Alfarma Radio and Tv

Alfarma Radio and Tv Kafar Yada Labarai Mai Zaman Kanta dake gabatar da Shirye - Shirye a Shafukan Sada Zumunta. KU TUNTUBE MU A WHATSAPP TA 09162339283
(4)

10/06/2026

Tuna Baya: Yadda Gwamnan Kano Alh Abba Kabir Yusuf Yake Rantsuwar Cewa Bazai Ci Amanar Jagoran Kwankwasiyya Rabi'u Musa Kwankwaso Ba, Kuma Bazai Ci Amanar Al'ummar Kano Ba.

📷2019

10/06/2026

📣 TUNATARWA 📣

AZUMIN NAFILA NA GOBE (ALHAMIS)!

Yana daga cikin Sunnar Manzon Allah ﷺ yin Azumi a ranakun Alhamis da Litinin.

Manzon Allah ﷺ ya ce:
Tirmizii (747).

Manzon Allah ﷺ ya kuma ce:
Bukaarii (1896, 3257).

Wannan ba ƙaramar falala da ɗaukaka ba ce; A ce Allah ﷻ ya kira ka a gaban Mala'iku, da Mutane, da Aljanu, da sauran halittu ya yi maka irin wannan karramawar!".

Ya Allah ﷻ ka ba mu ikon yi, kuma ka karɓa mana baki-ɗaya. Aamiin 🤲🏻

❉ ╤╤╤╤ ✿ ╤╤╤╤ ❉           🄻🄰🅁🄰🄱🄰❉ ╧╧╧╧ ✿ ╧╧╧╧ ❉⁠ [ASHURAH SAURA KWANA: 14] ⁠ADDU'AR YAU"Ya Allah ﷻ Ina roƙon ka Afuwa da...
10/06/2026

❉ ╤╤╤╤ ✿ ╤╤╤╤ ❉
🄻🄰🅁🄰🄱🄰
❉ ╧╧╧╧ ✿ ╧╧╧╧ ❉

⁠ [ASHURAH SAURA KWANA: 14] ⁠

ADDU'AR YAU
"Ya Allah ﷻ Ina roƙon ka Afuwa da Lafiya a nan Duniya da Lahira".

HADISIN YAU
UMARNI A KAN YIN SAURI-SAURI WAJEN BINNE MAMACI; DA ZARAR AN TABBATAR DA MUTUWAR SA!

Manzon Allah ﷺ ya ce:
Muslim (1575).

Ƙarin Bayani:
Wannan Hadisin yana koyar da mu cewa a yi sauri-sauri wajen binne mamaci; Ba tare da jinkiri ba. Domin idan mamaci na-gari ne; To ana hanzarta shi ne zuwa ga Rahama da lada, idan kuma ya kasance akasin haka; To ana sauke nauyin da yake kan rayayyu ne da wuri. Wannan yana nuna mana cewa jinkirta Jana’iza ba abin so ba ne a Addinin Musulunci; Sai dai idan akwai wani dalili mai ƙarfi.
Allah ﷻ ne mafi sani.

10/06/2026

As-Salaamu Alaikum

Yau Laraba (الأربعاء), 24 ga Watan Zul-Hijjah (ذو الحجة), 1447 Bayan Hijrah, wanda ya yi daidai da 10 ga Watan Yuni, 2026.

Allah ﷻ Ya ce:
{Kuma waɗanda suke tara zinariya da azurfa, kuma ba sa ciyar da su a cikin hanyar Allah ﷻ; To ka yi musu bushara da wata azaba mai raɗaɗi}.
(Suratut-Taubah, 9:34).

Allah ﷻ Ya kuma ce:
{Lallai Sadaka (Zakkah) tana ga talakawa, da miskinai, da waɗanda ake aiki da su wajen karɓar ta, da waɗanda ake ƙoƙarin shawo kan Zukatan su (Zuwa ga Addinin Musulunci), da a cikin fansar bayi, da waɗanda ake bin su bashi, da a cikin hanyar Allah ﷻ, da matafiyi (Wanda guzurin sa ya ƙare); Farilla ce daga Allah ﷻ, kuma Allah ﷻ Masani ne Mai Hikima}.
(Suratut-Taubah, 9:60).

