Daily News 24 Hausa

Daily News 24 Hausa • Labarai • Nishadi • Hira • Al’adu • Wasanni
(2)

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da hade Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi domin samar da s...
01/06/2026

Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da hade Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi domin samar da sabuwar ma’aikata guda daya.

Sabuwar ma’aikatar za ta rika aiki da sunan Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 1 ga Yuni, 2026, wadda Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, ya sanya wa hannu.

A cewar gwamnati, an dauki wannan mataki ne domin kara inganta tafiyar da harkokin gwamnati, hada kai wajen tsara manufofi da kuma amfani da albarkatu yadda ya kamata wajen kula da harkokin ruwa da muhalli a fadin jihar.

"An ci amanar mutane fiye da miliyan 1 da s**a zabi gwamnatin Kano, kuma suna nan ba zasu kyale ba a zabe mai zuwa"Sanat...
01/06/2026

"An ci amanar mutane fiye da miliyan 1 da s**a zabi gwamnatin Kano, kuma suna nan ba zasu kyale ba a zabe mai zuwa"

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar mataimakin shugaban kasa a NDC.

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya karɓi ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar mazab...
01/06/2026

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya karɓi ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar mazabar Makoda, Muhammad Ahmad Tomas, bayan ya koma jam’iyyar APC daga jam’iyyar NDC.

Tomas ya sanar da komawarsa APC ne a yayin wata ziyara da ya kai gidan Barau da ke Abuja a ranar Litinin.

Ya samu rakiyar shugabannin ƙananan hukumomin Makoda da Dambatta, Alhaji Isa Currency da Alhaji Jamilu Abubakar Dambatta.

A wata sanarwa da ya fitar, Barau ya bayyana komawar ɗan majalisar a matsayin wani muhimmin ci gaba ga jam’iyyar APC, yana mai cewa hakan na nuna aniyar Tomas ta mara wa ci gaba da kyakkyawan shugabanci baya.

Mazauna jihar Borno sun bayyana rashin jin daɗin su kan abin da s**a kira rashin kulawar gwamnatin tarayya bayan sace ɗa...
01/06/2026

Mazauna jihar Borno sun bayyana rashin jin daɗin su kan abin da s**a kira rashin kulawar gwamnatin tarayya bayan sace ɗalibai 42 na firamare da ƙaramar sakandare a ƙauyen M***a da ke ƙaramar hukumar Askira/Uba.

Sun yi zargin cewa gwamnati ta mayar da hankali sosai kan wani makamancin hari da ya faru a jihar Oyo, inda aka tura manyan jami’an gwamnati domin duba halin da ake ciki, yayin da lamarin Borno bai samu irin wannan kulawa ba.

Shugaban gamayyar Ƙungiyoyin Farar Hula ta Borno, Abubakar Suleiman, ya ce akwai bambanci a yadda ake tafiyar da batutuwan tsaro a yankuna daban-daban na Najeriya.

A cewarsa, duk da cewa an yi garkuwa da mutane sama da 400 a Ngoshe a watan Mayu tare da sace ɗalibai 42 a Askira/Uba, babu wata babbar tawaga daga gwamnatin tarayya da ta kai ziyara ko ta nuna cikakken matakin gaggawa kan lamarin.

Wata kungiyar matasan Kiristocin arewa ta bayyana jin dadin ta kan amincewar da Shugaba Bola Tinubu ya yi a dauki masu g...
01/06/2026

Wata kungiyar matasan Kiristocin arewa ta bayyana jin dadin ta kan amincewar da Shugaba Bola Tinubu ya yi a dauki masu gadin dazuzzuka 1,000 a Jihar Oyo domin inganta tsaro.

Kungiyar ta ce wannan mataki zai taimaka wajen dakile ayyukan masu laifi a yankunan dazuzzuka, tare da kara tabbatar da zaman lafiya da kariyar al'umma.

Sai dai kungiyar ta yi gargadin cewa kada a samu jinkiri wajen aiwatar da shirin, tana mai nuni da yadda wasu irin tsare-tsaren tsaro a wasu jihohi s**a fuskanci tsaiko.

