The Historica Nigeria Hausa

The Historica Nigeria Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from The Historica Nigeria Hausa, Media/News Company, Kano.

Shugaba Tinubu ya nada sabon shugaban bankin aikin gonaShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Muhammad Babangida, dan t...
18/07/2025

Shugaba Tinubu ya nada sabon shugaban bankin aikin gona

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya nada Muhammad Babangida, dan tsohon shugaban mulkin soja, Janar Ibrahim Babangida, a matsayin shugaban Bankin Cigaban Aikin Gona da aka sauyawa fasali.

Sanarwar nadin ta fito ne a ranar Juma’a, tare da nadin wasu mutum bakwai da za su jagoranci wasu manyan hukumomin gwamnatin tarayya daban-daban.

Muhammad Babangida, wanda ke da shekaru 53, ya samu digiri a fannin Gudanar da Kasuwanci da kuma Huldar Jama’a daga Jami’ar Montreux, Switzerland. Haka kuma, ya kammala wani shirin horo a kan shugabanci da tafiyar da kamfanoni a makarantar koyar da harkokin kasuwanci ta Harvard Business School a shekarar 2002.

HOTUNA: Taron musamman da aka gudanar da addu’o’i ga tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari, a zauren taron maj...
18/07/2025

HOTUNA: Taron musamman da aka gudanar da addu’o’i ga tsohon shugaban ƙasa, marigayi Muhammadu Buhari, a zauren taron majalisar zartarwa da ke fadar shugaban ƙasa, Abuja.

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya jagoranci taron, wanda ya samu halartar iyalan marigayin, ministoci, da manyan ‘yan siyasa daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

A yayin taron ne dai aka sauya sunan Jami'ar Maiduguri A jihar Borno, zuwa Jami'ar Muhammadu Buhari.

Shugaba zai ziyarci Kano a yau din yiwa iyalan attajirin dan kasuwa, marigayi Alhaji Aminu Dantata ta'aziyya.
18/07/2025

Shugaba zai ziyarci Kano a yau din yiwa iyalan attajirin dan kasuwa, marigayi Alhaji Aminu Dantata ta'aziyya.

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Jami'ar Muhammadu Buhari Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da ...
17/07/2025

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Maiduguri Zuwa Jami'ar Muhammadu Buhari

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya sanar da sauya sunan Jami’ar Maiduguri da ke jihar Borno zuwa Jami’ar Muhammadu Buhari.

Shugaba Tinubu ya bayyana haka ne a wani taro na musamman na Majalisar Zartaswa ta Ƙasa da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja a ranar Alhamis.

Taron wanda ya kasance wani ɓangare na bikin tunawa da irin rawar da tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya taka wajen shugabancin ƙasar, ya gudana tare da halartar manyan jami’an gwamnati.

Rahotanni na nuni da cewa wannan sauyin sunan na cikin jerin matakan da gwamnatin Tinubu ta ɗauka domin girmama tsohon shugaban, wanda ya shugabanci Najeriya daga shekarar 2015 zuwa 2023.

Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDPTsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP.H...
16/07/2025

Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya fice daga jam’iyyar PDP.

Hakan na kunshe ne cikin wata Wasika da ya sanyawa hannu da kansa kuma aikawa Shugaban jam’iyyar PDP na mazabarsa ta Jada dake jihar Adamawa.

Ya ce ya fice daga jam’iyyar ne saboda mawuyacin halin da take cikin na rashin Tabbas.

Ya godewa Shugabannin jam’iyyar bisa gudunmawar da s**a ba shi tun lokacin da ya shige tun a shekarun baya.

Shehu Sani ya bukaci shugabannin Najeriya su koyi darasi daga martanin jama’a bayan rasuwar BuhariTsohon Sanata Shehu Sa...
16/07/2025

Shehu Sani ya bukaci shugabannin Najeriya su koyi darasi daga martanin jama’a bayan rasuwar Buhari

Tsohon Sanata Shehu Sani ya shawarci shugabannin Najeriya na yanzu da masu tasowa su dauki darasi daga irin martanin da 'yan Najeriya s**a nuna cikin awanni 48 da s**a gabata, bayan rasuwar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari.

Wannan dai na kunshe cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, inda Sanata Sani ya bayyana cewa matasan wannan lokacin masu zafin rai ne, wadanda ke bayyanawa ba tare da fargaba ba yadda suke jin haushin duk wani shugaba da s**a dauka ya zalunce su.

