VR Hausa

VR Hausa Voice Radio Hausa gidan Radio ne wanda zai yinga kawo muku shirye-shirye da labaran duniya na yau da kullum

NNPP Deserves a Leader, Not Dungurawa’s Rash Decisions
14/11/2024

NNPP Deserves a Leader, Not Dungurawa’s Rash Decisions

I strongly advise Hashimu Dungurawa to retract his defamatory allegations against Senator Kawu Sumaila and other party members.

GANGANCI KO KUMA RASHIN ƘWAREWA??Daga. Mubarak Shehu DayyabAcikin wani rubutu da na karanta na (U.S. Africa Command Stri...
06/12/2023

GANGANCI KO KUMA RASHIN ƘWAREWA??

Daga. Mubarak Shehu Dayyab

Acikin wani rubutu da na karanta na (U.S. Africa Command Strike Process) sunyi bayani akan hanyoyin da ake bi wajen ƙaddamar da harin jirgin sama. Kamar haka...

1: (Defensive Strike Process) wanda shine na ƙara kai daga hari, sai kuma
2: (Deliberate targeting process) wanda shine na kai wa, wato shi wannan (Deliberate Targeting process) saboda matuƙar hatsarin sa yana bukatar kwararru wajen aiwatarwa.
A lokacin kai wannan harin ana buƙatar military lawyers wajen target identification da kuma nomination process, inda military lawyers zasu conducting review akan harin da kuma inda za'a kai harin, shin gurin akwai civilians ko babu, kafin a kai wannan harin sai an tabbatar da cewa babu wani civilian a gurin, ana samun ƙwararru masu kaifin basira domin bujuro da mataki daban daban da za'a bi kamarsu, samun signal, human imagery, da open source intelligence da sauransu. A duk lokacin da aka fahimci cewar akwai civilians a gurin to ana adjusting lokacin kai harin, kokuma a canja makamin da za'a yi amfani da shi, ko kuma ayi haƙuri da kai wannan harin, har sai lokacin da aka tabbatar babu civilians a gurin. Duk da cewa wani lokaci ana samun matsaloli wajen samun bayanai da kuma kurarurai da baza a rasa ba, amma to ya abun yake ne a Nijeriya????

Shin ganganci ne ko kuma rashin sanin makamar aiki, ganin irin abubuwan da s**a faru a baya bayannan da kuma kwana kwanannan kamar haka....

2014: BORNO STATE

A cikin watan March 2014, jirgin sojoji, a ƙoƙarin sa na zakulo, yan ta'addan boko haram, a dajin sambisa, sun harba ma bayin Allah da basu ji ba basu gani ba bom a ƙauyen, Daglun a jahar Borno State. Inda hakan ya janyo rasa rayuka masu yawa. A wannan lokacin rahoton da aka bayar shine wai kuskure ne akayi, saboda anyi tunanin wani san sani ne wanda mayaƙan boko haram suke ɓuya, a wannan lokacin rahoton da CNN, ta bayar Ali Ndume, sanatan dake wakiltan wannan shiyar yace wai kuskure ne.

2017: BORNO STATE

Acikin January 2017, an sake ayyanawa jirgin saman sojoji ya ƙara sakin bomb a sansanin ƴan gudun hijira na Rann, a ƙauyen Kala-Balge, inda hakan yayi sanadiyar mutuwar mutane sama da ɗari, da kuma jikkata mutane masu yawa, a wannan lokacin ma an ƙara cewa wai kuskure ne.

2019: ZAMFARA STATE

Har ila yau acikin watan April 2019, jirgin sojoji a ƙoƙarin su na ɗakile harin ta'addanci na masu garkuwa da mutane, sun kai hari a ƙauyen Tangaram, a jahar Zamfara inda haka yayi sanadiyar rasa rayuka masu yawa, da kuma jikkata wasu, a wannan lokacin ma an ce kuskure ne.

2021: BORNO STATE

Shekara hudu bayan harba bomb da akayi a sansanin a gudun hijira wanda sojoji s**a je bisa kuskure ne, sun ƙara tafka wani kuskuren wajen harbawa a kauyen, Kwatar Daban Masara kusa da Lake Chad, inda yayi sanadiyar mutuwar a ƙalla fiye da mutane 20 masu kamun kifi sun mutu inda da yawa s**a jikkata.