Tawagar masu tattaunawa ta Iran ta dakatar da musayar saƙonni da Amurka ta hannun masu shiga tsakani, bayan hare-haren d...
01/06/2026

Tawagar masu tattaunawa ta Iran ta dakatar da musayar saƙonni da Amurka ta hannun masu shiga tsakani, bayan hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kaiwa a Lebanon, kamar yadda kafafen yaɗa labarai na Iran s**a ruwaito.

Jami’an Iran sun bayyana cewa ci gaba da hare-haren da ake kaiwa a Lebanon na kawo cikas ga ƙoƙarin sulhu da tattaunawar diflomasiyya tsakanin Tehran da Washington.

Sun kuma jaddada cewa ba za a samu ci gaba a tattaunawar ba matuƙar ba a dakatar da hare-haren ba.

Rahotanni sun nuna cewa Iran na kallon rikicin Lebanon a matsayin wani muhimmin ɓangare na tattaunawar da ake yi da Amurka, inda ta danganta yiwuwar komawa tattaunawa da samun tsagaita wuta da dakatar da farmakin da Isra’ila ke kaiwa yankunan da ke ƙarƙashin kulawar Hezbollah.

Wannan mataki na Iran na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin Gabas ta Tsakiya ke ƙara tsananta, lamarin da ya haifar da fargabar ƙara tabarbarewar dangantaka tsakanin ɓangarorin da ke rikicin.

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta w...
01/06/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta wani saƙo da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ke ikirarin cewa yana shirin jagorantar zanga-zanga kan tabarbarewar tsaro a ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Kwankwaso ya bayyana cewa saƙon ƙarya ne kuma ba ya wakiltar ra’ayin sa ko na jam’iyyar sa. Ya yi kira ga jama’a da su guji yaɗa bayanan da ba su da tushe.

Ya ce shi ko jam’iyyar sa basa goyon bayan duk wani mataki da zai iya haddasa rikici, karya doka ko lalata rayuka da dukiyoyin al’umma.

Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a wani masallaci da ke kauyen Unguwan Namama a karamar hukumar Giwa ta j...
01/06/2026

Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kai hari a wani masallaci da ke kauyen Unguwan Namama a karamar hukumar Giwa ta jihar Kaduna, inda s**a kashe mutum daya tare da yin awon gaba da wasu mutane da dama.

Harin ya faru ne a daren Juma’a da misalin karfe 8:00 na dare yayin da jama’a ke gudanar da ibada a masallacin.

Rahotanni sun bayyana cewa maharan sun bude wa masu sallah wuta, lamarin da ya haddasa firgici da rudani a yankin.

Rahotanni sun nuna cewa rundunar sojin Najeriya tare da hadin gwiwar rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka (AFRICOM...
01/06/2026

Rahotanni sun nuna cewa rundunar sojin Najeriya tare da hadin gwiwar rundunar sojin Amurka da ke kula da Afirka (AFRICOM) sun kashe mayakan kungiyar ISWAP guda 21 a wani harin sama da aka kai a yankin Arege da ke karamar hukumar Kukawa a jihar Borno.

Majiyoyi sun bayyana cewa an gudanar da harin ne a ranar Asabar bayan bayanan sirri da sa ido sun tabbatar da kasancewar mayakan kungiyar a yankin.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya sanar da ficewarsa daga Jam'iyyar ADC bayan Atiku Abubakar ya zam...
01/06/2026

Tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir Lawal, ya sanar da ficewarsa daga Jam'iyyar ADC bayan Atiku Abubakar ya zama ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar a zaɓen 2027.

Wata sanarwa da Babachir Lawal ya fitar ta bayyana cewa sakamakon zaɓen fidda gwanin shugaban ƙasa na ADC an tsara shi ne domin bai wa Atiku Abubakar nasara, lamarin da ya sa ya yanke shawarar ta barin jam'iyyar.

Yace tun da farko an tsara zaben domin nasarar Atiku.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Daily News 24 Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Daily News 24 Hausa:

Share