AREWA Daily Post

AREWA Daily Post Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AREWA Daily Post, Media/News Company, Ahmadu Bello Way, Kano.

Ziyarci Shafinmu na AREWA Daily Post domin Samun Sahihan Labarai da Rahotanni Fadakarwa Wa'azantarwa Ilimantarwa da Nishadantarwa mun Kuduri Aniyar tsage Gaskiya komai Dacinta

04/10/2021
02/10/2021

Dogo Dan Daura
Nokia Rike Charge
Madugu uban Tafiya
Rugum Babban motsi
Gatari kafi Saran shuka
Ba Sata ba cin Amana
Waken Suya ka gagari qwari
Jan Biro maganin dakikin yaro
Tsamiyar kabari Bakin Cikin masu kunu
Katangar Sukari kowa ya Tabata sai ya lasah
Likitan mahaukata kana musu magani suna zaginka
Kura ga bakin jini ga nisan kwana
Angon Aisha ba gaba da gaba ba kota baya sai an Shirya

Send a message to learn more

01/10/2021

MURNA MAI TATTARE DA KUKA😭
Yau Kasarmu NIGERIA take cika shekara 61 da samun Yen Cin kai

Wannan Abin murna ne
A bangare guda kuma muna kokawa bisa halin da Nigeria take ciki na Rashin Ayyukan Cigaba da ayyukan more Rayuwa

Har yanzu Nig babu ingantaccen tsarin ilimi lafiya ruwan sha wutar Lantarki Tituna samawa matasa Aikin yi

Uwa uba Rashin Tsaro duk wanda ya kwana ya tashi a Nigeria ya kwana da sanin muna fama da Matsalar Tsaro

Wannan Rashin Tsaron ya nakasa Nigeria kamar ta fannin kasuwanci da harkar Koyarwa da Noma da kiwon lafiya

Yanzu haka saboda Matsalar Tsaro Wasu Karatu ya gagaresu kasuwancinsu ya durkushi
Harkar Nomansu ya tsaya cak a wasu jihohi kamar Sokoto katsina Zamfara da Borno

Muna Addu'ar Allah ya kawomana karshen Matsalar Tsaro a Nigeria
Ameen

27/09/2021

Bin Umarnin Allah S.W.T
Da koyarwar Manzon Allah S.A.W Ita kadai ce mafita a wannan Zamani
Allah yasa mu Dace Ameen

20/09/2021
15/09/2021

Kowa Nada Rawar Takawa Dan Samar Da Zaman Lafiya a Arewacin Nigeria 🇳🇬
Kuzo mu Ceto Arewacin Nigeria Daga Halin da take Ciki

An Samu daidaito tsakanin Engr. Muaz Magaji  da Sheikh Kabiru Haruna Gombe.Hakan ya Biyo bayan wani rubutu da 'Dan Sarau...
11/09/2021

An Samu daidaito tsakanin Engr. Muaz Magaji da Sheikh Kabiru Haruna Gombe.

Hakan ya Biyo bayan wani rubutu da 'Dan Sarauniya ya wallafa da aka alakanta Kabiru Gombe da Wani sha'ani na Siyasar APC da PDP.

Muaz Magaji ya janye wadanchan kalamai.

SHIGA YAJIN AIKI A WANNAN LOKACI DA ƳAN-NAJERIYA SUKAFI BUKATAR KU BASHI NE MATAKI DA YA KAMATA KU DAUKA BA, SHUGABA BUH...
11/09/2021

SHIGA YAJIN AIKI A WANNAN LOKACI DA ƳAN-NAJERIYA SUKAFI BUKATAR KU BASHI NE MATAKI DA YA KAMATA KU DAUKA BA, SHUGABA BUHARI YA FAƊIWA LIKITOCI.

Fassara: Hon. Buhari Sallau Hadimin Shugaban kasa Muhammadu Buhari Bangaren Rediyo da Talabijin.

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ranar Juma'a a Abuja, yayi kira ga Ma'aikatan jinya da su komo bakin aikin su, ya bukaci Sauran masu tunanin tsunduma yajin aiki kan su zabi yin sulhu ta hanyar tattaunawa, komi tsawon lokaci da hakan zai dauka.

"Rayuwar mutane da za'a iya rasawa ko lalatarwa idan Likitoci s**a janye aikin su, sun isa susa azabi hanyar lumana da samun mafita akan Banbance Banbance dake tsakanin," Shugaban kasa ya nunar da Hakane, a yayin daya karbi Membobin Ƙungiyar likitoci ta Ƙasa (NMA) a fadar Gwamnati.

Shugaba Buhari ya bada tabbaci cewa za'a bisa dukkan hakkoki likitocin da suke bi, bayan an kammala tantancewa, ya nunar da cewa tsunduma yajin aiki a wannan lokaci Muhimmi da bukatar lafiya ga Ƙasar da Ƴan-kasa ba abu ne daya dace ba.

