Daily News 24 Hausa

Daily News 24 Hausa • Labarai • Nishadi • Hira • Al’adu • Wasanni
(1)

INEC ta ayyana Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun na shekarar 2026.▪️ Adeleke (Accord): ...
16/08/2026

INEC ta ayyana Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Osun na shekarar 2026.

▪️ Adeleke (Accord): ƙuri’u 511,067
▪️ Oyebamiji (APC): ƙuri’u 444,815
▪️ Adeleke ya lashe ƙananan hukumomi 19 cikin 30.

Ku karanta cikakken labarin da ƙarin bayanan zaɓen a Daily News 24. 👇

https://dailynews24ng.com/inec-declares-adeleke-winner-osun-election-2026/

EPL: Obi Mikel ya yi wa magoya bayan Arsenal ba’a kan rashin lashe gasar Champions LeagueTsohon ɗan wasan tsakiyar Chels...
11/08/2026

EPL: Obi Mikel ya yi wa magoya bayan Arsenal ba’a kan rashin lashe gasar Champions League

Tsohon ɗan wasan tsakiyar Chelsea, John Obi Mikel, ya yi wa magoya bayan Arsenal ba’a, bayan ƙungiyar ta kasa ɗaukar Vinicius Junior daga Real Madrid a kasuwar musayar ’yan wasa ta bana.

Vinicius ya zama ɗaya daga cikin ’yan wasan da Arsenal ta nuna sha’awar ɗauka ba zato ba tsammani a wannan bazarar.

Rahotanni sun ce Arsenal ta shirya bai wa ɗan wasan ƙasar Brazil albashin da zai sanya shi zama ɗan wasan da ya fi kowa karɓar albashi a tarihin gasar Premier ta Ingila.

Sai dai a ƙarshe, ɗan wasan mai shekaru 26 ya tsawaita kwantiraginsa da Real Madrid.

Da yake magana a sabon shirin **The Obi One Podcast**, Obi Mikel ya yi nuni da cewa Arsenal ba ta taɓa lashe kofin Champions League ba, sannan ta lashe kofin Premier League sau ɗaya kacal cikin shekaru 22.

Ya ce hakan na nufin Vinicius ba shi da dalilin barin Real Madrid, inda ya riga ya lashe kofuna da dama.

Kwankwaso ya yi Allah-wadai da kalaman Jingir, ya ce Kano ta yi watsi da kalaman rarrabuwar kaiƊan takarar mataimakin sh...
11/08/2026

Kwankwaso ya yi Allah-wadai da kalaman Jingir, ya ce Kano ta yi watsi da kalaman rarrabuwar kai

Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress, NDC, Rabi’u Musa Kwankwaso, ya yi Allah-wadai da kalaman da ake dangantawa da malamin addinin Musulunci, Sheikh Sani Yahaya Jingir, na bayyana Kiristoci a matsayin “kafirai” tare da cewa waɗanda ba su amince da tsarin takarar Musulmi da Musulmi ba su bar Najeriya.

Kwankwaso ya bayyana damuwarsa ne a cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook da aka tabbatar a ranar Litinin, inda ya ce ya kamata a yi tir da duk wasu kalamai da za su iya haifar da rarrabuwar kai da rashin haɗin kai, musamman a wannan muhimmin lokaci a tarihin ƙasar.

Fadar shugaban kasa ta kammala shirin miƙawa Shugaban Tinubu ƙudurin dokar kafa ƴan sandan jihohi..Fadar shugaban ƙasa t...
04/08/2026

Fadar shugaban kasa ta kammala shirin miƙawa Shugaban Tinubu ƙudurin dokar kafa ƴan sandan jihohi..
Fadar shugaban ƙasa ta sanya ranar 3 ga watan Satumban 2026 a matsayin ranar da za a gabatar wa Shugaba Bola Tinubu da ƙudirin dokar kafa ƴan sandan jihohi domin nazari, don tabbatar da cewa an shirya tsaf da kuma nuna cewa gwamnati na da niyyar aiwatar da wannan mataki a lokaci mai kyau.

Matakin na daya daga cikin jadawalin makonni bakwai da gwamnatin tarayya ta tsara domin samar da cikakken tsarin doka da zai ba da damar aiwatar da shirin.

Shugaban ƙwamitin aiki na fadar shugaban ƙasa kan ƙudirin dokar tsaron ƴan sanda ta ƙasa, Femi Gbajabiamila, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin bayan taron farko na kwamitin da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, don tabbatar da cewa jama'a suna samun sahihan bayanai daga masu ruwa da tsaki.

Gbajabiamila ya ce kwamitin ya riga ya fara aikin gudanarwa kan shirya ƙudirin dokar, yana mai cewa aikin gaba daya zai gudana daga 27 ga watan Yuli zuwa 14 ga watan Satumban 2026, kamar yadda jadawalin da aka amince da shi ya tanada.

