31/05/2026
Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Ambasada Isma’il Abba Yusuf, ya yabawa ‘yan jaridun Najeriya da ke aikin Hajji a Saudiyya bisa yadda s**a gudanar da rahotanni cikin kwarewa, gaskiya da jajircewa.
Ya bayyana cewa rahotannin da aka rika aikawa daga wuraren ibadar Hajji sun taimaka wajen isar da sahihan bayanai ga al’umma, tare da alkawarin kara inganta yanayin aikin ‘yan jarida a hajjin shekaru masu zuwa.
👇 Yaya kake ganin rawar da kafafen yada labarai ke takawa wajen nasarar gudanar da Hajji?