"Bada kariya ga Ƴan-Kasar mu ba abu ne daya kamata abar gwamnati ita kadai akai ba, abune da zamu dauka hakkin sa gaba da yan mu, wanda musamman kwararru a Fannin lafiya ke taka muhimmin rawa. Bari na fada kai tsaye wa likitocin dake yajin aiki, matakin tsunduma a dai dai wannan lokaci da Ƴan-Nijeriya ke bukatar ku fiye da kowani lokaci ba mataki ne daya dace ku dauka ba, koma wace irin sabani aka samu.

"Wannan Gwamnati tanada ƙyaƙƙyawan tarihi na biyan dukkanin bashi da ma'aikatan gwamnati ke binta, Ƴan fansho, da Ƴan kwangila kuma mun waiwayi bashi da Gwamnatocin baya s**a bari, da zarar an tantance duk abinda ya kamata bisa ka'ida, bashi na gaskiya da ma'aikatan jinya ke bi za'a biyasu.

“Na fahimci cewa wasu cikin Manyan bukatu goma sha biyu 12 na yajin aiki da akeyi abune da tuntuni an magance su. Duk da de abun sake dubi kan alawus na aiki kan hatsari ba'a tattauna sosai yadda ya kamata akai ba saboda yana yin dake ciki na likitoci dake yajin aiki."

Shugaban Ƙasa Buhari, yace matsala da dama kenan wanda Shugaban Ma'aikata ya miƙa saikula akai, kan batun cire abinda ake kira (House Officers) da cire likitoci daga shirin Bautar ƙasa na NYSC an karashi cikin batun da aka tura ga Hukumar Kula da daidaita albashi na ƙasa don tayi karin haske cewa za suci gaba da samun albashi harda tsarin kari kan bukatun su, sama da yawan wanda s**a saba samu.

Ya kara da cewa "Na bukaci cewa yarjejeniya da aka cimma a taron da akayi ranar 20th da 21st ga watan Ogusta dake cikin yarjejeniyar wanda na gani an fara aiki dashi,".

Don kara inganta Sashin lafiya, Shugaban kasa yace, an kara yawan kasafin kudi kuma an kaddamar da Kwamitin gyara sashen lafiya, karkashin Ma'taimakin Shugaban kasa, domin gano da magance inda ake da naƙaso a tsarin lafiya da yin daidaito da tsarin aiki mai kyau irin na ƙasashen Duniya, wanda jama'a s**a gamsu dashi.

"kuma muna Tallafawa shirye shirye don faÉ—aÉ—a inshuran lafiya da samar da karin kuÉ—aÉ—e ga Sashin lafiya.

“Muna da kalubale da yawa dake gaban mu da abubuwa da dama da zamuyi, ga Ɗunbin jama'a da muke dasu,

Ya kara da cewa "Don haka, ya dace na tunatas daku cewa, a matsayin ku na Manyan Ma'aikatan Jinya kuma Wakilai na daya cikin kungiyoyi dake da ƙima sosai a Duniya, Hakki dake wuyan ku karara yake na wanzuwan Ƴan-Nijeriya cikin lafiya.

"Bai kare kawai kan batun abubuwan walwalar membobin ku ba, amma abune daya kunshi ci gaba da sauke nauyi dake wuyan ku ga dukkan kasa baki daya, da fannin lafiyar da daidaituwar Al'amuran Kasar,".

Shugaba Buhari, yayi nuni da cewa hanyoyin tattalin arzikin Najeriya sama da Shekaru yana raguwa a hankali, hankali, tare da karuwar yawan Al'umma.

"Annoba Korona ya shafi Tattalin arzikin Duniya, duk da labarin mai dadin daya faru Ƴan kwanakin nan, na samun haɓakan tattalin arzikin Najeriya da sama da kaso biyar cikin watanni uku da s**a shuɗe, har yanzu akwai kalubale da muke son ganin mun magance kan asusun Kasar, kamar dai Sauran kasashe.

Shugaban kasa yace "Hanyar samun kudin shiga da Najeriya ta dogara dashi tsawon lokaci yana fiskantar koma baya a duniya, yawan Al'umman mu na karuwa ba dare ba rana, tashin hankali dake tattare da haka na karuwa daga kowani Bangaren, hakan na kara sanya matasa tsunduma cikin fitintunu.

Ƙungiya kamar ta likitoci NMA zata iya taka rawa mai Imfani da zai kawo daidaito a cikin zaman takewa,"

Shugaba ya yaba da irin aiki cigaba da kungiyar likitocin ta Ƙasa take taka wa, a matsayin ta na babbar kungiyar Ma'aikatan lafiya, musamman kan abinda ya shafi yajin aiki dake gudana.

"Wannan Shine rawar daya kamata kungiyar ta NMA ta taka, a matsayinta na kungiya mai Dattako, wanda membobin masu kamala da gogewar aiki ke jagoranta.