2022: YOBE STATE

Har ila yau acikin watan September 2021, a ƙoƙarin sojojin Nigeriya na yaƙar yan ta'adda sun ƙara harba wani bomb a ƙauyen Buhari dake Yobe, inda yayi sanadiyar mutuwar mutane sama da Goma da jikkata mutane sama da ashirin.
Inda a sanarwar su sun tabbatar sunga wurgawar yan ta'addan boko haram a yankin Kudancin Kanama, kasancewar yankin yana fama da matsalar ta'addanci.

2022: KATSINA STATE

Acikin watan July 2022, jirgin yaƙi na Sojojin Najeriya ya ƙara jefa bomb a ƙauyen Kunkuna ƙaramar hukumar Safana a jahar Katsina, inda yayi sanadiyar mutuwar mutane masu yawa da kuma jikkata wasu. Inda rahoto ya bayar hakan yafaru a bisa kuskure ne wai, wajen ƙoƙarin su na kaima ƴan ta'adda hari.

2023: KADUNA STATE

Ranar 4 ga watan December, sojojin Nijeriya sun ƙara harba bom a wani ƙauye me suna tudun ɓiri inda jama'a suke yaran maulidi na shekara, inda yayi sanadiyar mutuwar mutane sama da ɗari da kuma jikkata mutane masu ɗimbin yawa, acikin rahoton da sojojin s**a bayar sunce hakan ya faru bisa kuskure ne.

Note:
Shawara itace yakamata a samu ƙwararru wanda s**a san makamar aiki, ba yaƙi da jiragen sama a ɓangaren sojojin saman Najeriya wanda zasu bada horo da kuma bayanai masu inganci wajen ganin an magance wannan matsalar, da kuma ƙara lura da kulawa da kayan aiki, wato jiragen da ake fita dasu ƴaki wajen ganin suna da isasshen lafiya, domin kaucewa afkuwar irin wannan matsalar nan gaba.
Allah ya jiƙan ƴan uwan mu wanda s**a riga mu gidan gaskiya. Ameen.

Abdallah wani matashi ne Dan shekara 17 a rayuwa yana rubuta jarabawar kammala sakandare (SSCE) a lokacin da wani abin t...
10/08/2023

Abdallah wani matashi ne Dan shekara 17 a rayuwa yana rubuta jarabawar kammala sakandare (SSCE) a lokacin da wani abin takaici ya faru wanda yayi sanadiyyar mutuwarsa
An tuhumi matashin da laifin satar waya (iPhone 7) mallakin makwabcin su Shuaibu Wambai Zumo, a staff of the Adamawa State Scholarship Board.

Wadan su mutane da aka bayyana sunan su da (operation farauta) s**a dauke Yaron daga gidansu s**a shaidawa iyalansa cewa suna son yi masa tambayoyi ne kawai.

Daga baya andawo da Abdullah gida yana kuka bayan an daure shi da mari anyi masa duka

Abdallah ya ansa laifin da ake tuhumarsa dashi inda ya shaida wa baban sa ya ansa laifin ne saboda ya tsira da ransa duba da irin azabtarwar da suke masa

Gungun mutanen da ake kira da (operation farauta) sun shigo gidan s**a nemi wayar amma basu same ta ba

Ana cikin bincike Abdallah ya fara amai jin ya fadi

Makwabcin yace babu wani abu da ya faru da Abdallah kawai yana kame kame ne Amma iyayen s**a garzaya da yaron assibitin koyarwa na jami’ar Modibbo Adama yayi kwana hudu a sume kuma ya rasu a safiyar yau (9 ga watan august 2023)

Daga baya aka gano wayar wani ne ya dauka ba Abdallah ba

Masu laifi na kokarin a rufe shari’a
Mukuma Muna neman ayiwa Abdallah adalci

Alhamdulillah.Bayan samun taimakon ku na yaɗa sanarwar ɓacewar waɗannan yara, Allah Ya nufe mu da samun ƴan uwan su, tar...
06/08/2023

Alhamdulillah.
Bayan samun taimakon ku na yaɗa sanarwar ɓacewar waɗannan yara, Allah Ya nufe mu da samun ƴan uwan su, tare da miƙa Yaren gare su.
Mun samu damar damƙa yaran wa ƴan uwan su ne a chaji ofis ɗin ƴan sanda na Unguwar Rogo a gaban DPO da kuma Hajiya Kaltume Auwal, wato Amirar FOMWAN ta jihar Plateau.
Allah saka mu ku da alkairi a bisa taya mu yaɗa cikiyar da kuka yi.
Na gode.
Daga Harun Umar

