Aliyu Lawal Ali

Aliyu Lawal Ali when you see anything wrong on our page don't feel lazy to contact us. Alhamdu lillahi.2025
(6)

This page is an Islamic page which bring you awareness about Islamic.our page will make you have incited about Islam and make you to know more about our scholars.

Addinin Musulunci ya hana murna ko jin daɗi a lokacin da wani Musulmi ya mutu.Duk wanda ke murna ko mummunar Addu'a zuwa...
14/07/2025

Addinin Musulunci ya hana murna ko jin daɗi a lokacin da wani Musulmi ya mutu.

Duk wanda ke murna ko mummunar Addu'a zuwa ga marigayi BUHARI, kada ya manta shima zai mutu, kuma watakila kafin ya mutu zai iya aikata wani babban laifi da yake so mutane su nema masa gafara a wajen Allah bayan mutuwar sa.

Ko da mutum ya yi kuskure, ko ya aikata wani laifi, Wauta ne a lokacin mutuwarsa ka zake da murna kana dariya da jin daɗi kana masa mummunar Addu'a.

Bai k**ata Musulmi yayi mummunar Addu'a ga Musulmi ɗan uwansa wanda Allah ya karɓi rayuwarsa ba.

Ya k**ata mutuwar wani ta zama babban darasi ga mai hankali ba abin murna ba.

Amma sai ka ga wasu idan wani ya mutu: Suna dariya, Suna zagi, Suna murna da mutuwar sa, musamman saboda siyasa ko wata kiyayya ta Addini da suke masa.

Kowane rai zai mutu, wanda ke jin daɗi da murna shi ma zai mutu. Kuma Allah ne ke hisabi ba Mutum ba.

Ya Allah ka tsare mu daga Wauta da duhun zuciya. Ka ba mu ladabi da tausayi. Ka sa mutuwarmu ta zama alheri a gare mu.

Naxeer Kaoje

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!Muna rokon Allah Ya yi gafara ga President Baba Muhammad Buhari.Zuciya ta yi kunc...
14/07/2025

Inna lil Laahi wa inna ilaiHi Raaji'un!
Muna rokon Allah Ya yi gafara ga President Baba Muhammad Buhari.
Zuciya ta yi kunci, ido yana zubar da hawaye. Muna bakin ciki rabuwa da Baba. Ba zamu fadi komai ba sai abun da Allah Ya yarda da shi.
Allah Ya sa Aljannar Firdaus ne makomarsa tare da sauran magabatanmu. Prof pantami

*ZANCE MAI KYAU GA DAN UWANKA* Zance mai kyau ko kace kalma mai dadi sadakace inji bakin da baya qarya, don haka kar ka ...
13/07/2025

*ZANCE MAI KYAU GA DAN UWANKA*

Zance mai kyau ko kace kalma mai dadi sadakace inji bakin da baya qarya, don haka kar ka munana lafazi ga dan uwanka koda kuwa danka ne ko matarka, baqar magana tana cusa baqin ciki a zuciyar wanda ka gaya masa, magana mai dadi tana sanya farin ciki ga wanda ka gaya masa,

Ka zama mai faranta rai ba mai baqantawa ba, koda wa'azi zakayi dan uwa zabi kalmomi na mutanta wadanda kakewa wa'azi cikin hikima da tausayawa don kai buqatarka a fahimta don a gudu tare kuma a tsira tare.

Abdul'Azeez Ibrahim Bauchi (Al-misry)

KAYI KARATUN KA NA ALLO SHEKARA 5 KO 10 WANIMA HAR 20 KAFIN SAUKA 😢KASAMU KASAUKA DAKYAR BAYAN WANNAN DAUKI BA DADI DAKA...
12/07/2025