"Ina kuma alfahari da fahimtar cewa an samu cigaba matuka a asibitocin mu, kamar na raba tagwaye da aka haifa a like da juna, da kokarin Ma'aikatan mu na sashen lafiya Gurin tafiyar da Annobar Cutar Korona, Wanda abinda s**a yi ya janyo mana daraja a nan gida da kasashen ke tare, da bada gurbin aiki da akayi kwanan nan, ga daya daga cikin Abokan aiki a mukamin Ma'taimakin Babban Darakta a Hukumar Lafiya ta Duniya, har wayau Muna kara taya murna wa Dakta Chikwe Ihekweazu kan samun wannan mukamin."

Shugaba Buhari ya aiyana cewa Illar da Cutar Korona ta jefa Najeriya ciki har yanzu ba'a kammala goge shi ba, kana kuma dole mu hada kai Gurin magance ta.

Cikin jawabin sa, Ministan Lafiya, Dakta Osagie Ehanire, yace kungiyar NMA yana taka muhimmin rawa ga Cigaban sashen lafiya, musamman Gurin magance Annoba, aiki guri daidaituwa da lafiyan Al'umma.

Shugaban Ƙungiyar Likitoci NMA, Farfesa Innocent A. Ujah, ya godewa Shugaban kasa, na nadin membobin kungiyar a Muhimman matsayi a gwamnati, da amincewa da shirin, Medical Residency Act and immunization coverage.

Shugaban NMA, yace kungiyar ta damu da yajin aikin da likitoci s**a tsunduma, kuma yana iya kokarin don ganin an rage sassauta halin da majinyata suke ciki a Fadin ƙasa, yayin kuma ya Roki a samu sasanci cikin kankanin lokaci.

Shugaban Ƙungiyar NMA, ya godewa Shugaba Buhari, bisa kafa Jami'an Kimiyyan Lafiya a Karon farko a Otukpo jihar Benuwe, da Azare, jihar Bauchi da Ila Orangun, jihar Osun, Shugaban Ƙungiyar ya miƙa bukatar Samar da kudade da s**a dace ga Sabbin Jami'oin.

Ya tabbatar wa Shugaban kasa, cigaba da samun goyon baya na membobin kungiyar don kara inganta sashen lafiya a Ƙasar.

Mal. Garba Shehu:
Babban Mai Tallafawa Shugaban kasa A Kafofin Watsa Labarai da Wayar da kan Jama'a.
10th ga watan Satumba, 2021

11/09/2021


Meyake kawo yawaitar Mutuwar Aure a Kasar HAUSA?

Send a message to learn more

08/09/2021

TURƘASHI: Yadda Wata Mata Ta Shekara 40 Ba Ta Yi Bacci Ba

Wata mata mai suna Li Zhanying ta bayyana cewa tun tana da shekara 5 rabonta da bacci.

Matar ta fito ne daga ƙasar China kuma wannan ikirari nata ya baiwa Likitoci mamaki sosai.

Rahoton yace makwabtanta da dama sun so su ƙureta akan cewa bata bacci amma da an fara sai kowa ya ɓuge da bacci amma ita tana nan ƙuri ido biyu.

Matar ta riƙa shan maganin bacci amma duk a banza, bai mata magani ba.

Mijin matar ma ya tabbatar da wannan ikirarin inda yace tunda s**a yi aure matar tasa bata bacci.

Sai dai Likitoci a Beijing sun samar mata da maslaha inda a yanzu take samun baccin minti 10.

-Idon Mikiya

Mai kudin duniya Jeff Bezos ya gano maganin dake hana tsufaFitaccen attajiri dan kasar Amurka Jeff Bezos wanda aka ce ya...
06/09/2021

Mai kudin duniya Jeff Bezos ya gano maganin dake hana tsufa

Fitaccen attajiri dan kasar Amurka Jeff Bezos wanda aka ce yafi kowa kudi a duniya, ya gano wani magani wanda zai sanya mutum ya rayu har illa masha Allah ba tare da ya tsufa ba.

Shi dai wannan magani an kirkiro shi ne a wani katafaren dakin gwajagwajen kimiyyar halittu da aka kashe masa sama da dalar Amurka miliyan 270 domin inganta shi da kayan aiki, anyi amfani da kwararren mai gwajegwaje inda ya kirkiro wani sinadari da aka yi amfani da shi a jikin bera, kuma aka gano beran baya girma tunda aka yi amfani da sinadarin a jikinsa, yayin da aka samu wani beran da ba a sanya masa sinadarin ba kuma aka ga yana girma.

Binciken dai ya nuna za a iya amfani da sinadarin a jikin Bil adama kuma yayi aiki, ba tare da mutum ya tsufa ko kamanninsa sun canja ba.

Jaridar Daily Mail ta kasar Burtaniya ce ta ruwaito labarin.

Address

Ahmadu Bello Way
Kano
197

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA Daily Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share