Chakwalkwalin Siyasa Tv

Chakwalkwalin Siyasa Tv muhimman labaran Kano

04/06/2025

Yes

Manufofin Kafa Ƙungiyar Gwale Social Media Crew Da Matsayar Ta A Siyasar Ƙaramar Hukumar GwaleAn kafa wannan ƙungiyar ta...
04/06/2025

Manufofin Kafa Ƙungiyar Gwale Social Media Crew Da Matsayar Ta A Siyasar Ƙaramar Hukumar Gwale

An kafa wannan ƙungiyar ta Gwale Social Media Crew ne ƙarƙashin jagorancin shugaban ta Hon. Junaidu Aminu Kilishi, Domin haɗa kan dukkanin matasan jam'iyyar APC maza da mata musamman masu amfani da kafofin sada zumunta waɗanda s**a fito daga gidajen siyasa daban-daban duk domin kawo ci gaba da daidaito a tsakanin su.

Kuma tun kafa wannan ƙungiya an samar mata da shugabanni da s**a fito daga mazaɓu 10 da ake da su a ƙaramar hukumar Gwale, Sannan tana da mambobi kusan 500 daga sassa daban-daban na Gwale, Wanda ta yi ƙoƙarin samar musu da tallafin kayan Abinci tun cikin Azumi a wannan lokacin wasu sun amfana da tallafi Kuɗin duk domin su kasance cikin walwala da jin daɗi.

Babban burin wannan ƙungiya shi ne samar da haɗin kai da magana da murya ɗaya ta yadda za a ci gajiyar siyasa, Ba kamar a baya da ake tafiya a rarrabe ba. Bugu da ƙari kuma a gujewa cin mutunci da nuna ƙyama ga wani ko wasu daga cikin ƴan siyasa da jagororin jam'iyyar APC a ƙaramar hukumar Gwale wanda Alhamdulillah an samu nasara da ci gaba sosai a wannan ɓangare.

A kasancewar mu ƴan adam kuma Media tana da faɗi da girma muna sanar da duk wani ɗan jam'iyyar APC a Gwale da idanun mu ko hannun mu bai kai kan sa ba, Da su yi mana magana da mu ta kai tsaye ko ya sanar da wanda ya san yana ciki domin shigowa shima a dama da shi.

Kazalika, Gwale Social Media Crew, Ta bawa kowane mamban ta damar tallata gwanin sa da yake da shi a cikin jam'iyyar APC, Amma ba ta yadda a fake da wani tsagi ko ɗan takara a ci mutuncin wani ba wanda ko a addinin Musulunci da mutuntakar ɗan adam wannan ba daidai ba ne, Wanda an yi nasara kasacewar dama matasan jam'iyyar APC a Gwale masu ilimi ne da tarbiyya da sanin yakamata.

Matsayar wannan ƙungiya mai suna a sama shi ne tsayawa kai da fata ta jajirce kuma tana biyayya ga shugaban jam'iyyar APC na jihar Kano, Alh. Abdullahi Abbas (Ɗan Sarki Jikan Sarki) da sauran jagororin jam'iyyar APC musamman akan daukkanin abun da "ƊAN SARKI" ya yanke ko ya yi umarni a kowane mataki a faɗin ƙaramar hukumar Gwale da Kano da ƙasa baki ɗaya, Domin haka har yanzu ƙungiyar Gwale Social Media Crew ba ta da wani ɗan takara ko wanda take goyon bayan sa a kowane mataki, Muna jiran lokacin fitar da uwar jam'iyya za ta yi umarni, Kuma muna biyayya da duk jam'iyya a matakin mazaɓu da ƙaramar hukumar da jihar baki ɗaya akan abun da ta yanke.

A ƙarshen ƙofar mu a buɗe take domin karɓar gyara a wajen da muka yi kuskure mu gyara, Kuma muna kira da mambobin mu da cewar kar mu sake mu saka kan mu a rigingimu siyasa ko zagi da cin mutunci duk ba mafita ba ce a siyasa, Ku zo mu haɗa kai mu samawa kan mu mafita da ci gaba domin gyaran goben mu, Allah ya ƙara yi mana jagora ya ci gaba da haɗa kan jagororin jam'iyyar APC a Gwale ya ba mu nasara a zaɓen 2027, Amin

Hon. Junaidu Aminu Kilishi, Shugaban Ƙungiyar Gwale Social Media Crew

23/05/2025

Kadan daga bakin Hamdiyya Sidi Sharif

22/05/2025

Abinda ya faru da hamdiyya Sidi Sharif

22/05/2025

Kwankwaso Baida Tsuntsu Baida Tarko

20/05/2025

Innanillahi wa inna ilaihir raji'un ayi temako don Allah

20/05/2025

Innanillahi wa inna ilaihir raji'un

Mawaƙin Siyasa Dauda Kahutu Rarara Ya Gabatar Da Sabuwar Motar Alfarma Da Ya Saya Sati Ɗaya Bayan Auransa Da Jarumar Kan...
18/05/2025

Mawaƙin Siyasa Dauda Kahutu Rarara Ya Gabatar Da Sabuwar Motar Alfarma Da Ya Saya Sati Ɗaya Bayan Auransa Da Jarumar Kannywood A'isha Humaira

Wane fata zaku yi masa?

"Babu wani abu da nake zaton zai iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027,” — Tanko Yakasai.Me zaku ce ?
18/05/2025

"Babu wani abu da nake zaton zai iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027,” — Tanko Yakasai.

Me zaku ce ?

Shugaban kasa, Bola Tinubu, Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi, da tsohon gwamnan Eki...
18/05/2025

Shugaban kasa, Bola Tinubu, Tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour, Mista Peter Obi, da tsohon gwamnan Ekiti, Kayode Fayemi, sun gana a wajen taron nadin Paparoma Leo na 14 da ya wakana a ranar Lahadi a birnin Rome na kasar Italy

18/05/2025

Sha'aban Sharada

18/05/2025

ABBA DAMBATTA DDN

Address

Kuntau
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Chakwalkwalin Siyasa Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share