01/06/2026
Gwamnatin Jihar Kano ta sanar da hade Ma’aikatar Albarkatun Ruwa da Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi domin samar da sabuwar ma’aikata guda daya.
Sabuwar ma’aikatar za ta rika aiki da sunan Ma’aikatar Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi.
Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da kwanan watan 1 ga Yuni, 2026, wadda Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, ya sanya wa hannu.
A cewar gwamnati, an dauki wannan mataki ne domin kara inganta tafiyar da harkokin gwamnati, hada kai wajen tsara manufofi da kuma amfani da albarkatu yadda ya kamata wajen kula da harkokin ruwa da muhalli a fadin jihar.