A B N HAUSA

A B N HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from A B N HAUSA, Media/News Company, Kano.

Gawarwakin mutane 7 da aka yi wa kisan gilla a unguwar Dorayi Charanachi a jihar Kano a yau Asabar. Tuni dai rundunar Ƴa...
17/01/2026

Gawarwakin mutane 7 da aka yi wa kisan gilla a unguwar Dorayi Charanachi a jihar Kano a yau Asabar.

Tuni dai rundunar Ƴansanda ta jihar Kano ta tabbatar da faruwar ibtila'in ta bankin Kakakin ta, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa

Kiyawa ya nuna alhini kan abinda ya faru tare da cin alwashin k**a waɗanda s**a aikata wannan ta'addanci.

Allah Ya yi musu rahama.

A Daina Kallonmu a Matsayin Mabarata.Wasu daga cikin al’umma nada tunanin cewa masu buƙata ta musamman ba za su iya guda...
16/01/2026

A Daina Kallonmu a Matsayin Mabarata.

Wasu daga cikin al’umma nada tunanin cewa masu buƙata ta musamman ba za su iya gudanar da rayuwarsu yadda ya k**ata ba, su a ganinsu idan mutum yanada wata nakasa to k**ata yayi ya boye kansa a cikin gida, babu abinda zai fitar da shi waje sai bara.

Ya k**ata mutane su sani, muma muna da hakkin fita domin gudanar uzurinmu na rayuwa k**ar kowa, muna da burikan da muke so mu cimma a rayuwa, don haka ba za mu bari wani ya saka mana haddi ko iyakance mana damar fitar ba.

🗣 ya k**ata masu bukata ta musamman mu tashi tsaye! mu nuna wa duniya cewa muna da damar yin duk abin da kowa zai iya.

Shin a matsayinka/ki na PWDs me aka taba yi miki ko aka yi maka don ke/kai PWDs ne wanda ya bata miki rai ko kai?




Kayan aikin sojoji daga Amurka sun iso NajeriyaKasar Amurka ta kawo  kayan aikin soja ga hukumomin tsaron Najeriya domin...
13/01/2026

Kayan aikin sojoji daga Amurka sun iso Najeriya

Kasar Amurka ta kawo kayan aikin soja ga hukumomin tsaron Najeriya domin tallafa musu a ayyukan tsaro da ake ci gaba da gudanarwa a fadin kasar.

Rundunar sojin Amurka da ke kula da nahiyar Afirka (AFRICOM) ta tabbatar da isar da kayan a ranar Talata ta hanyar wani sako da ta wallafa a shafin X.

"Masu bukata ta musamman a Kano: wa ke tsayawa tsayin daka domin kare hakkokinsu idan babu Commission?”A Jihar Kano, har...
11/01/2026

"Masu bukata ta musamman a Kano: wa ke tsayawa tsayin daka domin kare hakkokinsu idan babu Commission?”

A Jihar Kano, har yanzu babu cikakkiyar Commission ta Masu bukata ta musamman da za ta kula da muradunsu, kare hakkokinsu, da tabbatar da an shigar da su cikin manufofi da shirye-shiryen gwamnati.

Rashin wannan Commission na haifar da matsaloli da dama, ciki har da:
Rashin wakilci a matakan yanke shawara
Rashin tsari wajen aiwatar da dokoki da manufofi
Watsi da bukatun ilimi, lafiya da ayyukan yi
Wahalar samun adalci da kariya daga wariya

Idan aka kafa Commission ta Masu bukata ta musamman:
Za a samu wakilci da murya mai ƙarfi
Za a kare hakki da mutunci
Za a samar da tsari mai dorewa
Za a karfafa rayuwa mai zaman kansu da ci gaba
Masu bukata ta musamman ba sadaka suke nema ba hakki suke nema. Kano ta cancanci tsarin da zai tabbatar da hakan.

Muna kira ga Gwamnatin Jihar Kano da Majalisar Dokoki su gaggauta kafa Commission ta Masu bukata ta musamman.
👉 Ku yi comment, kuyi share na wannan sakon, domin a ji muryar masu bukata ta musamman.







Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya tashi daga Najeriya zuwa ƙasar ...
11/01/2026

Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya tashi daga Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya a wata ziyarar aiki.

