Fidelity Hausa

Fidelity Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Fidelity Hausa, Media/News Company, Kano.

An Bude Wannan Kafar Ranar 11, July 2022
An Fara Gabatar Da Shirye-shirye A Ranar 1 January 2023

Wannan Kafa Wacce Take Yin Shirye-shirye Cikin Harshen Hausa Zallah

Don Tuntubar Mu Kai Tsaye
08124052625

Hukumar Kididdiga ta Jihar Gombe ta Kaddamar da Kundin Kididdiga na Shekara ta 2023Daga Aliyu Bala Gerengi, GombeHukumar...
29/07/2025

Hukumar Kididdiga ta Jihar Gombe ta Kaddamar da Kundin Kididdiga na Shekara ta 2023

Daga Aliyu Bala Gerengi, Gombe

Hukumar Kididdiga ta Jihar Gombe (GSBS) ta kaddamar da kundin kididdiga na shekarar 2023, wanda ke bayyana cikakken bayani kan ci gaban jihar ta hanyar tattara bayanai.

Wannan kundin yana bayar da mahimman bayanai kan bangarori kamar noma, kudaden shiga, yawan jama’a, ilimi, lafiya, albarkatun dan Adam, hanyoyi, da sauran al’amuran tattalin arziki.

27/07/2025

Wasu Daga Cikin Ma'aikatan FIDELITY HAUSA

Najib Hussaini Ahmad
Mudassir Saleh
Ahmad Hussain Ahmad
Aliyu Gerengi Bala
Ibrahim Musa Gozawa
Zuhraty Muhammad Abdallah
Umar Teemary
Da Sauran su.

27/07/2025
FIDELITY HAUSA Gaskiya Da Gaskiya
27/07/2025

FIDELITY HAUSA

Gaskiya Da Gaskiya

Kwamishinar Harkokin Mata da Ci gaban Jama'a ta Jihar Gombe, Asma’u Mohammed Iganus, ta mika kwafin dokar hana cin zaraf...
25/07/2025

Kwamishinar Harkokin Mata da Ci gaban Jama'a ta Jihar Gombe, Asma’u Mohammed Iganus, ta mika kwafin dokar hana cin zarafin mata da yara (GBV) ga Mai Martaba Sarkin Gombe, Alhaji Dr. Abubakar Shehu Abubakar III.

An gabatar da dokar ne yayin wata ziyarar wayar da kai da fadakarwa a fadarsa, domin nemab goyon bayan al’umma wajen yaki da cin zarafi da munanan dabi’u a cikin al’umma.

Kwamishinar ta jaddada muhimmancin rawar da shugabannin gargajiya da na addini ke takawa wajen yada ilimi, bin doka, da kare ‘yancin mata da yara.

Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya Ya Kafa Kwamitin Sanya Ido Don Rabon Taki Yadda ya Kamata Daga Aliyu Bala Gerengi a jih...
22/07/2025

Gwamnan jihar Gombe Inuwa Yahaya Ya Kafa Kwamitin Sanya Ido Don Rabon Taki Yadda ya Kamata

Daga Aliyu Bala Gerengi a jihar Gombe

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, ya amince da kafa kwamitin jiha kan rabon taki na daminar bana.

An ɗorawa kwamitin alhakin tabbatar da ganin an rattaba takin cikin gaskiya da adalci ga manoma a faɗin jihar.

A cewar wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar Farfesa Ibrahim Abubakar Njoɗi ya fitar, Kwamitin zai kasance ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Noma, Kiwo da Ƙungiyoyin Gama Kai, yayin da sauran mambobin kwamitin s**a haɗa da manyan masu ruwa da tsaki da s**a fito daga sassa daban-daban na gwamnati, ƙungiyoyin fararen fula, da hukumomin tsaro.

Jihar Gombe ta Zama ta 7 a Rahoton Jihohi Mafiya Ƙoƙari na BanaDaga Aliyu Bala Gerengi a GombeJihar Gombe ta sake samun ...
18/07/2025

Jihar Gombe ta Zama ta 7 a Rahoton Jihohi Mafiya Ƙoƙari na Bana

Daga Aliyu Bala Gerengi a Gombe

Jihar Gombe ta sake samun karramawar ƙasa a matsayin abar koyi a fagen shugabanci na gari, da sauye-sauye da kuma muhimman harkokin ci gaba, inda ta samu matsayi na 7 a ƙasa baki ɗaya a bana, a rahoton ƙoƙarin jihohi na ‘Phillips Consulting State Performance Index’ inda ta yiwa jihohi 30 fintinkau a faɗin ƙasar nan.