⚖️ NISABI Bisa Dinar (الدينار):
•⁠ ⁠Sadaki (Kuɗin Aure): ₦180,625.00
•⁠ ⁠Zakkah (2.5%): ₦14,450,000.00
•⁠ ⁠Diyyah (Kuɗin fansar rai): ₦722,500,000.00

Allah ﷻ Ya kuma ce:
{Lallai Sallah ta kasance wajibi a kan Mumunai a bisa lokuta ƙayyadaddu}.
(Suratun-Nisaa’i, 4:103).

🕰️ Lokutan Sallah – Kano, Najeriya:
•⁠ ⁠Asubah: 4:36 AM
•⁠ ⁠Fitowar Rana: 6:00 AM
•⁠ ⁠Azahar: 12:26 PM
•⁠ ⁠La’asar: 3:52 PM
•⁠ ⁠Magriba: 6:50 PM
•⁠ ⁠Isha’i: 8:06 PM
(Inshaa’Allah ﷻ)

Ya Allah ﷻ Ka ba mu Lafiya, da zaman Lafiya, da yalwar Arziƙi. Aamiin 🤲🏻

An daura auren wannan matashiya yar Shi'a mai suna Nusaiba da masoyinta akan Sadaki zai mutu a wajen kare Shi'a da Sheik...
09/06/2026

An daura auren wannan matashiya yar Shi'a mai suna Nusaiba da masoyinta akan Sadaki zai mutu a wajen kare Shi'a da Sheikh Ibrahim Al-Zakzaky (Shahada)

Matashiyar ta bayyana cewa idan har bai yi shahada ta wannan hanya ba to baza ta yafe masa Sadakin ba sai an biya ta.

"A sadda aka ce in fito da mijin Aure ko a fiddo min da shi (in fitar ko a fitar min) sai na wari mutum biyar, a cikinsu na ware uku, a cikin ukun na zaɓi ɗaya — Sayyidi Muhammad Sunusi Muhammad. Babu wata ja'inja, aka yarje min".

Sai na je na same shi na sanar da shi cewa shi ne na fitar a matsayin wanda zan aura. Na faɗa masa cewa ina jin tsoro, ina jin tsoron shiga hannun wanda zai hana ni ko ya sauya min manufa, domin ina da manufofi da burace-burace da nake son cimmawa, kuma ban san kowa kamar yadda na san shi ba.

A ranar dai Sayyidi bai ce komai ba, duk da kusan kowa ya sani, nima na sani cewa yana martaba ni, kuma nima haka. Ba iya soyayya ba, akwai shaƙuwa a tsakaninmu.

Da aka zo maganar sadaki, na ce bana son ko sisi. Aka ce a'a, ya kamata a yi sadaki. Sai na ce: "To ni, SHAHADA CE SADAKINA!"

Sai Abba ya ce: "Kamar yaya?"

Na ce: "Sadakina shi ne kar Sayyidi ya juya daga fagen da'awa, ko ya gujewa maƙiyan Allah ko da hakan zai yi sanadin shahadarsa. Idan ya yi shahada, ya biya ni sadakina. Idan kuma bai yi shahada ba, to ina binsa bashi."

Aka tambaye ni: "Me ya sa kika ce haka?"

Na amsa da cewa: "Matsoracin mutum ba shi ne nake nema ba. Ina neman jarumin sadauki ne, dodon maƙiyan Allah wanda a shirye yake ya bada ransa a kowane lokaci domin kare gaskiya da jagorancin Sayyid Zakzaky (H), kuma ba na son Sayyidi ya tuna da Ni idan ya tunƙari Shahada, dan kar in zama dalilin da zai sa ya juyo. Idan ba zai iya bada wannan sadakin ba, to ba zan iya aurensa ba."