A cewar wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Ahmad Mu’azu, ya fitar, ziyarar na da nufin kammala shirye-shiryen ƙarshe dangane da aikin Hajjin shekarar 2026, bisa jadawalin ayyuka da aka riga aka amince da su.

Sanarwar ta bayyana cewa ma’aikatan ofishin NAHCON na shiyyar Kano ne s**a raka shugaban hukumar zuwa filin jirgin sama, ƙarƙashin jagorancin kodinetan shiyyar, Malam Umar Kalgo.

Ziyarar ta nuna ƙudirin hukumar NAHCON na fara shirye-shiryen aikin Hajji tun da wuri, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da hukumomin Saudiyya, domin tabbatar da nasarar aikin Hajji ga al’ummar Najeriya.

08/01/2026

"Kar ka taɓa raina mai bukata ta musamman, ka saurare su farko"

Masu bukata ta musamman ba mutane ne da za a raina ba, mutane ne da ke da murya, tunani da ƙarfi.
Sau da yawa ana kallon su k**ar ba za su iya cimma buri ba, amma wannan bidiyon yana nuna gaskiyar lamarin.

Lokacin da ka ba su goyon baya da dama, za ka ga cewa nakasa ba ta hana nasara.
A One Life Initiative, muna dagewa wajen tabbatar da cewa muryar masu bukata ta musamman tana fitowa fili, ba tare da tsangwama ko raini ba.

Ka tsaya ka saurare su, domin wani lokaci abin da kake kira rauni shi ne ainihin ƙarfi.
Ka kalla bidiyon har ƙarshe
Ka share domin wasu su sami ƙarfafawa
Ka rubuta ra’ayinka a comment


Kungiyar tsofaffin daliban ZAURA BABBA (ZOBA – Aji na 2008) ta gudanar da taron bankwana domin karrama tsofaffin shugaba...
07/01/2026

Kungiyar tsofaffin daliban ZAURA BABBA (ZOBA – Aji na 2008) ta gudanar da taron bankwana domin karrama tsofaffin shugabanninta, bayan kammala wa’adin mulkinsu.

A yayin taron, tsohon shugaban ƙungiyar, Ashiru Adamu Abdullahi, ya bayyana manyan ci gaban da ƙungiyar ta samu a tsawon shekaru goma da ya shafe yana shugabanci. Daga cikin nasarorin da ya ambata akwai ƙarfafa haɗin kai a tsakanin ’yan ƙungiya, yin rijistar ƙungiyar bisa doka, da kuma gina allon bango na tile a cikin makarantar ZAURA BABBA, tare da wasu ayyukan alheri da s**a amfanar da makarantar.

Shi ma Principal na makarantar ZAURA BABBA, M. Idris Yau Ahmad, ya yabawa ƙungiyar bisa gudummawar da ta bayar, inda ya ce ayyukan da s**a yi sun dace kuma sun ƙara ɗaga martaba da darajar makarantar.

A nasa bangaren, Mataimakin Principal, M. Ashiru Usman Bello, ya bayyana cewa ƙungiyar ZOBA ta aji na 2008 ta bayar da gudummawa mai yawa, musamman gina allon bango na tile da kuma ziyarar da suke kaiwa makaranta domin jin matsalolinta. Ya kuma yi kira ga sabbin shugabannin da za su karɓi ragamar jagoranci da su yi koyi da kyawawan ayyukan shugabannin da s**a gabata.

Kotu ta yanke hukunci, tsohon Minista ya samu beli!Alƙali mai shari’a Justice Emeka Nwite na Federal High Court, Abuja, ...
07/01/2026

Kotu ta yanke hukunci, tsohon Minista ya samu beli!

Alƙali mai shari’a Justice Emeka Nwite na Federal High Court, Abuja, ya bayar da beli ga tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami, SAN, tare da matarsa da dansa, bisa sharuɗɗan da kotu ta gindaya.

Kamar yadda kotu ta bayyana, an amince da belin ne a kan kudin Naira miliyan dari biyar. Wannan mataki ya biyo bayan shari’ar da ake ci gaba da saurare a gaban kotun.

