MGR BROADCAST

MGR BROADCAST Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from MGR BROADCAST, Media/News Company, Kano.

"MGR broadcast Kafar yada labarai ce mai zaman kanta da ke yada zunzurutun tsagwaron labarai na fadakarwa,wa'azantarwa,siyasa,nishadi,da tattauna wa wasu muhimman batutuwa a kafafen intanet, a ko yaushe!" Cikin yaren hausa📡 ko video

Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya yabawa ‘yan jaridun Najeriya da ke aikin Hajj...
31/05/2026

Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya yabawa ‘yan jaridun Najeriya da ke aikin Hajji a Saudiyya bisa yadda s**a gudanar da rahotanni cikin kwarewa, gaskiya da jajircewa.

Ya bayyana cewa rahotannin da aka rika aikawa daga wuraren ibadar Hajji sun taimaka wajen isar da sahihan bayanai ga al’umma, tare da alkawarin kara inganta yanayin aikin ‘yan jarida a hajjin shekaru masu zuwa.

👇 Yaya kake ganin rawar da kafafen yada labarai ke takawa wajen nasarar gudanar da Hajji?

Ma’aikatar Lafiya ta Kano ta bayyana cewa kafafen yaɗa labarai na taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma kan ha...
31/05/2026

Ma’aikatar Lafiya ta Kano ta bayyana cewa kafafen yaɗa labarai na taka muhimmiyar rawa wajen wayar da kan al’umma kan harkokin lafiya da inganta lafiyar mata da yara a faɗin jihar.

👇 Mene ne ra’ayinku kan rawar da kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen wayar da kan jama’a kan harkokin lafiya?

31/05/2026

🎙️ BITAR LABARAN MAKO

A cikin makon da ya gabata, an samu manyan labarai da s**a girgiza Najeriya da duniya baki ɗaya. Daga siyasa, tsaro, wasanni, zuwa al'amuran rayuwa, mun tattaro muku muhimman abubuwan da s**a fi ɗaukar hankali.

Ku kasance tare da MGR Broadcast domin jin cikakken bayani da nazari kan manyan abubuwan da s**a faru cikin wannan mako.

👇 Wanne labari ne ya fi ɗaukar hankalinku a wannan makon? Ku bayyana mana a sashen sharhi.

MGR BroadcastA yau, 31 ga Mayu, 2026, ya cika shekara guda cif da rasuwar wasu daga cikin 'yan'uwanmu da s**a riga mu gi...
31/05/2026

MGR Broadcast
A yau, 31 ga Mayu, 2026, ya cika shekara guda cif da rasuwar wasu daga cikin 'yan'uwanmu da s**a riga mu gidan gaskiya sakamakon hatsarin mota da s**a yi a hanyarsu ta dawowa daga Jihar Ogun.

A wannan rana ta tunawa, muna sake miƙa addu'o'inmu ga Allah Maɗaukakin Sarki da Ya jiƙansu da rahama, Ya gafarta musu kura-kuransu, Ya yalwata musu ni'imomin Aljanna, Ya haskaka kaburburansu, kuma Ya sanya su cikin Aljannatul Firdausi.

Muna kuma roƙon Allah Ya ba iyalansu, abokansu da daukacin waɗanda s**a bari baya haƙurin jure wannan babban rashi.

Allah Ya jikansu, Ya gafarta musu, Ya sa ƙarshenmu ya zama mai kyau. Ameen Ya Rabbal Alameen. 🤲🕊️

🎙️ Rahoto: __________
© MGR Broadcast

Ƙungiyar Paris Saint-Germain ta zama zakarar Turai a karo na biyu a jere bayan ta doke Arsenal a wasan ƙarshe na UEFA Ch...
30/05/2026

Ƙungiyar Paris Saint-Germain ta zama zakarar Turai a karo na biyu a jere bayan ta doke Arsenal a wasan ƙarshe na UEFA Champions League na 2026. Rahotanni sun nuna cewa wasan ya tashi 1-1 bayan ƙarin lokaci, kafin PSG ta yi nasara a bugun fenareti.

Wannan nasara ta sa PSG ta kare kambunta bayan ta lashe kofin a karon farko a bara, lamarin da ya sanya ta cikin ƙungiyoyin da s**a yi nasarar lashe Champions League sau biyu a jere a zamanin gasar ta zamani.

Shin PSG ce mafi ƙarfi a Turai a yanzu?

Ko Arsenal ta cancanci cin kofin?

Ra'ayinku fa? 👇

🏆⚽🔥

30/05/2026

KAITSAYE DAGA ARTV KANO WACCE AKA FI SANI SA CTV A DA DUK ACIKIN RUGUN TSIMIN SALLAH

30/05/2026

Sharshi wasan Arsenal KO PSG

Iran ta yi watsi da sabbin ikirarin Donald Trump kan yarjejeniyar sulhu, inda ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawa da Am...
30/05/2026

Iran ta yi watsi da sabbin ikirarin Donald Trump kan yarjejeniyar sulhu, inda ta ce ba za ta ci gaba da tattaunawa da Amurka ba har sai an saki dala biliyan 12 na kadarorinta da aka daskarar.

Shin kana ganin Amurka za ta amince da wannan sharadi?

👇 Faɗi ra'ayinka a comment.

30/05/2026

🇳🇬 Shugaban ƙasa ya bayyana cewa sauye-sauyen tattalin arzikin gwamnatinsa sun taimaka wajen ƙara kuɗaɗen shiga na jihohi.

⚠️ Sai dai wasu 'yan Najeriya na ganin har yanzu rayuwa na da tsada.

❓ Kai kana ganin tattalin arzikin ƙasar ya inganta kuwa?

👇 Faɗi ra'ayinka a comment 👉 Follow MGR Broadcast domin sabbin labarai

29/05/2026

🚨 Mutane uku sun faɗa rijiyoyi a Kano cikin sa'o'i kaɗan 😳🕳️

🚒 Jami'an kashe gobara sun ceto wani mutum, wata mata da jaririnta a Kumbotso da Warawa

⚠️ Dukkaninsu an fito da su cikin rashin sani

❓ Me ya kamata a yi domin hana irin waɗannan haɗurra?

👇 Comment yanzu 👉 Follow MGR Broadcast domin sabbin labarai

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when MGR BROADCAST posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share