TTN Hausa

TTN Hausa TTN Hausa kafa ce mai zaman kanta da aka samar don kawo sahihan labarai da rahotanni cikin harshen Hausa.

Ku tura mana sakonninku ta WhatsApp a +234 703 662 1583

Ku bi channel dinmu: https://whatsapp.com/channel/0029VbAuIz77dmebznWVa31L

Matatar Dangote ta rage farashin dizal daga ₦1,800 zuwa ₦1,600 kan kowace lita yayin da ake samun ƙaruwar shigo da man f...
28/05/2026

Matatar Dangote ta rage farashin dizal daga ₦1,800 zuwa ₦1,600 kan kowace lita yayin da ake samun ƙaruwar shigo da man fetur a Najeriya.

Rahoton TheCable ya bayyana cewa an aiwatar da rage farashin ne a ranar Talata 26 ga Mayu.

Jami’in hulɗa da jama’a na PETROAN, Joseph Obele, ya ce matakin na da alaƙa da ƙaruwar gasa a ɓangaren man fetur a ƙasar.

Ragin ya zo ne a daidai lokacin da farashin ɗanyen mai a kasuwannin duniya ke ci gaba da sauka.

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya lashe zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a daren La...
28/05/2026

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya lashe zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC a daren Laraba bayan samun ƙuri’u 1,846,370.

A cewar jami’in tattara sakamakon zaɓen, Tunde Ogbeha, Atiku ya kayar da Rotimi Amaechi da Mohammed Hayatu-Deen.

Bayan karɓar tutar jam’iyyar, Atiku ya buƙaci abokan takararsa su haɗa kai da shi domin tunkarar zaɓen 2027.

Sai dai Amaechi da Hayatu-Deen sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓen, inda s**a zargi an samu kura-kurai da hana wasu kaɗa ƙuri’a.

Sanata Sabo Muhammad Nakudu ya lashe zaɓen fidda gwani na gwamnan Jigawa na jam’iyyar ADC bayan kammala tattara ƙuri’u a...
28/05/2026

Sanata Sabo Muhammad Nakudu ya lashe zaɓen fidda gwani na gwamnan Jigawa na jam’iyyar ADC bayan kammala tattara ƙuri’u a daren ranar Laraba.

Rahoton ya nuna cewa ya samu ƙuri’u 35,939 inda ya kayar da Alhaji Bashir Muhammad Adamu Jumbo da ya samu 19,537.

A cewar kwamitin zaɓen, an gudanar da tattara sakamakon a cikin awanni sama da 48 kafin sanar da nasarar a ƙarshe.

Nakudu ya ce “Babu wanda yai nasara ko rashin nasara,” yana mai kira ga haɗin kai a jam’iyyar ta ADC.

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, da Mohammed Hayatu-Deen sun yi watsi da sakamakon zaɓen fidda gwani na shugaban ...
27/05/2026

Tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi, da Mohammed Hayatu-Deen sun yi watsi da sakamakon zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa na ADC da aka gudanar a faɗin Najeriya. Sun yi zargin hana wasu mambobin kaɗa ƙuri’a da kuma maguɗin zaɓe a wasu wurare. A cewar sanarwar da Amaechi ya fitar ranar Talata, ba zai amince da sakamakon da bai cika ƙa’idoji na gaskiya da adalci ba. Rahotanni sun nuna cewa Atiku Abubakar na kan gaba yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaɓen.

26/05/2026



Rana ta 88 da abubuwan da suke faruwa a cikinta a ci gaba da rikicin hadin gwiwar Amurka da Isra'ila kan Iran.

A ranar Talatar nan a dutsen Arfa kusa da Makka, sama da musulmi miliyan 1.5 s**a gudanar da addu’o’i a lokacin aikin Ha...
26/05/2026

A ranar Talatar nan a dutsen Arfa kusa da Makka, sama da musulmi miliyan 1.5 s**a gudanar da addu’o’i a lokacin aikin Hajji, duk da tsananin zafin rana da ya kusa kaiwa digiri 40 zuwa 44 a Saudiyya.

