02/09/2026
ATIKU YA YI ALƘAWARIN YAFE WA ƊALIBAI BASHIN NELFUND
Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar (ADC), Atiku Abubakar, ya yi alƙawarin sake duba tsarin Asusun Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND), tare da yafe bashin karatu ga ɗaliban da s**a cancanta idan ya lashe zaɓen 2027.
Mai magana da yawunsa, Phrank Shaibu, ya ce Atiku zai mayar da hankali wajen rage tsadar ilimi, domin kada matasan Najeriya su fara rayuwar aiki da nauyin bashin karatu.
Shaibu ya kuma soki gwamnatin Shugaba Bola Tinubu kan amfani da NELFUND a matsayin hujjar cewa ilimi ya zama mai sauƙin samu, yana mai cewa lamunin karatu ba tallafin karatu ba ne, kuma bai kamata ɗalibai su ci bashi domin biyan tsadar ilimi ba.
📲 Ku ci gaba da bin MGR BROADCAST don ƙarin labarai masu zafi!