KAYI KARATUN KA NA ALLO SHEKARA 5 KO 10 WANIMA HAR 20 KAFIN SAUKA 😢

KASAMU KASAUKA DAKYAR BAYAN WANNAN DAUKI BA DADI DAKAI TSAKANIN RAYUWA DA MUTUWA 🤔

GA RASHIN TABBAS DIN ABINCI WASUMA GA QUNTATACCEN MASAUKI GA BARA ZANAR MALAM DATA GADDAWA 💪

AMMAN BAYAN DUK KAGAMA WANNAN FAMAN KUMA WAI SEKA RASA WACCE AQIDA ZAKA DAUKA SE AQIDAR TATSINENCI ⛏️

AIKUN GA KARATU BEYI ALBARKA BA WLLH

ALLAH YATSAREMU DA LALACEWAR DAZATASA MUJEFA KANMU A WANNAN MUMMUNAR TAFIYA TA MASU QARYATA ANNABI S A W

🤲🏾🤲🏾🤲🏾 AJEEB DU A YA RAB

KASAYA KA KARANTA ZAKAYI FARIN CIKI ZAKAJI DADI.Akwai wasu Ibadun Guda Shiadai (6) Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya...
09/07/2025

KASAYA KA KARANTA ZAKAYI FARIN CIKI ZAKAJI DADI.

Akwai wasu Ibadun Guda Shiadai (6) Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace wannan Ibadun Girmar Sa basu da Iyaka Falalar Sa Basu da Karshe. Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace duk Wanda ya Lizamci wannar Ibadun ya Rabauta Duniya da Lahira.

***Na Farko Shine Kamar Haka (1)
Rak'atul Fajiri, Raka'a Biyu kafin Sallar Asbahi, Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace Rak'atul Fajiri yafi Duniya da abinda ke cikin ta.

*** Na biyu Shine Kamar Haka (2).
Duk Wanda yake Karanta Ayatul Kursiyu a ko wace Sallah Babu abun da zai hanashi Shigan Aljannah sai dai in bai mutu bah.

*** Na uku shine k**ar haka (3).
Sallar Witiri.

*** Na hudu shine k**ar haka (4).
Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace.
Duk Wanda yace Subhanallahi Wabi Hamdihi sau 100 Allah zai gafarta masa zununban SA Koda sun Kai Kunfar kogi ne .

***Na Biyar shine k**ar haka (5)
Duk Wanda ya kara ta suratul Iklasi sau 10 Allah zai Gida masa bene a Aljannah (Suratul Iklas) Kulhuwa Kenan

***Na shida shine k**ar haka (6)
Manzan Allah Sallallahu Alaihi Wa Sallam yace shin bazan Maka nuni zuwa ga Taskar Aljannah bah sai yace eh ina so ya RASULULLAH kamin nuni .

Sai yace Fadan Lahaula Wala kuwata Illa Billah .

Wannar Ibadah Guda Shaidan Nan karkayi Wasa dashi Allah mana Jagora.

Dan Allah Ka Daure kayi sharing Dan Yan Uwa Su Anfana Kai ma Kayi sadakatul Jariya.

Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum Hafizahullah

farin cikin iyaye

08/07/2025

𝕋𝕌ℕ𝔸𝕋𝔸ℝ𝕎𝔸 ⏰
Azkar ɗin safiya 📿 📖.
Rashin yin Azkar gafala ne.

Good News
07/07/2025

Good News

Waɗanda s**a fi kowa kuɗi a duniya suna faƙirai s**a tara ilimin. Alokacin da mutum ba shi da kuɗi, burin sa zai iya zam...
07/07/2025

Waɗanda s**a fi kowa kuɗi a duniya suna faƙirai s**a tara ilimin.

Alokacin da mutum ba shi da kuɗi, burin sa zai iya zama neman kuɗi da neman ilimi. Lokacin da ya samu kuɗi, burin sa ba ilimi bane, ɗaukaka ya ke nema da ƙarin yawan kuɗi.

Talauci ya na sawa a sha wahalar neman ilimi ne. Me neman ilimi da ba shi da wadata zai fi shan wahala wajen neman ilimi fiye da wanda ya ke da rufin asiri ko kuma wanda iyayensa s**a tsaya masa ko wanda ya samu tallafi.

A ɗabi'a, wanda ya ke da kuɗi ya fi wanda ba shi da shi son kuɗi don shi ya fi sanin zaƙinsu. Saboda haka, daga cikin abinda ya fi so kuma wanda ke cinye masa lokaci da tunani shi ne yadda kuɗinsa za su dauwama ko su riɓanya.

