
21/09/2025
Jagoran Ƙasa na jam’iyyar NNPP, Mai Girma Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, PhD, FNSE, ya karɓi gungun mutane da s**a sauya sheƙa daga jam’iyyun APC da PDP zuwa NNPP daga ƙananan hukumomin Kiru, Sumaila, Tudun Wada da Garko na Jihar Kano.
Wannan taro ya gudana a gidan Jagoran dake titin Miller Road, inda dubban mambobi daga manyan jam’iyyun adawa s**a bayyana amincewarsu da jagorancin Sanata Kwankwaso tare da jaddada aniyarsu ta yin aiki tukuru wajen ƙarfafa NNPP a matakan ƙananan hukumomi da yankunan karkara.
A yayin tarbar, Mai Girma Sanata Kwankwaso ya yaba wa waɗanda s**a sauya sheƙar bisa kwarin guiwar da s**a nuna, tare da basu tabbacin cewa NNPP jam’iyya ce ta talakawa wacce ke shimfiɗa manufofin ci gaba, ilimi, lafiya, da bunƙasa matasa da mata. Ya jaddada cewa ƙofar jam’iyyar a buɗe take ga duk wanda ke son sauyin gaskiya a Kano da Najeriya baki ɗaya.
Shugabannin waɗannan sabbin mambobi sun bayyana cewa sun yanke shawarar barin jam’iyyun da s**a fito ne sakamakon rashin adalci da kuma gaza sauke nauyin da aka ɗora musu wajen ciyar da al’umma gaba. Sun ce abin da s**a gani a cikin NNPP shi ne gaskiya, adalci, da kulawa da talakawa.
Wannan sauya sheƙar ya ƙara ɗaga martabar jam’iyyar a Kano, inda ake ganin hakan zai ƙarfafa ginshikin NNPP a zaben da ke tafe, musamman kasancewar waɗannan ƙananan hukumomi na daga cikin manyan cibiyoyin siyasa a jihar.