"Sayyidi ya amince da yin shahada a matsayin sadakin da zai bayar na aurena. Duk da haka ya ce zai bada wasu kuɗaɗe domin rage hidindimun biki. Sai na ce:"

"Naira dubu ɗari uku da goma sha uku (₦313,000) su ne abin da zai bayar."

"Bisa sahhalewa da umarnin Abba Malam Muhammad Sunusi Birnin Kebbi, aka biya wannan kuɗi a matsayin abin da zai wakilci sadakin aure a zahiri, tare da yarjejeniyar shahada a matsayin sadaki na manufa".

"Bayyana wannan zai hana tarihi sauyawa. Ban ce a yi koyi da ni ba, amma wannan ne matsayata. Kuma akan wannan sharaɗin aka ɗaura mana aure".

Jirgi na 28: Jirgin Kamfanin Air Peace Ya Dawo Da Alhazai 317 Zuwa AbujaJirgin kamfanin Air Peace mai lamba AP07929 ya t...
09/06/2026

Jirgi na 28: Jirgin Kamfanin Air Peace Ya Dawo Da Alhazai 317 Zuwa Abuja

Jirgin kamfanin Air Peace mai lamba AP07929 ya tashi daga Jeddah da ke ƙasar Saudiyya zuwa Abuja da misalin ƙarfe 3:55 na yamma a ranar 09/06/2026, ɗauke da Alhazai 317.

Daga cikin fasinjojin da jirgin ya dawo da su, 316 sun fito ne daga Babban Birnin Tarayya (FCT), yayin da ɗaya ya fito daga Jihar Borno.

Da wannan jirgi, adadin Alhazan Najeriya da aka dawo da su daga Saudiyya bayan kammala aikin Hajjin 2026 ya kai 10,858, yayin da yawan jiragen da s**a yi jigilar dawowa ya kai 28.

Tsohon Gwamnan Kano Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi bakuncin ‘yan takarar NDC daga Jihar Kogi a Abuja.A ranar Litini...
09/06/2026

Tsohon Gwamnan Kano Sen. Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi bakuncin ‘yan takarar NDC daga Jihar Kogi a Abuja.

A ranar Litinin, 8 ga Yuni, 2026, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi bakuncin ‘yan takarar jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) daga Jihar Kogi a gidansa da ke Maitama, Abuja.

Ziyarar ta kasance wani ɓangare na ci gaba da tattaunawa tsakanin shugabancin jam’iyya da masu neman takara daga sassa daban-daban na ƙasar, domin ƙarfafa haɗin kai da kuma tabbatar da tsari mai inganci a cikin jam’iyyar.

A yayin ganawar, an tattauna kan batutuwan haɗin kai, da ƙarfafa jam’iyya a matakin jiha, tare da bayyana buƙatar samun jagoranci da shawarwari daga shugabancin jam’iyyar yayin shirin tunkarar zaɓe mai zuwa.

Wannan ganawa na ci gaba da nuna yadda NDC ke ƙarfafa alaƙa tsakanin shugabanni da ‘yan takara a matakai daban-daban na siyasa.

An samu tsaiko a jigilar dawowar alhazan Jihar Katsina daga Saudiyya bayan sauye-sauyen da hukumomin zirga-zirgar jirage...
09/06/2026

An samu tsaiko a jigilar dawowar alhazan Jihar Katsina daga Saudiyya bayan sauye-sauyen da hukumomin zirga-zirgar jiragen sama na ƙasar s**a yi a jadawalin tashin jirage.

Amirul Hajj na jihar, Barista Ahmad Usman El-Marzuq, ya bayyana cewa an sanar da Gwamna Dikko Umaru Raɗɗa halin da ake ciki, yana mai tabbatar da cewa ana ci gaba da samar da abinci da masauki ga alhazan ba tare da wata matsala ba.

Ya ce jinkirin ba laifin kamfanin Max Air ba ne, sai dai sakamakon sabon tsarin rabon lokutan jirage da Saudiyya ta aiwatar.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar, Alhaji Kabir Bature, ya tabbatar da cewa babu wani alhaji da za a hana abinci ko masauki.