A watan Yulin da ya gabata ne shugaba Bola Tinubu ya ƙaddamar da wannan kwamitin, tare da ɗora masa alhakin samar da tsarin doka da zai zama tubalin aiwatar da tsarin ƴan sandan Jihohi a Najeriya.

04/08/2026

BIDIYO: Majalisar Dokokin Kano ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin Bebeji, Rogo da Bagwai

Kano: Majalisar Dokoki ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin Bebeji, Rogo da Bagwai---Majalisar Dokokin Jihar Kano...
04/08/2026

Kano: Majalisar Dokoki ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin Bebeji, Rogo da Bagwai

---
Majalisar Dokokin Jihar Kano ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomin Bebeji, Rogo da Bagwai kan zargin karkatar da kuɗaɗe da yiwa dokar aiki karan tsaye.

Shugaban Majalisar Jibril Isma'il Falgore, ya umarci mataimakan shugabannin da su karɓi ragamar mulki nan take don tabbatar da ci gaba da ayyuka.

An mika batun ga Kwamitin Harkokin Ƙananan Hukumomi don gudanar da cikakken bincike cikin makonni 10.

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta amince da biyan fam miliyan 77 domin sayen ɗan wasan tsakiyar Newcastle United kuma ...
01/08/2026

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal ta amince da biyan fam miliyan 77 domin sayen ɗan wasan tsakiyar Newcastle United kuma ɗan ƙasar Brazil, Bruno Guimarães.

Rahotanni sun ce ƙungiyoyin biyu sun kai ga cimma yarjejeniya kan kuɗin cinikin ɗan wasan mai shekaru 28, wanda ya kasance ɗaya daga cikin fitattun 'yan wasan tsakiyar Newcastle.

Idan aka kammala sauran matakan cinikin, Bruno Guimarães zai koma Arsenal domin ƙarfafa tsakiyar fili gabanin fara kakar wasa mai zuwa.

Jam’iyyar PDP tsagin Tanimu Turaki ta sanar da cewa ta mika sunan tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ga Hukumar Za...
31/07/2026

Jam’iyyar PDP tsagin Tanimu Turaki ta sanar da cewa ta mika sunan tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Jonathan, ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen 2027.

Mai magana da yawun tsagin, Ini Ememobong, ya ce sun kuma mika sunayen ’yan takarar gwamnoni da na majalisun dokoki, inda ya bayyana cewa an yi hakan ne ta hanyar kai takardu kai tsaye bayan sun kasa samun damar amfani da shafin yanar gizon INEC.

Ya ce matakin ya dace da tanade-

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce a karon farko tattalin arzikin Najeriya ya samu cigaba a cikin sauri...
31/07/2026

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce a karon farko tattalin arzikin Najeriya ya samu cigaba a cikin sauri fiye da yawan al'ummar ƙasar, sakamakon sauye-sauyen da Babban Bankin kasa (CBN) ya aiwatar.

Sanusi ya bayyana hakan ne yayin da yake jawabi a taron kolin tattalin arzikin kasa karo na 31, inda ya yabawa CBN kan yadda ya daidaita tattalin arziki bayan shekaru na yawaitar kuɗi a kasuwa da rashin daidaiton tsarin kuɗi.

Najeriya ta shiga wata haɗakar ƙasashe ƙarƙashin jagorancin Saudiyya domin kafa rundunar tsaro ta musamman da za ta kare...
31/07/2026

Najeriya ta shiga wata haɗakar ƙasashe ƙarƙashin jagorancin Saudiyya domin kafa rundunar tsaro ta musamman da za ta kare zirga-zirgar jiragen ruwa a Mashigin Bab al-Mandab, bayan barazanar hare-haren mayaƙan Houthi da ke Yemen.

Sanarwar da Ma'aikatar Tsaron Saudiyya ta fitar ta bayyana cewa ƙasashe 14 ne s**a amince da shiga wannan haɗakar. Ƙasashen sun haɗa da Bahrain, Bangladesh, Djibouti, Masar, Jordan, Kuwait, Najeriya, Pakistan, Qatar, Somalia, Sudan, Turkiyya, Yemen da kuma Saudiyya.

Manufar rundunar ita ce tabbatar da tsaron Mashigar Bab al-Mandab da Tekun Bahar Maliya da kuma Tekun Gulf of Aden, domin kare jiragen ruwa da hanyoyin kasuwanci da makamashi daga hare-haren Houthi.

Matakin ya biyo bayan ƙarin barazanar da mayaƙan Houthi s**a yi ga jiragen ruwa masu alaƙa da Saudiyya, lamarin da ya ƙara dagula tsaro a yankin tare da haifar da fargabar tangarɗa ga kasuwancin duniya.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News 24 Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News 24 Hausa:

Share