Prince24

Prince24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Prince24, Media/News Company, Getso Bakin Kasuwa Gwarzo LG Along Karaye Road, Kano.

Musa Hasahya Kenan, Mai Mata 12, Da 'Ya'ya 102 Da Kuma Jikoki 568Dan kasar Uganda ne, saidai yanzu ya ce ya soma yin tsa...
07/02/2023

Musa Hasahya Kenan, Mai Mata 12, Da 'Ya'ya 102 Da Kuma Jikoki 568

Dan kasar Uganda ne, saidai yanzu ya ce ya soma yin tsarin tazarar haihuwa don takaita iyali. Ya kuma kara da cewa wasu daga cikin 'ya'yan nasa ma yana mance sunansu.

MUTANE DA DAMA SUN RASA RAYUKAN SU A KASAR SIRIYAInnalillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un Yadda Gilgizar Ƙasa Ta Halaka Dubba...
07/02/2023

MUTANE DA DAMA SUN RASA RAYUKAN SU A KASAR SIRIYA

Innalillahi Wa'inna Ilaihir Raji'un Yadda Gilgizar Ƙasa Ta Halaka Dubban Mutane A Ƙasar Turkiyya Da Syria......

Rahotanin da yawa da suke fitowa daga ƙasar Turkiyya da Syria sun bayyana cewa kimanin Mutane Dubu Huɗu ne s**a rasa rayukan su sanadiyyar wata girgizar ƙasar da ta afk**a gabashin ƙasar.

Ya Allah kajiƙan waɗanda s**a rasu Allah ka kare mu daga ganin aukuwar irin wannan yanayin a yankunan mu A

Fitacciyar jarumar wasan Hausa Maryam Wazeery (Lailai) a Shirin Labarina, ta haihu inda aka raɗawa ɗiyar nata da suna Fa...
07/02/2023

Fitacciyar jarumar wasan Hausa Maryam Wazeery (Lailai) a Shirin Labarina, ta haihu inda aka raɗawa ɗiyar nata da suna Fadeela.

DÁ ƊUMÍ ƊUMÍ: Bóla Tìnúbú Ya Ziyarci Mahaifiyar Tsohon Shúgaban Nájeriya Marigayì Umar Musa Ƴar'adua.Wane fata zakuyi ma...
06/02/2023

DÁ ƊUMÍ ƊUMÍ: Bóla Tìnúbú Ya Ziyarci Mahaifiyar Tsohon Shúgaban Nájeriya Marigayì Umar Musa Ƴar'adua.

Wane fata zakuyi masa

YANZU-YANZU: Alhaji Muhammad Hameem Nuhu Sanusi Ya Zama Sabon Sarkin Dutse, Jihar JigawaMasu zabar sarki guda bakwai a m...
05/02/2023

YANZU-YANZU: Alhaji Muhammad Hameem Nuhu Sanusi Ya Zama Sabon Sarkin Dutse, Jihar Jigawa

Masu zabar sarki guda bakwai a masarautar Dutse sun zaɓi, Alhaji Muhammad Hameem a matsayin sabon sarkin Dutse, ciki harda kuriu uku na masu zabar guda uku da s**a nemi sarautar.

A wata sanarwar da masarautar Dutse ta fitar yau Lahadi, ta ce an gabatar da sunan sabon sarkin da aka zaɓa ga majalisar sarakunan jihar Jigawa wanda ta amince da sunan da masu Zaɓar sarkin masarautar Dutse s**a bayar.

Sanarwar ta kara da cewar majalisar sarakunan jihar Jigawa ta aike da sunan Muhammad Hameem da sauran yan takarar biyu ga gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru Abubakar domin neman amnincewarsa kuma ya amince da wannan zaɓin.

Idan Allah ya kaimu karfe 4:00 na yammacin yau za'a miƙa wa sabon sarkin takardar k**a aiki a fadar sarki dake Garu.

Allah Ya Taya Riko!

Daga Jamilu Dabawa

Jaridar Prince24 ta Dawo Aiki Kamar Yadda ta fara Gabatar da shirye shirye ta a BayaZaku iya Aiko Mana da Sakonnin da s*...
26/04/2022

Jaridar Prince24 ta Dawo Aiki Kamar Yadda ta fara Gabatar da shirye shirye ta a Baya

Zaku iya Aiko Mana da Sakonnin da s**a shafi na Fatan Alkhairi Hadi da Rahotanni da ku ka samu A Yan' kunan Ku Kan Abida ke faruwa da Yanzu da Anjima Ko Anyi ya Wuce a Naso a Sanar Ko wanda s**a shafi Harkar Siyasa a Kowanne Nashiya a fadin Kasar Najeriya dama wajen ta

Hadi da Harkokin Siyasar Ku da s**a Hada da Kowacce Jamiyya Kowanne Bangare Kowacce nashiya

Zaku Iya Iko Mana da Sakonnin Ku

Ta..............