Cikakken bayani a Rahoton ƙoƙarin Jihohin na bana, sakamako ne na binciken da babban kamfanin ƙwararrun masana, Phillips Consulting ya tattara, ɗaya daga cikin nagartattun cibiyoyin bincike da ƙididdiga masu ƙima a Najeriya.

Binciken ya sanya jihohi 36 da Abuja a kan wassu ma'aunai masu mahimmanci da s**a haɗa da mulki, tattalin arziki, ci gaban zamantakewa da samar da ababen more rayuwa.

A yawancin waɗannan batutuwan da aka auna, Jihar Gombe ta yi rawar gani tare da samun gamsuwa daga al’ummarta.

Jihar ta zo ta ɗaya a fannin ingantattun hanyoyi da kulawar jinya a asibitocin gwamnati, hakan ya nuna ƙarara irin jajircewar gwamnati wajen samar da ababen more rayuwa da inganta lafiya.

Har ila yau, jihar ta zo ta 1 a fagen Sauƙaka harkokin Kasuwanci, lamarin dake nuna kyakkyawan yanayi mai haba-haba da masu zuba jari da hukumomi masu nagarta.

Har ila yau, Gombe ta zama ta 2 a fannin Tsaron Rayuka da Dukiyoyi da Tsaftar Muhalli, wanda hakan ke nuni da irin ƙoƙarin da gwamnati ke yi wajen samar da zaman lafiya, tsaro da ci gaban al’umma.

Sauran sassan da Jihar Gomben ta yi fice sun haɗa da: zuwa matsayi na 3 a fagen Taimakekeniyar Lafiyar Jama’a – biyo bayan nasarar aiwatar da shirin inshorar lafiya na Go-Health, da kuma zuwa matsayi na 5 a fannin Sufuri da Ilimi, lamarin dake tabbatar da ƙaruwar tallafi ga talakawa da marassa galihu.

Rahoton ya alaƙanta wannar nasarar da himma da jajircewar Gwamna Inuwa Yahaya, da salonsa na gudanar da mulki daya karkata ga muradun jama’a, da kuma ci gaba da kawo sauye-sauye.

Rahoton ya yi hasashen cewa an ɗora Gombe kan

Shugaba Tinubu zai kashe Bilyan 120bn a jihar Gombe domin samar da cibiyar kiwon shanu don samar da abinci a arewacin Na...
15/06/2025

Shugaba Tinubu zai kashe Bilyan 120bn a jihar Gombe domin samar da cibiyar kiwon shanu don samar da abinci a arewacin Najeriya.

Shugaba Tinubu ya amince da fitar da Naira Biliyan 120 don tallafa wa Jihar Gombe don samar da yankin masana’antar noma da kiwo mai fadin hekta 184 kamar yadda Gwamna Inuwa Yahaya ya tabbatar da karbar chakin Naira biliyan 60 (kashin farko)

Gwamnoni Arewacin Najeriya Sun Tattauna Kan Al'amuran yankin a Taron Ƙungiyar GwamnoniDaga Aliyu Gerengi, GombeGwamnan J...
21/11/2024

Gwamnoni Arewacin Najeriya Sun Tattauna Kan Al'amuran yankin a Taron Ƙungiyar Gwamnoni

Daga Aliyu Gerengi, Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya CON, ya bi sahun takwarorinsa a ƙarƙashin Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) a wani taro da s**a gudanar a sakatariyar ƙungiyar dake Abuja.

Sanarwar Ismaila Uba Misilli,
Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe ta bayyana cewa, taron wanda ya samu halartar gwamnoni daga sassan ƙasar nan, an tattauna muhimman batutuwan da s**a shafi ƙasa baki ɗaya.

Hakazalika taron ya samu halartar wassu ‘yan majalisan wakilai ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar Rt. Hon. Benjamin Kalu.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fidelity Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fidelity Hausa:

Share