APA Hausa

APA Hausa African Press Associated (APA)

For Advertising your Business

Contact us through WhatsApp on this
+2348117479303
(2)

A karon farko tun bayan yaƙin duniya na biyu, yanzu cikin daren nan Amurka ta yi gwajin makamin Nukiliya mai tafiya wata...
06/11/2025

A karon farko tun bayan yaƙin duniya na biyu, yanzu cikin daren nan Amurka ta yi gwajin makamin Nukiliya mai tafiya wata nahiya mai ketare Duniya ba, Lucas Tomlinson, dan jaridar Fox News ne ya ruwaito bisa bayanin rundunar sojin saman Amurka.

Musulunci ya samu babbar ɗaukaka a Duniya, inda a karon farko a tarihi aka zaɓi Musulmi a matsayin magajin garin birnin ...
05/11/2025

Musulunci ya samu babbar ɗaukaka a Duniya, inda a karon farko a tarihi aka zaɓi Musulmi a matsayin magajin garin birnin NewYork na Amurka.

Musulmi na farko Mamdani ya yi nasara a kan Andrew Cuomo na Indifenda da kuma Curtis Sliwa na jam'iyyar Republican wanda ake gani shi ne zai zo na uku a zaɓen.

Nifa ina ganin nafi kowa jijji da kai a faɗin Duniya, babu wanda ya kaini girman kai, kuma ba zan iya cigaba da bayar da...
04/11/2025

Nifa ina ganin nafi kowa jijji da kai a faɗin Duniya, babu wanda ya kaini girman kai, kuma ba zan iya cigaba da bayar da tallafin kyautar abinci ga talakawan Amurka ba, ai ba kyauta kuka zaɓeni ba da kuɗi na naci zaɓen—Trump

SANARWA:Babban daraktan yaɗa labarai da sadarwa, na kamfanin African Press Associated (APA).Salisu Saminu, na farin ciki...
04/11/2025

SANARWA:

Babban daraktan yaɗa labarai da sadarwa, na kamfanin African Press Associated (APA).

Salisu Saminu, na farin cikin gayyatar ƴan'uwa da abokan arziki zuwa wajen ɗaurin aurensa, da za ayi insha Allahu a ranar Juma'a 07/11/2025.

Muna fatan Allah ya tabbatar da alheri ya bada zuri'a ta gari ameen.

Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci kan tsaro a Najeriya, inda ya bawa shugabannin rundunonin tsaron ƙasar da gwamnonin jihohi ...
04/11/2025

Tinubu ya kafa dokar ta ɓaci kan tsaro a Najeriya, inda ya bawa shugabannin rundunonin tsaron ƙasar da gwamnonin jihohi 36 waɗanda sune Chief Security a jihohi, wa'adin kwana 30 su kawo masa rahoton yin nasarar kawar da dukkannin ƴan ta'adda a faɗin ƙasar.

Farkar Lamine Yamal, Nicole ta koma wajen Kylian Mbappe bayan sun rabu da Yamal.
04/11/2025

Farkar Lamine Yamal, Nicole ta koma wajen Kylian Mbappe bayan sun rabu da Yamal.

Gwamnan Jihar Adamawa Ya Naɗa Sabon Shugaban Kwalejin Aikin Noma Ta GanyeGwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya...
04/11/2025

Gwamnan Jihar Adamawa Ya Naɗa Sabon Shugaban Kwalejin Aikin Noma Ta Ganye

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya amince da naɗin Aminu Kardu Tsigiya a matsayin sabonshugaba, Provost na Kwalejin Noma, Kimiyya da Fasaha ta Ganye, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

Naɗin ya biyo bayan shawarar da Majalisar Gudanarwar Kwalejin ta bayar, bayan da Tsigiya ya fi kowa nasara a jarrabawar da aka gudanar don neman wannan muƙami.

Haka kuma, Gwamnan ya amince da naɗin Yusuf Haman Adama a matsayin Registrar na kwalejin, da Mustapha Baba Nasir a matsayin Librarian. Waɗannan naɗe-naɗe suna fara aiki nan take.

Yayin da yake taya sabbin shugabannin murna, Gwamna Fintiri ya buƙace su da su jagoranci cibiyar da hikima, gaskiya, da jajircewa, tare da yin aiki kafaɗa da kafaɗa don ci gaban kwalejin.

Ya kuma umurci Provost ɗin da ya haɗa kai da sauran mambobin gudanarwa domin inganta ilimi da basirar aiki ga ɗalibai, tare da tabbatar da cewa kwalejin ta ci gaba da kasancewa cibiyar haɓaka harkar noma a jihar da ma wajen ta.