A ɗabi'a, wanda ba shi da kuɗi burin sa ya same su haka kuma a ɗabi'ar ilimi, ya na kawo arziƙi ko ɗaukakar daraja. A saboda haka, wanda ba shi da kuɗi, ya fi wanda ya ke da kuɗi son ilimi, lokacin nemansa da damar samunsa.

Wani daga lokacin da ya samu kuɗi, kowa ma rainawa ya ke hatta waɗanda su ke da ilimi ko s**a fi shi ilimi. Ya fi ganin girma da mutuncin masu kuɗi yan uwansa.

Yawan masu ilimin da ba su da arziƙi a duniya ya fi yawan masu arziƙi da su ke da ƙarancin ilimi. Haka kuma waɗanda s**a fi kowa kuɗi a duniya, ba su ne su ka fi kowa ilimi ba.

Talauci ba ya hana neman ilimi.

Badamasi Aliyu Abdullahi

Allah ya yiwa fitaccen mai yabon Annabi Muhammad SAW. Abdullahi Gano wanda akafi sani da DANGANO  mai Kasidar Saba'a ras...
06/07/2025

Allah ya yiwa fitaccen mai yabon Annabi Muhammad SAW. Abdullahi Gano wanda akafi sani da DANGANO mai Kasidar Saba'a rasuwa.

Za'ayi Jana'izarsa da misalin Karfe 2 na rana a garin Gano k**ar yadda Majalisar Sha'iran Jihar Kano ta bayyana.

MATAN DA ALLAH YA TSINE MUSU.-"Wasu daga cikin matan da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace Allah ya tsine musu...
04/07/2025

MATAN DA ALLAH YA TSINE MUSU.
-
"Wasu daga cikin matan da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam yace Allah ya tsine musu sabida wasu dabi'u da s**a kebanta dasu"
-
1. Me ƙarin gashi, da wacce ake ƙarawa.
-
2. Masu canza halittar Allah, (k**ar yin bleaching).
-
3. Masu kankare haƙora don wushirya, da wacce ake yiwa.
-
4. Masu rina gashi, (dying), da wacce ake yiwa.
-
Ya ku ƴan uwana mata, ku kiyaye aikata dukkanin abinda Allah ta'ala yayi la'anta a kansa.
-
Muhammad Umar Baballe.
Abu Amatillah.

AZUMIN TASU'A DA ASHURATASU'A: Shi ne Azumin ranar Tara ga watan Muharram, an shar'anta shi ne dan saɓawa Yahudawa, Manz...
03/07/2025

AZUMIN TASU'A DA ASHURA

TASU'A: Shi ne Azumin ranar Tara ga watan Muharram, an shar'anta shi ne dan saɓawa Yahudawa, Manzon Allãh (SAW) yana cewa, Idan Allah ya rayani zuwa shekara mai zuwa zan azumci ranan tara ga wata. - Muslim (1134)

ASHURA: Manzon Allah (SAW) Ya ce Game da Azumin ranan goma ga watan Al-Muharram (Ashura) ina kyautata tsammanin a wurin Allah da ya kankare zunuban shekarar da ta gabace shi. - Muslim (1162)

Note:
Juma'a 4th July da Asabar 5th July zai k**a 9 da 10 Al-Muharram.

Allah Ta'ala ya bamu ikon Azumta

*JAN HANKALI GARE KI YAR UWA*❝Duk abin da zai kusantar dake zuwa ga shirka ga Allah,a cikin kowacce irin nau'i na Bauta ...
03/07/2025

*JAN HANKALI GARE KI YAR UWA*

❝Duk abin da zai kusantar dake zuwa ga shirka ga Allah,a cikin kowacce irin nau'i na Bauta ki ni san ce shi.❞

Wannan shi yake nuna ke mai addini ce, kuma addinin ki zai amfane ki.

❝Kar ki yadda ace kina sallah,kina azumi,kina saka hijabi,kina karatun Alkur'ani,Amman ace kina zuwa wajen Bokaye.❞

Mallam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum Hafizahullah

Address

Kano

Telephone

+2347046156790

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Aliyu Lawal Ali posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Aliyu Lawal Ali:

Share