Alfarma Radio and Tv

Alfarma Radio and Tv Kafar Yada Labarai Mai Zaman Kanta dake gabatar da Shirye - Shirye a Shafukan Sada Zumunta. KU TUNTUBE MU A WHATSAPP TA 09162339283
(3)

Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami Na Iya Zama Magajin Kwankwaso A Siyasar Arewacin NajeriyaDaga Ahmad Bin AliTun bayan ba...
12/08/2026

Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami Na Iya Zama Magajin Kwankwaso A Siyasar Arewacin Najeriya

Daga Ahmad Bin Ali

Tun bayan bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Gwamnan Jihar Gombe da Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami ya yi, al’ummar jihohin Arewacin Najeriya, ciki har da jiharsa ta Gombe, s**a nuna amincewa da goyon bayan wannan takara tasa.

Bayan gudanar da zaɓen fidda gwani, inda Pantami ya rasa tikitin takarar Gwamnan Jihar Gombe a ƙarƙashin Jam’iyyar APC, masoya da magoya bayansa s**a fara kiraye-kirayen ya fice daga jam’iyyar zuwa wasu jam’iyyun siyasa, ciki har da ADC, NDC da PDP.

Daga bisani, Jam’iyyar PDP ta yi wa Pantami alkawarin ba shi tikitin takarar Gwamnan Jihar Gombe idan ya koma cikinta, kuma hakan ta kasance.

Kyakkyawan zato da al’umma ke yi wa Pantami da irin amincewar da yake samu na da kamanceceniya da yadda ake kallon Rabiu Musa Kwankwaso a siyasar Arewacin Najeriya.

Tasirin tafiyar Pantamiyya a tsakanin matasan Arewacin Najeriya ma na da kamanceceniya da tasirin Kwankwasiyya.

Saboda haka, wasu na ganin cewa idan wannan tasiri ya ci gaba da bunƙasa, salon siyasar Pantamiyya na iya zama babban ƙalubale ga tasirin Kwankwasiyya nan da shekaru 15 masu zuwa.

A ɓangaren tasiri a kafafen sada zumunta, bayan Kwankwaso, ana iya cewa Pantami na daga cikin ’yan siyasar Arewacin Najeriya da ke da dimbin mabiya. Hakan na ƙara masa tasiri musamman a tsakanin matasa, duk da cewa a wasu lokuta mabiyan Kwankwasiyya ma suna nuna goyon baya ga Pantami.

Yayin da zaɓen 2027 ke ƙara gabatowa, ana iya kallon nasarar Pantami a zaɓen Gwamnan Jihar Gombe a matsayin wani mataki da zai iya ƙara faɗaɗa tasirinsa a siyasar ƙasa.

Idan har ya samu nasarar zama Gwamna kuma ya ci gaba da samun irin wannan karɓuwa a tsakanin al’umma, to akwai yiwuwar a shekaru masu zuwa a fara kallon sa a matsayin ɗaya daga cikin ’yan siyasar Arewa da za su iya neman takarar Shugaban Ƙasa.

Shin kuna ganin Farfesa Isah Ali Ibrahim Pantami na iya zama magajin Rabiu Musa Kwankwaso wajen jagorantar wata sabuwar tafiyar siyasa a Arewacin Najeriya?

12/08/2026

Ku tuntube mu ta WhatsApp a 09162339283 domin bayyana ra'ayinku na siyasa kyauta.

Akwai Sharuda da Ka'idoji!

Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Tudun Wada, Sule Lawan Shuwaki, ya sanar da ficewarsa daga...
12/08/2026

Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Tudun Wada, Sule Lawan Shuwaki, ya sanar da ficewarsa daga Jam’iyyar APC zuwa PDP.

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Ismail Falgore, ne ya karanta wasiƙar ficewar Shuwaki daga APC a zaman majalisar na ranar Litinin.

A cikin wasiƙar, Shuwaki ya ce ya yanke shawarar barin APC ne bayan “nazari mai zurfi da shawarwari” da ya gudanar da abokan siyasarsa, magoya bayansa da iyalansa.

Ya gode wa shugabannin APC daga matakin mazaba zuwa na ƙasa bisa damar da s**a ba shi da goyon bayan da ya samu a lokacin da yake cikin jam’iyyar.

Sai dai ya ce ya zaɓi wata sabuwar hanyar siyasa da ta dace da ƙa’idoji da ra’ayinsa.

Bayan karanta wasiƙar, Kakakin Majalisar ya tambayi Shuwaki ko shi da kansa ne ya gabatar da wasiƙar, inda ɗan majalisar ya tabbatar da hakan. Ya kuma bayyana cewa ya koma PDP tun watanni da s**a gabata, sai dai shawarwari na siyasa s**a jinkirta sanar da hakan a hukumance.

Shuwaki ya kuma gode wa tsoffin abokan siyasarsa da magoya bayansa a Tudun Wada, yana mai kira ga al’umma da su ci gaba da kiyaye haɗin kai da kyakkyawar mu’amala duk da bambancin siyasa.