07043206008

WhatsApp
09032696729

Facebook

[email protected]

Muna Jiran Sakonnin Ku

Mungode

ALHAMDULILLAHI: Addinin Musulmci Ya samu Karuwa Mutane (104) sun Karbi Kalmar shahada a wani Gari mai suna Ijaw Dake cik...
15/12/2021

ALHAMDULILLAHI: Addinin Musulmci Ya samu Karuwa

Mutane (104) sun Karbi Kalmar shahada a wani Gari mai suna Ijaw Dake cikin Jihar Dalta Bayan sun Karbi Addinin Musulmci sun Gudanar da Sallah Azhar Jim Kadan Bayan shigowar su

Allah Ubagiji Yasa sun shigowa Kenan

Jaridar Prince24
15/12/2021

Kullum sai an kashe mutane a Arewacin Nijeriya -- Sarkin MusulmiSarkin Musulmin Nijeriya, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar...
10/12/2021

Kullum sai an kashe mutane a Arewacin Nijeriya -- Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmin Nijeriya, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar na 3 ya koka da cewa babu wata rana da ba za a kashe al'umma a Arewacin Nijeriya ba.

Sarkin Musulmin kuma ya shawarci ƴan Nijeriya da su haɗa kansu don kawo karshen ta’addanci a ƙasar.

A lokacin da yake tsokaci kan matsalar tsaro a Nijeriya a taron Majalisar Haɗin kan Addinai, NIREC, Sultan ya ce ba lokaci ba ne da mabiya addinai, musamman Musulmi da Kirista za su riƙa zargin juna da yi wa juna barazana ba.

Sarkin Musulmin ya nuna damuwa kan yadda kashe-kashe da sace-sacen jama’a ke ci gaba da afkuwa, amma kuma Musulmi da Kirista sun ɓige da nuna wa juna yatsa da yi wa juna barazana.

” Dole ne mu daina zargin juna kuma mu haɗa kai matsawar muna son mu yaki makiyanmu. Idan na ce zan yi magana kan rashin tsaro a arewa babu lokacin da za mu bar ɗakin taron nan. In ji Sultan.

Yakara da cewa , “yan kwanakin da s**a wuce mun karanta a jaridu yadda aka kona matafiya a bas a Sokoto. Babu ranar da za ta zo ta wuce ba a kashe mutane a Arewa ba, musamman Arewa maso Yamma.”

Bugu-da-ƙari Sultan ya buƙaci shugabanni da sauran hukumomin tsaro su haɗa kai su kuma fahimci girman matsalar tare da magance ta.

“Kar mu yaudari kanmu, abubuwa ba sa tafiya yadda yak**ata a Nijeriya. Na sha faɗa a lokuta da dama cewa abubuwa ba sa tafiya yadda ya k**ata. Kuma idan dai kasan matsalarka, magance ta ba zai yi maka wahala ba. Saboda haka ya k**ata mu san na yi kafin lokaci ya kure mana

A Rana Mai Kamar Ta Yau 9 Ga Watan Disamba A Shekarar 2014, Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Wasan Barkwanci Rabilu Musa, w...
09/12/2021

A Rana Mai Kamar Ta Yau 9 Ga Watan Disamba A Shekarar 2014, Allah Ya Yiwa Shahararren Dan Wasan Barkwanci Rabilu Musa, wanda aka fi sani da Dan Ibro Rasuwa.

An haife shi: 12 Disamba 1971, A Danlasan Da Ke Kano

Ya rasu: 9 ga Disamba, 2014, A Kano

Ya Bar Ya'ya: 7

Da mata 3

Allah ya gafarta masa.

©: B Salia

Ƙasar Saudiya ta haramtawa 'Yan Najeriya shiga ƙasar ta kai tsaye saboda sabuwar  cutar Corona ta Omicron.Gwamnatin ƙasa...
08/12/2021

Ƙasar Saudiya ta haramtawa 'Yan Najeriya shiga ƙasar ta kai tsaye saboda sabuwar cutar Corona ta Omicron.

Gwamnatin ƙasar Saudi Arabiya tabi sahun wasu kasashen duniya wajen hana jiragen sama da s**a tashi daga Najeriya shiga kasar sak**akon samun wasu mutanen dake dauke da sabon nau’in cutar korona da ake kira Omicron.

Wannan mataki na zuwa ne kwana biyu bayan Birtaniya da Canada sun haramtawa baki daga Najeriya shiga ƙasar su sak**akon samun masu dauke da cutar.

Rahotanni daga birnin Kano sun ce yanzu haka maniyata Umrah da dama sun makale a birnin sak**akon wannan mataki da Saudiyar ta dauka, yayin da jami’an kula da tashohin jiragen saman Malam Aminu Kano s**a tabbatar da samun umurnin hana jirage tashi zuwa kasar.

Wata matafiya da yanzu haka take birnin Kano akan hanyar ta na zuwa Umrah Tabbatar da cewar gwamnatin Saudiya ta soke tafiyar su daga Najeriya.

Jaridar Daily Trust ta jiyo ta bakin wani jami’in ofishin Jakadancin Saudiyar dake Kano na cewar tabbas sun samu umurnin hana jiragen sama daga Najeriya tafiya kasar.