Ya ce “Shugabannin yanzu da na gaba su dauki darasi daga irin martanin da ‘yan Najeriya s**a nuna cikin awanni 48 da s**a gabata. Sabon zamani ne da ya samar da sabuwar al’umma mai dauke da fushi, rashin hakuri da kuma rashin yafiya.”

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura jihar Katsina.Rahotanni na cewa an binne ...
15/07/2025

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a gidansa da ke Daura jihar Katsina.

Rahotanni na cewa an binne Buhari da misalin karfe 5:50 na yamma.

Buhari ya rasu a ranar Lahadi a birnin Landan bayan ya sha fama da rashin lafiya.

HOTUNA: Shugaba Tinubu da Shugabannin Afirka Sun Karrama Buhari a Jana’izarsaShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, tare da ma...
15/07/2025

HOTUNA: Shugaba Tinubu da Shugabannin Afirka Sun Karrama Buhari a Jana’izarsa

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, tare da manyan baki daga kasashen Guinea-Bissau da Nijar, da kuma wasu ministoci da gwamnonin jihohi masu ci da wadanda s**a gabata, sun halarci jana’izar marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Taron ya ja hankalin shugabannin yankuna da na kasa da s**a hallara domin girmamawa ta karshe ga dattijon dan kasa.

An dage jana'izar marigayi Muhammad Buhari sai zuwa gobe Talata 15 ga watan Yuli, 2025, da misalin karfe 2 na rana a gar...
14/07/2025

An dage jana'izar marigayi Muhammad Buhari sai zuwa gobe Talata 15 ga watan Yuli, 2025, da misalin karfe 2 na rana a garin Daura, kamar yadda gwamnan jihar Katsina Dikko Umaru Radda ya shaida wa manema labarai jim kadan da isowarsa gida Nijeriya daga kasar Birtaniya

Rushewar Gini Yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 4 Da Kuma Jikkata 7 a Kano Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta...
14/07/2025

Rushewar Gini Yayi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 4 Da Kuma Jikkata 7 a Kano

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta tabbatar da mutuwar mutane huɗu da kuma jikkatar bakwai sakamakon rushewar wani gini a Abedi, Sabon Gari, ƙaramar hukumar Fagge, Jihar Kano.
Dr. Nuraddeen Abdullahi, Kwamishina a NEMA na Ofishin Shiyyar Kano ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN a yau Litinin a Kano.
a ce hukumar ta samu kiran gaggawa a jiya Lahadi, 13 ga Yuli, da misalin ƙarfe 6:49 na yamma cewa wani bene mai hawa uku da ba a kammala ba ya rushe a Abedi Sabon Gari, Kano.
Malam Abdullahi ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6:42 na yamma bayan mamakon ruwan sama da aka shafe tsawon lokaci ana yi.
“muna samu bayanin, sai mu kahanzarta tura tawagar ceto da neman agaji (SAR) zuwa wurin tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi masu ruwa da tsaki,” in ji shi.
Abdullahi ya ƙara da cewa, shaidu sun tabbatar da cewa mutane da dama na kasan ginin lokacin da ya rushe, kuma da dama sun makale ƙarƙashin baraguzan ginin.
Kwamishinan NEMA ya ce, zuwa ƙarfe 1:56 na safe a yau Litinin, an tabbatar da mutuwar mutane biyu, sannan an ceto mutane shida da s**a jikkata.
A cewarsa, karin mutane biyu sun mutu, sannan wani mutum guda ya ji rauni da misalin ƙarfe 5:41 na safe, kuma duk an garzaya da su zuwa Asibitin Kwararru na Murtala Muhammed da ke Kano domin kulawar likita.

Tsohon shugaban Najeriya Buhari ya rasu a birnin LandanBuhari, ya rasu yana da shekaru 81, a duniya bayan fama da jinya ...
13/07/2025

Tsohon shugaban Najeriya Buhari ya rasu a birnin Landan

Buhari, ya rasu yana da shekaru 81, a duniya bayan fama da jinya a kasar Birtaniya.

An samu wannan sanarwar daya iyalan sa, tare da tsaffin masu taimaka masa.

Ya mulki Najeriya, a mulkin soji, sannan ya mulke a mulkin farar hula a tsakanin shekarun 2015 zuwa 2023.

Address

Kano

Telephone

+2349034429947

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The Historica Nigeria Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to The Historica Nigeria Hausa:

Share