Kakakin Majalisar ya bayyana cewa an karɓi wasiƙar ficewar tun kimanin watanni biyu da s**a gabata, amma ba a karanta ta nan take ba, saboda shugabancin majalisar ya ci gaba da tattaunawa da ɗan majalisar domin tabbatar da matsayinsa.

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez.Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Portugal, Cristiano Ronaldo, ya auri ...
12/08/2026

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez.

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Portugal, Cristiano Ronaldo, ya auri abokiyar zamansa na dogon lokaci, Georgina Rodríguez, a ranar Talata.

An gudanar da bikin auren ne a garin Cascais, wani wurin yawon buɗe ido da ke Portugal, kamar yadda wakilan ɗan wasan s**a tabbatar.

Ronaldo da Georgina sun shafe shekaru suna tare, kuma suna da ’ya’ya 5 tare.

'Yan Birnin Kano Wanene Zabinku Tsakanin Tijjani Hussaini Da Nabil Sarki Aliyu Daneji?
12/08/2026

'Yan Birnin Kano Wanene Zabinku Tsakanin Tijjani Hussaini Da Nabil Sarki Aliyu Daneji?

12/08/2026

Daga ina kuke kasancewa damu?

12/08/2026

📣 TUNATARWA 📣

AZUMIN NAFILA NA GOBE (ALHAMIS)!

Yana daga cikin Sunnar Manzon Allah ﷺ yin Azumi a ranakun Alhamis da Litinin.

Manzon Allah ﷺ ya ce:
Tirmizii (747).

Manzon Allah ﷺ ya kuma ce:
Bukaarii (1896, 3257).

Wannan ba ƙaramar falala da ɗaukaka ba ce; A ce Allah ﷻ ya kira ka a gaban Mala'iku, da Mutane, da Aljanu, da sauran halittu ya yi maka irin wannan karramawar!".

Ya Allah ﷻ Ka ba mu ikon yi, kuma Ka karɓa mana baki-ɗaya. Aamiin 🤲🏻

12/08/2026

As-Salaamu Alaikum

Yau Laraba (الأربعاء), 28 ga Watan Safar (صفر), 1448 Bayan Hijrah, wanda ya yi daidai da 12 ga Watan Agusta, 2026.

Allah ﷻ Ya ce:
{Kuma waɗanda suke tara zinariya da azurfa, kuma ba sa ciyar da su a cikin hanyar Allah ﷻ; To ka yi musu bushara da wata azaba mai raɗaɗi}.
(Suratut-Taubah, 9:34).

Allah ﷻ Ya kuma ce:
{Lallai Sadaka (Zakkah) tana ga talakawa, da miskinai, da waɗanda ake aiki da su wajen karɓar ta, da waɗanda ake ƙoƙarin shawo kan Zukatan su (Zuwa ga Addinin Musulunci), da a cikin fansar bayi, da waɗanda ake bin su bashi, da a cikin hanyar Allah ﷻ, da matafiyi (Wanda guzurin sa ya ƙare); Farilla ce daga Allah ﷻ, kuma Allah ﷻ Masani ne Mai Hikima}.
(Suratut-Taubah, 9:60).

⚖️ NISABI Bisa Dinar (الدينار):
•⁠ ⁠Sadaki (Kuɗin Aure): ₦190,187.00
•⁠ ⁠Zakkah (2.5%): ₦15,215,000.00
•⁠ ⁠Diyyah (Kuɗin fansar rai): ₦760,750,000.00

Allah ﷻ Ya kuma ce:
{Lallai Sallah ta kasance wajibi a kan Mumunai a bisa lokuta ƙayyadaddu}.
(Suratun-Nisaa’i, 4:103).

🕰️ Lokutan Sallah – Kano, Najeriya:
•⁠ ⁠Asubah: 4:55 AM
•⁠ ⁠Fitowar Rana: 6:14 AM
•⁠ ⁠Azahar: 12:32 PM
•⁠ ⁠La’asar: 3:42 PM
•⁠ ⁠Magriba: 6:48 PM
•⁠ ⁠Isha’i: 7:59 PM
(Inshaa’Allah ﷻ)

Ya Allah ﷻ Ka ba mu Lafiya, da zaman Lafiya, da yalwar Arziƙi. Aamiin 🤲🏻

11/08/2026

Sako na musamman daga Shugaban hukumar Hisbah ta karamar hukumar Birnin Kano Hamidan Tanko Alasaka

Muna farin cikin gabatar muku da Amina Abubakar Hausawa a matsayin mataimakiyar shugabam sashin shirye-shirye na Alfarma...
11/08/2026

Muna farin cikin gabatar muku da Amina Abubakar Hausawa a matsayin mataimakiyar shugabam sashin shirye-shirye na Alfarma Radio and Tv.

Wane fata kuke Mata?

Address

Sani Mainagge Along Mandawari
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alfarma Radio and Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category