Lamarin ya ja hankalin jama’a, inda mutane da dama ke sa ido kan yadda shari’ar za ta kaya a gaba.

MENENE RA’AYINKU?
Shin kana ganin wannan mataki na kotu ya dace? Ku bayyana ra’ayinku a comment

’a

Masu bukata ta musamman ba matsala ba ne, rashin damar da ake basu ne matsala.Ana ƙara samun kira a Najeriya na tabbatar...
06/01/2026

Masu bukata ta musamman ba matsala ba ne, rashin damar da ake basu ne matsala.

Ana ƙara samun kira a Najeriya na tabbatar da haƙƙin masu bukata ta musamman, musamman wajen ilimi, aikin yi da kiwon lafiya. Kungiyoyi da masu fafutuka na jaddada muhimmancin samar da muhalli mai sauƙin shiga da kuma haɗa su cikin tsare-tsaren raya ƙasa.

Haka kuma, ana ƙara kira ga gwamnatoci a matakai daban-daban da su samar da muhallai masu sauƙin shiga (accessibility) a makarantu, asibitoci da ofisoshin gwamnati, tare da tabbatar da cewa muradin masu bukata ta musamman yana cikin tsare-tsaren raya ƙasa.

Masu fafutuka sun ce haɗa masu bukata ta musamman cikin al’umma ba taimako ba ne kawai, haƙƙi ne na ɗan Adam, kuma hakan na taimakawa wajen gina al’umma mai adalci da daidaito.



Ƙungiyar Mata ’Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ) shiyyar Kudu maso Kudu ta yi kira ga gwamnatoci da su ɗauki matakan gaggaw...
05/01/2026

Ƙungiyar Mata ’Yan Jarida ta Najeriya (NAWOJ) shiyyar Kudu maso Kudu ta yi kira ga gwamnatoci da su ɗauki matakan gaggawa domin rage wahalhalun da masu lalurar gani, musamman mata da ’yan mata, ke fuskanta a kasar nan. Ƙungiyar ta bukaci a ƙara samar da takardar Braille a wuraren jama’a, tare da horar da malamai da ma’aikata yadda zasu yi amfani da takardun wajen isar da sako ga masu lalurar gani.

NAWOJ ta bayyana hakan ne a jiya lahadi yayin bikin Ranar Braille ta Duniya 2026, tana mai jaddada cewa haɗa PWDs ba cikin dukkanin al'amuran al'umma ba alfarma ba ce, adalci ne, kuma dole ne a aiwatar da dokokin masu bukata ta musamman da aikace domin tabbatar da daidaito, bada damad samun ilimi da samun cikakkiyar damar shiga cikin al’umma ga PWDs.






Za'ayi Jana'izar 'Yar Jarida ma'aikaciyar gidan Radio Kano Hajiya Atine Usman Mai Mota da karfe 12 na rana, a unguwar Za...
05/01/2026

Za'ayi Jana'izar 'Yar Jarida ma'aikaciyar gidan Radio Kano Hajiya Atine Usman Mai Mota da karfe 12 na rana, a unguwar Zango Lungun Dan Ķuttuki.

Hajiya Atine Mai Mota ta rasu a daren Lahdi. Allah yaji kanta ya gafarta mata.

RANAR BRAILLE TA DUNIYA – 4 GA JANAIRU, 2026A yau ake bikin Ranar Braille ta Duniya, rana ta musamman da ke tunatar da m...
04/01/2026

RANAR BRAILLE TA DUNIYA – 4 GA JANAIRU, 2026

A yau ake bikin Ranar Braille ta Duniya, rana ta musamman da ke tunatar da mu muhimmancin Braille wajen bai wa masu larurar gani damar samun ilimi, bayanai da cikakkiyar damar shiga cikin al’umma.

Braille ba kawai rubutu ba ne, hanya ce ta ’yanci, ilimi da cin gashin kai ga masu raunin gani.

💙 ONE LIFE INITIATIVE na jaddada kiran a samar da dama iri ɗaya ga kowa, ba tare da nuna wariya ba.

Braille: Hakkinsu ne, ba alfarma ba.




Address

Kano
08166145431

Telephone

+2348166145431

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when A B N HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to A B N HAUSA:

Share