JK MEDIA

JK MEDIA LABARAI DA RAHOTANNI GAMI DA NISHADANTARWA

Sabbin hotunan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara a gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja.An ɗauki hotunan lokacin z...
30/11/2025

Sabbin hotunan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara a gidan yarin Kuje da ke birnin tarayya Abuja.

An ɗauki hotunan lokacin ziyarar ɗan gwagwarmaya Sowore tare da rakiyyar Comrade Yahya M Abdullahi, Brister Hamza Dantani da Alhaji Sani Ahamed Zangina.

Wane fata zaku yi masa?

NDLEA sun k**a wani sojan sama Anas Muhammed Fakai ɗauke da mak**aiA cewarsa, wannan mak**an zai kaiwa wani jami'in ɗan ...
27/11/2025

NDLEA sun k**a wani sojan sama Anas Muhammed Fakai ɗauke da mak**ai

A cewarsa, wannan mak**an zai kaiwa wani jami'in ɗan sanda ne mai suna "Muhammed Auwal Haliru" a birnin Abuja.

Allah ta'ala ya ƙara tona asirin duk wani mai hannu acikin matsalar najeriya.

04/11/2025

Yanzu-Yanzu: Sanata Natasha ta zargi shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da bayar da umurnin a kwace mata fasfo domin hana ta fita waje.

30/10/2025
DA DUDUMI:Wata mata mazauniyar Yakasai Gundutse a Karamar Hukumar Kura tana fuskantar zargi kan aurar da wata yar tsintu...
25/10/2025

DA DUDUMI:
Wata mata mazauniyar Yakasai Gundutse a Karamar Hukumar Kura tana fuskantar zargi kan aurar da wata yar tsintuwa ba tare da bincike ba, tare da haɗin gwiwar Mai unguwar Dalili.
Kotun Shari’ar Musulunci ta Kura, ƙarƙashin Malam Ibrahim Isa Usman, ta umarci a kawo su kotu tun watanni biyu da s**a wuce, amma ba su bayyana ba.
Yanzu kotun ta sake aika musu da gayyata don su bayyana a ranar 29 ga Oktoba, 2025, domin ci gaba da shari’a.
Daga Ɗantala Uba Nuhu kura

23/10/2025

Ba da son raina na amince da auren ‘Yar Guda ba, kawai tsoron hukuncin da za a yanke min ne ya sa na amince ~ Ashiru Mai Wushirya

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, kuma jagoran jam'iyyar NNPP, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya yi dirar mikiya a ...
23/10/2025

Ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, kuma jagoran jam'iyyar NNPP, Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso ya yi dirar mikiya a kan mutanen da ya kira 'yan jari-hujjan da s**a gudu Abuja, babban birnin ƙasar, s**a bar talakawa a cikin wahala.

A cewarsa, "Allah ba zai bar su ba".

Ya zargi 'yan siyasar ƙasar da mantawa da talakawa, inda ya ce suna can "sun samu manya-manyan gidaje sun zauna a ciki. "Waɗansu 'yan majalisa ne, waɗansu sanatoci ne, waɗansu ministoci ne".

23/10/2025

‘Yan sanda a Yobe sun k**a sakataren APC na Karasuwa bisa zargin kisan wata mata, inda ake ci gaba da bincike don gurfanar da shi a kotu.

KIMANIN WATA 17 KENAN DAGA ƊANIN BUBUR BAI DAWO BA.  Wani Matashi Iliyasu Mustafa  Dan-Asalin Garin Ana Dariya Dake 'Kar...
19/10/2025

KIMANIN WATA 17 KENAN DAGA ƊANIN BUBUR BAI DAWO BA.

Wani Matashi Iliyasu Mustafa Dan-Asalin Garin Ana Dariya Dake 'Karamar Hukumar Bebeji a Jahar Kano, Ya yi awon gaba da baburin ɗan uwansa daga aran baburdin. Hakan yasa aka mika shi gaban kotu
Tuni Ya Amsa Laifin Yiwa Dan-Uwansa Wayo Cikin Da Bara Wato Cin Amana
Inda Ya Rokeshi Da Dan Allah Ya Taimaka Ya Bashi Aron Sabon Babur Zaije Ziyara Wurin Mahaifiyar sa
Inda Nan Take Dan-Uwan Nasa Ya Bashi Aron Sabon Baburin nasa. Tun Daga Wannan Lokacin Da Ya Ari Sabon Baburin Saida Ya Shafe Kimanin Watanni Goma Sha-Bakwai ( 17 ) Bai Dawo Gida ba

Sai Daga bisani Ya Dawo Garinsu Na Ana Dariya a Karamar Hukumar Ana dariya mai suna Sumul Bukwi, Batare Da Sabon Baburin ba.
Bayan Ya Fada komar Jami'an
Tsaron Yan-Sandaan Karamar Hukumar Bebeji
Maigabatar Da Kara Insifector Bashir Ala Tiga Ya Gabatar Dashi a Gaban Kotun Majistare Dake Kafin Maiyaki a Karamar Hukumar Kiru Bisa Jagorancin Maisharia Muhammd Isah
Bayan An Karanta Masa Takardar Tuhumar
Gogan Naka Nan Take Ya sa Laifinsa
Alkalin Kotun Majistare
Muhammad Isa
Yayi Masa Hukuncin
Wata Hudu Babu Zabin Tara Sai Wata Biyu Ko Zabin Tarar Naira Dubu Arbain
Sai Biyan Kudin Ranko Naira Dubu Dari Shida Da Sittin Da Biyar
Ko Shekara Biyu

Alkalin Kotun Majistaren Na Kafin Maiyaki a Karamar Hukumar Kiru

Ya Dankashi a Hanun Jamiin Gidan Ajiya Da Gyaran Hali Insifector Zakariya Abdullahi Kurmawa

Bayan Futowa Daga Kotun

Wakilinmu Dantala Uba Nuhu Kura
Ya Sami Zantawa Da
Wanda Ya Aikata Laifin Musa Ana Dariiya
Ya Kuma Bayyana Nadamarsa Ta Aikata Hakan

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when JK MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to JK MEDIA:

Share