06/08/2023

Barkan mu da warhaka

Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce wasu 'yan ba-ni-na-iya ne s**a bayar da sunan Maryam S...
06/08/2023

Shugaban Jam'iyyar APC na ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya ce wasu 'yan ba-ni-na-iya ne s**a bayar da sunan Maryam Shetty don naɗa ta minista daga Kano, ba tare da saninsa ba.

Sai dai, ya ce shugaban ƙasa yana da damar naɗa mutanen da yake son tafiya da su a muƙaman ministoci daga jihohin ƙasar bisa la'akari da tsare-tsarensa da ƙwarewar mutanen da kuma sauran buƙatu.

A wata hira da ya yi da wasu kafofin yaɗa labarai ciki har da Freedom Radio ranar Asabar, tsohon gwamnan, wanda shi ne jagoran jam'iyyar a Kano, ya ce ba shi da cikakkiyar masaniya a kan Maryam Shetty, hasali ma ba su santa ba a matsayinsu na jagororin APC daga Kano.

Don haka ''ka ga ba mu da wani ma'auni da za mu ce za ta iya, ko ba za ta iya wannan aiki ba idan aka nemi shawararmu''.

Ganduje ya ce martanin da mutane s**a yi ta bayyanawa a shafukan sada zumunta, shi ma ya taka rawa wajen ɗaukar matakin sauya sunan Dakta Maryam Shetty, bayan wasu sun riƙa nuna cewa ba za ta iya riƙe muƙamin minista a Najeriya ba kasancewar ba ta taɓa riƙe wani muƙamin gwamnati ba.

Shugaban na APC ya ce da haka ne labari ya je har wajen shugaban ƙasa, wanda ya kira Ganduje don jin shawararsa.

''Ya ce min ga fa abin da ke faruwa, shin kai ka bayar da sunanta? Sai na ce masa a'a sam sam, ba ni ba ne, ban ma sani ba, daga nan ya ce to ya ka gani? akwai buƙatar a canja?, sai na ce masa ƙwarai da gaske kuwa'', in ji tsohon gwamnan na Kano.

Ganduje ya ce muƙamin minista, matsayi ne da ke buƙatar dattaku da sani (ƙwarewa), sannan yana buƙatar taka muhimmiyar rawa wajen kafa gwamnati a siyasance.

''To idan ka auna waɗannan abubuwa kuwa, ai mu ya kamata a tambaya, in dai ana so a bayar da wakilci daga jihar Kano'', in ji shi.

Ya ce ko da wani can ya bayar da wata shawara, to ya kamata a tuntuɓe su , idan ya dace sai su ba da goyon baya.

Cire sunan Maryam Shetty daga jerin ministocin Shugaba Tinubu, kamar bayyana sunanta a cikin waɗanda za a naɗa tun farko, ya yi matuƙar janyo muhawara musamman a tsakanin matasa.

Mahmoud Adam

CIKIYA! CIKIYA! CIKIYA!Jama'a, Assalamu Alaikum.Wannan yara da kuke gani an tsince su ne jiya da daddare a guraren hanya...
05/08/2023

CIKIYA! CIKIYA! CIKIYA!

Jama'a, Assalamu Alaikum.

Wannan yara da kuke gani an tsince su ne jiya da daddare a guraren hanyar shiga Unguwar Rimi, ta bayan gidan man A.A. Rano dake nan cikin garin Jos.

Babbar ta ce sunan ta Nana, ƙaramar kuma Islam, sannan shi kuma yaron da ke hannun su sunan shi Nasiru.

Nana ta ce sun taho da maman su ne daga jihar Jigawa, sannan maman tace wai za su je suna a ZUNTU.

Mutanen yankin sun ce tun misalin ƙarfe 9 na daren jiya Juma'a, 4 ga watan Agustan 2023 a ka ga yaran a zaune. To amma bawan Allahn da ya haɗa mu da su, wanda kuma gidan shi na kusa da gurin da aka ajiye yaran ya ce mana mai gadin gidan man A.A. Rano ya kira shi ne da misalin ƙarfe 11 na dare don sanar da shi halin da ake ciki.

