shirye tun da wuri za su baiwa Hukumar da NAHCON damar samun mafi ingancin hidima a ƙasar Saudiyya, wanda hakan zai taimaka wajen kyautata jin daɗi da walwalar alhazai daga jihar Gombe.

“Burinmu shi ne mu sanya tafiyar ta kasance mai sauƙi da kuma cike da lada na ibada,” in ji shi. “Wannan kuwa ba zai yiwu ba sai idan alhazai s**a tallafa wa tsarin ta hanyar biyan kuɗaɗensu akan lokaci.”

Sakataren ya kuma yi kira ga masu rike da sarautun gargajiya, shugabannin addini, da sauran jagororin al’umma da su taimaka wajen wayar da kan al’umma game da muhimmancin biyan kuɗi cikin wa’adin da aka kayyade.

Ya yaba da haɗin kai da masu aikin Hajji s**a nuna a baya, tare da bayyana fatansa cewa Gombe za ta ci gaba da riƙe martabarta na yin aikin Hajji cikin nasara.

“Jihar Gombe ta dade tana samun yabo wajen tsare-tsaren aikin Hajji.

Muna son mu ci gaba da wannan daraja a shekarar 2026 tare da goyon bayan alhazai,” in ji shi.

Alhaji Hassan ya jaddada cewa Hukumar za ta yi aiki kafada da kafada da NAHCON da kuma hukumomin Saudiyya domin tabbatar da an kammala dukkan shirye-shiryen tafiya cikin tsari.

Ya bayyana cewa kula da lafiya, masauki, abinci da sufuri sune manyan abubuwan da Hukumar ta fi mai da hankali akai, tare da tabbatar wa masu niyyar tafiya cewa ba za a bar wani abu a baya ba wajen ganin an samu aikin Hajji mai sauƙi da kwanciyar hankali a shekarar 2026.

A ƙarshe, Sakataren ya roƙi albarkar Allah ga duk masu niyyar tafiya, tare da jan hankalinsu da su shirya ba kawai ta fuskar kuɗi ba, har ma da ta fuskar ruhaniya domin gudanar da wannan ibada mai tsarki.

“Sakonmu yana da sauƙi: ku biya da wuri, ku shirya da wuri, mu yi aiki tare domin samun nasarar aikin Hajji,” in ji shi.

26/08/2025

Celebrating my 2nd year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

Farfesa Abdullahi Sale Ya Cika Shekara 1 a NAHCON Bayan Nasarar Gudanar da Hajin 2025 - Nura Ahmad Dakata Shugaba Bola T...
24/08/2025

Farfesa Abdullahi Sale Ya Cika Shekara 1 a NAHCON Bayan Nasarar Gudanar da Hajin 2025 - Nura Ahmad Dakata

Shugaba Bola Tinubu ya nada Farfesa Abdullahi Saleh Usman a watan Agustan 2024, sannan Majalisar Dattawa ta tabbatar da nadin nasa bayan watanni biyu. Ya karɓi jagorancin NAHCON a wani lokaci mai cike da ƙalubale na aiki da kuma kyakkyawan tsammanin alhazai na Najeriya.

Shekara guda bayan haka, ya samu Hadin kan alhazai, hukumomin jihohi, da abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa ta hanyar sauye-sauyen da s**a dawo da inganci da gaskiya a tafiyar da aikin Hajji.



Aikin Hajjin 2025 ya fito fili da tsari mai kyau. Karon farko kenan, dukkan alhazai ‘yan Najeriya s**a samu biza akan lokaci. Jigilar fiye da alhazai 52,000 ta kammalu cikin nasara kafin jadawalin da aka tsara, haka ma dawo da su gida ya kammalu da wuri fiye da yadda aka zata.



Alhazai sun ji daɗin karin walwala da jin daɗi ta hanyar masauki kusa da Harami a Madina, abinci safe da dare a kullum, da kuma ingantaccen sufuri tsakanin wuraren ibada. A Mina da Arafat kuma, an samar da tantuna na zamani da abinci, da kulawar lafiya mafi kyau.



Daya daga cikin muhimman abubuwa na tarihi shi ne kaddamar da tashin farko na alhazai daga yankin Kudu maso Gabas, inda mutum 315 s**a tashi daga Filin Jirgin Sama na Owerri.



Haka kuma, Farfesa Usman ya gana da gwamnoni, shugabannin gargajiya da malamai a dukkanin shiyyoyin kasar nan guda shida, abin da ya ƙarfafa jajircewar hukumar wajen kula da walwalar alhazai.



A wani mataki na nuna zumunci tsakanin addinai, Farfesa Abdullahi ya karɓi bakuncin shugaban Hukumar alhazai ta Kiristoci ta Najeriya (NCPC), Bishop Stephen Adegbite, a ofishinsa, inda s**a yi alkawarin ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin



Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya ce NAHCON zata dora kan waɗannan nasarori, tare da alkawarin samar da aikin Hajji mafi inganci a 2026 da masauki mafi kyau da abinci mai gina jiki da harkar kiwon lafiya da sufuri.



Masu lura da al’amura sun bayyana cewa shekara ta farko ta Farfesa Usman ta sake daidaita NAHCON don samar da ingantacciyar hidimar alhazai. Ana kuma sa ran ƙarin sauye-sauye da za su ƙara inganta tafiyar aikin Hajjin Najeriya a nan gaba.

Labari Cikin Hotuna: A yau 21 ga watan Augusta 2025, Gwamnan Jigawa Malam Umar Namadi ya karbi rahoto daga kwamatin aiki...
21/08/2025

Labari Cikin Hotuna: A yau 21 ga watan Augusta 2025, Gwamnan Jigawa Malam Umar Namadi ya karbi rahoto daga kwamatin aikin Hajji na shekarar 2025 da ya gabata Inda Amirul Hajju na bana, Mai Martaba Sarkin Kazaure, Alhaji Najib Hussaini Adamu ya jagoranci tawagar tare da yan kwamati a gidan Gwabnatin Jigawa.

Hotunan zaman tattaunawa tsakanin Shugabancin hukumar NAHCON da na kungiyar masu kamfanonin jirgin yawo wanda aka gudana...
21/08/2025

Hotunan zaman tattaunawa tsakanin Shugabancin hukumar NAHCON da na kungiyar masu kamfanonin jirgin yawo wanda aka gudanar yau alhamis 21ga watan Agusta a Shedikwatar Hukumar dake Abuja

14/08/2025

Sheikh Kabiru Haruna Gombe ya zama sabon Modibbon Lau

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai ziyarar jaje ga Gwamnan Katsina, Dr. Dikko Umaru Radda  bisa hadarin mo...
23/07/2025

Mataimakin Shugaban kasa, Kashim Shettima ya kai ziyarar jaje ga Gwamnan Katsina, Dr. Dikko Umaru Radda bisa hadarin mota da ya gamu da shi

Yayin ziyarar Shugaban NAHCON Farfesa Abdullahi Saleh Usman, shi ya jagoranci gudanar da addu'a ta musammam domin samun sauki cikin gaggawa ga gwamnan

Innalillahi wa inna ilaihi raji'un 😢 Allah ya karbi rayuwar Sheikh Abdullahi 'Yankaba
14/07/2025

Innalillahi wa inna ilaihi raji'un 😢 Allah ya karbi rayuwar Sheikh Abdullahi 'Yankaba

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Haji Ayarin Allah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Haji Ayarin Allah:

Share