Sai dai Jaridar ta ruwaito cewar duk da wannan umurnin, wani babban jami’in kamfanin jiragen sama ya shaida mata cewar jirage biyu sun tashi yau da safe daga Abuja zuwa Jeddah wadanda s**a hada da Qatar Air da Badar Air.

Ilimin Addinin Musulunci Ka Ke Buƙata Ba Boko Ba, Tsohon Kwamishina aiyuka Ya Faɗa Wa Ganduje....Injiniya Muazu Magaji, ...
08/12/2021

Ilimin Addinin Musulunci Ka Ke Buƙata Ba Boko Ba, Tsohon Kwamishina aiyuka Ya Faɗa Wa Ganduje....

Injiniya Muazu Magaji, tsohon kwamishinan ayyukan jihar Kano, ya shawarci gwamna Abdullahi Umar Ganduje .

Bisa shawarar Magaji, k**ata ya yi Ganduje ya bazama neman ilimin addini ba ya garzaya Jami’ar Harvard ba, don neman karin ilimi .

Dama an samu bayanai akan yadda Ganduje ya bazama jami’ar da ke Amurka don halartar taro akan ilimin ingantaccen shugabanci na mako guda.

Injiniya Muazu Magaji, tsohon Kwamishinan Ayyuka na jihar Kano, ya shawarci Gwamna Abdullahi Umar Ganduje akan komawa don karo ilimin addini maimakon tafiya jami’ar Harvard don karo ilimi.

Daily Nigerian ta ruwaito cewa Ganduje ya tafi Amurka don halartar wani taro kwas na sati daya “Bunkasa Shugabanci ” a Jami’ar Harvard da ke Boston.

Bayan samun wannan labarain ne tsohon kwamishinan ya wallafa a shafinsa na Facebook inda ya ba gwamnan shawara, Daily Trust ta ruwaito.

A cewarsa, gwamnan ya fi bukatar ilimin “Makarantar Allo” ma’ana ilimin addinin musulunci.

A cewar Magaji ilimomin bokon da Ganduje ya tara sun ishe shi Magaji ya kwatanta horarwa akan ci gaban mulkin da Ganduje ya tafi Amurka don yi a matsayin abu mara amfani, ya ce digiri na farkon da ya yi a ABU da digirin digirgir din da ya yi a Ibadan sun ishe shi.

“Abinda ka fi bukata ne ba ka mayar da hankalinka a kai,” k**ar yadda ya wallafa. A cewarsa: “Makarantar Allo ka fi bukata don sanin yadda za ka gudanar ayyuka da kuma tattala dukiyar al’umma, ya k**ata ka je don ka fahimci irin hadimai na kwarai da zaka dora don kulawa da fannoni daban-daban.

Mu gogaggun yan siyasa ne,  ba a bakin t**i muna tsinci siyasa ba -- Ganduje Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje,...
08/12/2021

Mu gogaggun yan siyasa ne, ba a bakin t**i muna tsinci siyasa ba -- Ganduje

Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa ya dauki tsawon shekaru sama da 40 yana cikin harkokin siyasa, bugu da kari ma ita ya karanta a jami'a kuma yanzu ma ita yake yi, saboda haka ya goge a cikinta, yasan yadda ake samun rarrabuwar kai a siyasa, wanda ba sabon abu bane, kuma azo a daidaita ma ba sabon abu bane, domin ba'a daukar mutum a matsayin makiyi na din-din-din, sai dai ma ace amini na har abada.

Nasara Radio (Amanar Talaka) ta rawaito cewa, gwamna Ganduje ya bayyana haka ne cikin wata tattaunawa da sashen Hausa na Rediyo Faransa, biyo bayan rikicin cikin gida da ta mamaye jam'iyyarsu ta APC a jihar Kano, tsakanin tsaginsa da kuma tsagin tsohon gwamna, Sanata Malam Ibrahim Shekarau, wanda har ta kai ga wata kotu a Abuja ta rushe zaben mazabu na tsagin Ganduje, ta kuma tabbatar da shugabancin tsagin Shekarau karkashin Ahmadu Haruna Dan Zago, hukuncin da tsagin Shekarau s**a ce yayi awon gaba da kujerar tsohon shugaban jam'iyyar, Alhaji Abdullahi Abbas.

Ganduje yace ana nan ana sasantawa, kuma tuni uwar jam'iyyar APC ta kasa ta shiga maganar, yace suna fatan hakonsu zai cimma ruwa, domin ita siyasa tana bukatar hakuri, idan an samu sabani to sai kuma azo a shirya, a cewarsa. Sai dai kuma wasu na ganin kalaman magoya baya na kara kunna wutar rikicin, k**ar a baya bayan nan anji muryar shugaban karamar hukumar Ungoggo, Injiniya Garba Ramat, yayi kausasan kalaman akan tsohon gwamna Shekarau da sauran yan tawagarsu.

Ya kuka kalli wannan batu?

Nasara Radio 98.5 FM
8/12/2021

Address

Getso Bakin Kasuwa Gwarzo LG Along Karaye Road
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prince24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Prince24:

Share