16/08/2025
Jam'iyyar APC a jihar Kano Tayi Allah ya isa, tare da yin Allah Wadai da Sak**akon Zaɓen Cike Gurbi na jihar Kano, inda ta ɓukaci INEC ta Soke Zaɓen Cike Gurbi da ake Gudanarwa a jihar Kano
Cikin wata takarda da Sakataren yaɗa labaran jam'iyyar na kasa Felix Morka, CON ya sanyawa hannu yace akwai tashin hankali mai tsanani da tada zaune-tsaye daga ‘yan daba dauke da mak**ai a rumfunan zabe da dama a mazabun Shanono, Bagwai da Ghari, wanda hakan ya lalata sahihancin zaben.
Ya kara da cewa Rahotanni daga kananan hukumomin Shanono da Bagwai da mazabar Ghari sun tabbatar da cewa, masu kada kuri’a sun gudu daga rumfunan zabe sak**akon tashin hankali, lamarin da ma’aikatan tsaro da aka tura wajen gudanar da aikin s**a kasa shawo kansa.
APC ta kara da cewa ci gaba da gudanar da zaben Shanono/Bagwai da na Ghari a irin wannan yanayi na tada zaune-tsaye, barazana da tsoratar da masu kada kuri’a da karfin tsiya, ya saba da tsarin dimokaradiyya na gudanar da zabe cikin ’yanci, gaskiya da lumana.
Ta ce hakan zai kafa mummunan tarihi na rashin adalci a harkar zabe, wanda kuma za a dauka a matsayin babbar barna da rashin gaskiya a tsarin zabubbuka.