Bugu da ƙari, Gwamnan ya shawarci sabbin shugabannin da su mayar da hankali kan ƙirƙire-ƙirƙire, bincike da hulɗa da al’umma, domin inganta martabar kwalejin da ci gaban jihar gaba ɗaya.

China tace tana tare da Najeriya 100% ,Nigeria abokiyar mu ce kuma duk wanda yake kokarin amfani da addini domin lalata ...
04/11/2025

China tace tana tare da Najeriya 100% ,Nigeria abokiyar mu ce kuma duk wanda yake kokarin amfani da addini domin lalata kasar wasu ba zamu dai dai ta dashi ba—Mr Xi Jin-ping

Dan majalisar Amurka Riley Moore ya nemi Trump da ya soke Visar fitaccen ɗan siyasar Najeriya Kwankwaso Ko a jiya ma dai...
04/11/2025

Dan majalisar Amurka Riley Moore ya nemi Trump da ya soke Visar fitaccen ɗan siyasar Najeriya Kwankwaso

Ko a jiya ma dai sai da ɗan majalisar dokokin na Amurka, Riley Moore, wanda ya dade yana cikin masu yin kira kan batun “kisan kiyashi ga Kiristoci” a Najeriya, ya kai farmaki kan tsohon gwamnan Jihar Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso, a ranar Litinin.

Moore ya bayyana cewa Kwankwaso yana daga cikin manyan ‘yan siyasar da s**a yi shiru kan abin da ya kira cin zarafin Kiristoci a Arewacin Najeriya, yana mai cewa “irin wannan shiru yana nufin amincewa da aikata laifi.”

Wannan zargi ya jawo cece-kuce a shafukan sada zumunta, inda wasu ke ganin Moore na kokarin haddasa rikici tsakanin addinai a Najeriya, yayin da wasu kuma ke ganin lokaci ya yi da shugabanni za su fadi gaskiya game da matsalar tsaron da ke afkuwa a Najeriya.

Har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto Ba mu samu martanin kai tsaye daga bangaren tsohon gwamnan ba kuma duk kokarin da muka yi na ganawa da shi kai tsaye ya ci tura.

Yanzu a iya cewa Lamarin na kara zafafa rikicin magana tsakanin ‘yan siyasa da shugabannin kasashen biyu wato Najeriya da Amurka.

Gaskiyane na karɓi addinin Musulunci kuma ba zan fita ba.Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da...
04/11/2025

Gaskiyane na karɓi addinin Musulunci kuma ba zan fita ba.

Shahararren mawakin Najeriya, Damini Ogulu wanda aka fi sani da 'Burna Boy', ya bayyana cewa ya karɓi Musulunci bayan dogon lokaci yana nazari da neman gaskiya game da addini da manufar rayuwa.

A cewar Burna Boy, babu wanda ya tilasta masa sauya addini, sai dai ya samu nutsuwa da fahimtar gaskiya bayan zurfin tunani.

“Na binciki addinai da yawa, ina tambayar kaina menene gaskiya game da rayuwa. A ƙarshe zuciyata ta samu natsuwa da Musulunci, don haka na karɓe shi,” in ji shi.

Mawakin ya ƙara da cewa yana mutunta dukkan addinai, kuma yana kira ga jama’a su zauna lafiya da juna, su guji rarrabuwa saboda addini ko ƙabila.
Boy, wanda ya yi fice da wakoki kamar “Last Last” da “City Boys”, ya ce burinsa shi ne ya rayu cikin gaskiya da mutunci, ba wai don sunan addini kawai ba.

Daga Sawaba Fm

Idan Zan Fada Maka Yadda Muke Amfana Da Arewacin Nijeriya, Za Ka So Ka Bar Lagos Ka Koma Kano Da Zama, Cewar 'Yar Kabiĺa...
04/11/2025

Idan Zan Fada Maka Yadda Muke Amfana Da Arewacin Nijeriya, Za Ka So Ka Bar Lagos Ka Koma Kano Da Zama, Cewar 'Yar Kabiĺar Ibo, Chidimma Precious

Manyan jami'an rundunar sojin Iran sun gudanar da taro don tunkarar barazanar Trump.
04/11/2025

Manyan jami'an rundunar sojin Iran sun gudanar da taro don tunkarar barazanar Trump.

Address

Kano
880000

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when APA Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to APA Hausa:

Share