Chakwalkwalin Siyasa Tv

Chakwalkwalin Siyasa Tv muhimman labaran Kano

21/09/2025

An nada Dr. Abdullahi Umar Ganduje Khadimul Qur'an

21/09/2025

Mutanen da s**a taba amsar Digirin girmamawa a Najeriya

21/09/2025

Menene Abinda Danbilki Kwamanda ke nufi da wannan Sabuwa samfurin hular?

Har yanzu Dan Bello bai yabawa Gwamnatin Kano ba akan Farfado da ilimi da Gwamnan Kano yai ba musamma nasarar da ɗaliban...
20/09/2025

Har yanzu Dan Bello bai yabawa Gwamnatin Kano ba akan Farfado da ilimi da Gwamnan Kano yai ba musamma nasarar da ɗaliban Kano s**a samu a jarabawar NECO.

Sannan har yanzu bai yabawa Gwamnan Kano ba kan ɗaukar ma'aikata sama da 2,000 da yai a jiya da alkawarin daukar sama da ma'aikata 4300 waɗanda kawai an dauke su ne domin koyarwa a makarantun Kano domin kara bunkasa ilimi.

Ko dai Dan Bello idon sa baya hango masa alkairi ne sai sharri

Raayin Salisu Editor

20/09/2025

Wane fata zaku yi masa?

MUHAWARA: Tsakanin Gawuna Da Sanata Barau Jibrin Wa Ya Kamata Ya Yiwa APC Takarar Gwamnan Kano A Zaɓen 2027 ?A Kafta....
20/09/2025

MUHAWARA: Tsakanin Gawuna Da Sanata Barau Jibrin Wa Ya Kamata Ya Yiwa APC Takarar Gwamnan Kano A Zaɓen 2027 ?

A Kafta....

Wannan sune s**a kafa Jam'iyar APC a 2013.Shin kunga suna ko saka hannun kwankwaso?
20/09/2025

Wannan sune s**a kafa Jam'iyar APC a 2013.

Shin kunga suna ko saka hannun kwankwaso?

WATA SABUWA:Ko menene ya hana Sunusi lamido sunusi Zuwa Daurin Auren Dan Kwankwaso?
20/09/2025

WATA SABUWA:Ko menene ya hana Sunusi lamido sunusi Zuwa Daurin Auren Dan Kwankwaso?

Zan iya barin NNPP – Inji Dan Majalisa Abdulmumin Jibrin KofaAbdulmumin Jibrin, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazab...
05/09/2025

Zan iya barin NNPP – Inji Dan Majalisa Abdulmumin Jibrin Kofa

Abdulmumin Jibrin, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Kiru/Bebeji kuma na kusa da Jagoran jam’iyyar NNPP na kasa, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce bai kamata a dauki abin mamaki ba idan ya bar jam’iyyar.

Ya ce kuma ya isa ya dauki matsayar kansa a siyasa bisa abin da ya ga ya fi masa alheri.

Yayin da yake zantawa da DCL Hausa, dan majalisar ya ce ya shiga Kwankwasiyya tun yana da kudi, inda ya yi amfani da dukiyarsa wajen taimakawa tafiyar, kamar yadda ita ma ta taimaka masa wajen dawowa majalisar wakilai a 2023.

Ya ce, “Ko jam’iyyar NNPP kanta ta bayyana cewa a shirye take don yin tattaunawa da sauran jam’iyyu, don haka ba dole bane in bi hanyar jam’iyya. Ni dai na isa na dauki matsayar da na ga ta fi mini kyau.”

Sai dai ya ce duk da haka zai ci gaba da girmama Kwankwaso a matsayin jagoransa, ko da kuwa ba su kasance a jam’iyya daya ba.

“Ko da ban kasance tare da Kwankwaso ba, ba zan taba zagin shi ba, kamar yadda ban taba zagin Ganduje ba ko da mun rabu. Ban taba neman kwangila ba duk da cewa na taka rawa wajen nasarar NNPP a Kano. Kwankwasiyya ta tsaya min, amma ni ma na tsaya mata.”

Dan majalisar ya kara da zargin cewa babu wani babban dan siyasar arewa da ya taimaka masa lokacin da aka dakatar da shi daga majalisar wakilai a 2016, bayan ya zargi shugabannin majalisar da yin “Aringizo a kasafi.”

Lokacin da aka tambaye shi ko yana shirin barin NNPP, Jibrin ya ce, “Komai zai iya faruwa. Zan iya ci gaba da zama a NNPP, zan iya komawa APC, zan iya shiga ADC ko PDP ko ma PRP. Zan iya zuwa inda na ga dama. Duk lokacin da na yanke shawara, zan bayyana matsayina.”

RARARA ZAI AURAR DA YARANSA 10Wannan sune jerin angwaye da Amare wayanda Mawaki Dauda Kahutu Rarara zai ɗaurawa aure ran...
05/09/2025

RARARA ZAI AURAR DA YARANSA 10

Wannan sune jerin angwaye da Amare wayanda Mawaki Dauda Kahutu Rarara zai ɗaurawa aure ranar 26/09/25

Nan da kwana 21 insha Allahu za'ayi wannan kataparen biki a jahar kano.

Rarara shine wanda ya ɗauki nauyin duk wani abu da ya shafi wannan biki, tun daga ɓangaren angwaye harda amaren su.

ZAƁEN 2027: Zan Iya Yanke Wa Kaina Jam‘iyyar Siyasar Da Ta Fi Dacewa Da Ni Ba Tare Da Neman Shawara Wurin Kowa Ba, Inji ...
03/09/2025

ZAƁEN 2027: Zan Iya Yanke Wa Kaina Jam‘iyyar Siyasar Da Ta Fi Dacewa Da Ni Ba Tare Da Neman Shawara Wurin Kowa Ba, Inji Jibrin Kofa

Dan majalisar wakilai mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru/Bebeji a jihar Kano, kuma wanda ke cikin jiga-jigan siyasar Kwankwasiyya, Abdulmumin Jibrin Kofa, ya bayyana haka a yayin hirarsa da gidan talabijin na Channels, ya ce, akwai kyakkyawar fahimta da girmamawa tsakaninsa da Shugaba Tinubu.

Me zaku ce?

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Juma'a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun Maulidi.
03/09/2025

Gwamnatin Najeriya ta ayyana ranar Juma'a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun Maulidi.

Address

Kuntau
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Chakwalkwalin Siyasa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share