Mahajjata sanye da fararen tufafi sun cika dutsen da addu’o’i da karatun Alƙur’ani tun daga wayewar gari a wajen da aka saurari hudubar ƙarshe ta Annabi Muhammad (SAW).

Rahoton AFP ya bayyana cewa duk da rikicin Gabas ta Tsakiya, an samu ƙarin mahajjata daga ƙasashen duniya a bana fiye da shekarar 2025.

Bayan Arfa, mahajjata za su wuce Muzdalifah domin kwana da kuma tattara ƙananan duwatsu don gudanar da jifan Shaidan a Mina.

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) a ranar Litinin 25 ga Mayu ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Tarayya da ke Abuja da...
26/05/2026

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta (INEC) a ranar Litinin 25 ga Mayu ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin Kotun Tarayya da ke Abuja da ya soke jadawalin lokutan gudanar da zaɓen fidda gwani da tsayar da ƴan takara na 2027, tare da neman a dakatar da aiwatar da hukuncin.

A hukuncin da Mai Shari’a Mohammed Umar ya yanke a makon da ya gabata, kotu ta ce, INEC ba ta da ikon sanya wa jam’iyyu jadawalin gudanar da zaɓen fidda gwani.

INEC ta ce kotun ta yi kuskure wajen fassarar sashe na 29, 82 da 84 na Dokar Zaɓe ta 2026, tare da rashin la’akari da wasu hujjojin doka da ta gabatar.

Rahoton NAN ya bayyana cewa hukumar ta shigar da ƙarar ne bisa dalilai guda tara daban-daban.

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da JohnMary Jideobi ya shigar da ke ƙalubalantar cancantar tsohon ...
26/05/2026

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yi watsi da ƙarar da JohnMary Jideobi ya shigar da ke ƙalubalantar cancantar tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ta yin takara a zaɓen 2027, saboda rashin hurumin shari’a daga mai shigar da ƙara.

Alƙalin kotun, Mai Shari’a Peter Lifu, ya ce mai ƙarar bai nuna cewa ya sami wata illa kai tsaye daga niyyar Jonathan ta tsayawa takara ba, don haka ba shi da ikon shigar da ƙara kwata-kwata.

Kotun ta kuma ci tarar Jideobi ta naira miliyan 20 da zai ba wa Jonathan, sannan ta ci shi wata ta naira miliyan 1 da zai ba wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya (AGF).

Rahoton TheCable ya bayyana cewa hukuncin ya fito ne a zaman kotun na ranar Talata a Abuja.

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayar da umarnin dawo da damar amfani da intanet ta duniya bayan kusan kwanaki 90 a...
26/05/2026

Shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, ya bayar da umarnin dawo da damar amfani da intanet ta duniya bayan kusan kwanaki 90 ana taƙaita amfani da ita a ƙasar.

Matakin ya zo ne bayan katsewar da aka yi sakamakon yaƙin da Iran ta shiga da Amurka da Isra’ila.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito cewa har yanzu ba a bayyana yadda ko yaushe za a kammala haɗa ƙasar da intanet gaba ɗaya ba.

Rahoton ya ce miliyoyin Iraniyawa sun shafe kwanaki 87 ba tare da samun cikakkiyar damar yin amfani da intanet ta duniya ba.

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da biyan tallafin Sallah na naira 20,000 ga ma’aikatan gwamnati a jihar ...
26/05/2026

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da biyan tallafin Sallah na naira 20,000 ga ma’aikatan gwamnati a jihar da ƙananan hukumomi 44 kafin Idin Babbar Sallah.

Sanarwar da aka fitar ranar Talata ta ce tallafin zai shafi ma’aikatan da ke mataki na 01 zuwa 14 a ma’aikatu da hukumomin gwamnati.

A cewar gwamnatin jihar, an ɗauki matakin ne domin rage wa ma’aikata nauyin kasha kuɗaɗe yayin bukukuwan Sallah.

Rahoton NAN ya bayyana cewa tallafin ya zo ne bayan an biya albashin watan Mayu ga ma’aikatan jihar.

Address

Sani Abacha Bypass
Dutse
720101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when TTN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to TTN Hausa:

Shortcuts

Share