Nana dai ta ce maman su ce ta ajiye su a gurin wai su jira ta, za ta je ta siyo mu su biredi tun da yamma.

A saboda haka mu ke rokon don girman Allah, al'umma su yita yaɗa wannan rubutu da hoto ko Allah zai sa ƴan uwan su zasu gani.

Ku tuna, shi dai “YARO NA KOWA NE".

ALLAH YA BAYYANA MANA ƳAN UWAN WANNAN YARA. AMIN THUMMA AMIN.

Za ku iya tuntubar lambobin waya kamar haka domin neman ƙarin bayani akan inda yaran su ke:

Haruna Umar (07062579831)

Ibrahim Idris Badamasi (08031866089)

Baban Jos (09163994346)

Haruna Umar, Ibrahim Idris Badamasi, Unity FM/TV, Jos.

04/08/2023
Tashin Hankali: Kasar Nijar ta katse hulɗa da NajeriyaGwamnatin mulkin sojin Nijar ta yanke hulɗa da Najeriya da Togo da...
04/08/2023

Tashin Hankali: Kasar Nijar ta katse hulɗa da Najeriya

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta yanke hulɗa da Najeriya da Togo da Amurka da kuma wadda ta raine ta, Faransa bayan tawagar da Ecowas ta tura don tattaunawa da sojojin da s**a hamɓarar da shugaba Bazoum ta gaza samun matsaya da sojojin.

A wani jawabi da ya yi ta kafar yaɗa labaran ƙasar ta Nijar, jagoran juyin mulkin, Kanar Amadou Abdramane ne ya sanar da matakin da ma wasu matakan da s**a ɗauka.

Ya ce “Mun kawo ƙarshen duk wata hulɗar jakadanci da Najeriya da Faransa da Togo da kuma Amurka. Duk wata matsaya da aka cimma a baya ta rushe.”

Tawagar da Ecowas ta tura don tattaunawa da sojojin Nijar ɗin a ƙarƙashin jagorancin Janar Abdulsalami Abubakar ta gana da wasu daga cikin sojojin a ranar Alhamis amma ba a cimma wata matsaya ba, rahoton BBC

Manyan hafsoshin sojin ƙasashen Ecowas sun kammala wani taro a birnin Abuja, inda s**a tattauna yiyuwar ɗaukar matakin soji a kan Nijar idan sasanci ya gagara.

Daga Katsina Daily News

Ko ba komai duk wanda ya san Maryam Shetty ya san mutuniyar kirki ce. Ko mu da muke jam'iyyar adawa tana mutuntamu cikin...
04/08/2023

Ko ba komai duk wanda ya san Maryam Shetty ya san mutuniyar kirki ce. Ko mu da muke jam'iyyar adawa tana mutuntamu cikin nishadi da dariya. Ni ko sunana ba ta fada sai dai ta ce "kanina". Amma yan bakin ciki kuka dinga surutu karshe sai da s**a samu damar canjata da matar da a shekara hudunta tana kwamishiniya a karkashinta ba abin da aka yi sai rufe makarantu da gine gefunansu. A lokacin ilimi ya yi lalacewar da bai taba yi ba a tarihin jihar Kano. Yanzu sai ku ji dadi tun da ku matasa ku ne makiyan kanku.
Daga Aliyu Dahiru Aliyu

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin Bulala Ashirin saboda satar Kaza a KanoƳan sanda ne s**a gurfanar da matashin mai...
19/04/2023

Kotu ta yanke wa wani matashi hukuncin Bulala Ashirin saboda satar Kaza a Kano

Ƴan sanda ne s**a gurfanar da matashin mai suna Nazifi Hassan a Kotun Shari'ar Muslunci da ke unguwar Ɗanbare ƙarƙashin mai shari'a Munzali Idris Gwadabe.

An karanta masa zargin satar Kaza a unguwar Gwazaye, wanda ya amsa nan take, har ma ya ce Kwaɗayi ne ya kamashi domin tun da aka fara azumi bai ci nama ba.

Baya ga Bulala Ashirin, alƙali ya yi masa nasiha sannan an mayar wa mai Kaza abarsa.

Source, Freedom Radio Nigeria

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when VR Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to VR Hausa:

Share