07/05/2026
Gwamnan Jihar Kano Alh Abba Kabir Yusuf Ya Mayar da Fom ɗin Takarar Gwamna Karo na Biyu a APC
Gwamnan Jihar Kano, Alh Abba Kabir Yusuf, ya mayar da fom ɗinsa na neman takarar gwamnan jihar karo na biyu ga uwar jam’iyyar APC, a wani gagarumin taro da ya ja hankalin dubban magoya baya, shugabannin jam’iyya da manyan masu ruwa da tsaki a harkokin siyasar Kano.
Taron wanda ya gudana cikin yanayi na farin ciki da nuna ƙarfin siyasa, ya samu halartar jiga-jigan APC daga matakai daban-daban, inda s**a bayyana cikakken goyon bayansu ga gwamnan domin ya ci gaba da jagorantar jihar Kano a zaɓen shekarar 2027.
A yayin da yake mika fom ɗin nasa, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa matakin sake neman kujerar gwamna ya samo asali ne daga irin goyon baya da amincewar da al’ummar Kano s**a nuna masa, tare da buƙatar ci gaba da ayyukan raya jihar da gwamnatinsa ta fara aiwatarwa.
Ya ce gwamnatin sa ta mayar da hankali wajen bunƙasa ilimi, lafiya, samar da ababen more rayuwa, tallafawa matasa da mata, da kuma inganta walwalar al’umma baki ɗaya. Ya ƙara da cewa har yanzu akwai manyan tsare-tsare da gwamnatin sa ke son kammalawa domin ɗora jihar Kano a sahun gaba wajen ci gaba da bunƙasa tattalin arziki da zaman lafiya.
Gwamnan Jihar Kano ya kuma yaba da irin haɗin kai da biyayya da shugabannin jam’iyyar APC suke nunawa, yana mai cewa wannan haɗin kai shi ne ginshiƙin nasarar jam’iyyar a jihar Kano. Haka kuma ya gode wa magoya baya bisa irin yadda s**a cika wajen taron domin nuna ƙauna da goyon baya ga takararsa.
Wasu daga cikin shugabannin APC da s**a yi jawabi a wajen taron sun bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin shugaba mai kishin al’umma da ci gaban jihar Kano. Sun ce ayyukan da ya gudanar a fannoni daban-daban sun ƙara tabbatar da cewa ya cancanci sake samun damar jagorantar jihar a karo na biyu.
Taron ya kasance cikin tsari da walwala, yayin da aka rika kaɗe-kaɗe da rera taken jam’iyya, tare da nuna alamun haɗin kai da ƙarfin APC a Kano gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Dubban magoya bayan jam’iyyar da s**a halarci taron sun bayyana ƙwarin gwiwarsu cewa jam’iyyar za ta sake samun nasara tare da ci gaba da riƙe madafun iko a jihar Kano.