Ya kuma yi kira ga mahajjatan da su kwantar da hankalinsu yayin da ake ci gaba da tattaunawa da hukumomin da abin ya shafa domin gaggauta dawo da su gida Najeriya.

Shettima: Dangote Da Abdussamad BUA Ba 'Yan Kano Ba Ne Domin Ba A Kano S**a Yi Arziki BaDaga Ahmad Bin Ali Mataimakin Sh...
09/06/2026

Shettima: Dangote Da Abdussamad BUA Ba 'Yan Kano Ba Ne Domin Ba A Kano S**a Yi Arziki Ba

Daga Ahmad Bin Ali

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana cewa fitattun attajiran Najeriya, Aliko Dangote da Abdussamad Isyaku Rabiu na kamfanin BUA, ba za a iya kallonsu a matsayin ‘yan Kano ba saboda ba a jihar Kano s**a gina tushen arzikin da s**a yi fice da shi ba.

Shettima ya yi wannan bayani ne yayin da yake magana kan batun asali, kasuwanci da gudummawar da manyan ‘yan kasuwa ke bayarwa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasa.

A cewarsa, duk da cewa Dangote da Abdussamad suna da alaƙa da Kano ta fuskar iyali da tarihi, manyan nasarorin kasuwancinsu da gina daulolin arziki sun samu ne a wurare daban-daban na Najeriya da ma ƙasashen waje.

Kalaman na Shettima sun haifar da muhawara a tsakanin masu bibiyar harkokin siyasa da tattalin arziki, inda wasu ke ganin ya yi nuni ne da cewa asalin mutum ba shi kaɗai ke tantance inda mutum ya fito ba, yayin da wasu ke jaddada cewa mutum na iya kasancewa ɗan wani yanki duk inda ya samu nasarar rayuwarsa.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, babu wata martani daga Aliko Dangote ko Abdussamad Isyaku Rabiu dangane da kalaman da aka danganta wa Mataimakin Shugaban Ƙasar.

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya so...
09/06/2026

Tsohon Gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya soki yadda Gwamnatin Tarayya ke tafiyar da harkokin tsaro, yana mai cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta gaza ɗaukar matakan da s**a dace domin kawo ƙarshen matsalar rashin tsaro da ke addabar sassan ƙasar nan.

A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Kwankwaso ya bayyana damuwarsa kan yadda hare-haren ’yan bindiga, garkuwa da mutane, ta’addanci da sauran laifuka ke ci gaba da ƙaruwa musamman a jihohin Zamfara, Borno, Sokoto, Katsina, Kwara da Oyo.

Ya ce ci gaba da zubar da jini da asarar rayuka a yankuna da dama na nuna cewa har yanzu gwamnati ba ta samu nasarar shawo kan matsalar tsaro ba, duk da kuɗaɗen da ake warewa fannin a kasafin kuɗin ƙasa.

Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan yadda masu aikata laifuka ke ƙara samun ƙarfin guiwa, har ma suna amfani da kafafen sada zumunta wajen yaɗa saƙonninsu da kuma yi wa jami’an tsaro ba’a.

Tsohon Ministan Tsaron ya jaddada cewa matsalar rashin tsaro ba ta kai matsayin da ba za a iya magance ta ba, yana mai cewa abin da ake buƙata shi ne jagoranci mai ƙarfi, sahihiyar niyya da kuma haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da al’umma.

Ya buƙaci gwamnatin tarayya ta gaggauta yin garambawul ga tsarin tsaron ƙasa, tare da inganta walwalar jami’an tsaro, ƙarfafa tattara bayanan sirri da bunƙasa tsarin tsaron al’umma.

Kwankwaso ya kuma yi kira da a magance tushen matsalolin rashin tsaro ta hanyar rage talauci, samar da ayyukan yi, inganta ilimi da koyar da sana’o’i ga matasa domin rage yawan masu fadawa cikin ayyukan ta’addanci da miyagun laifuka.

Address

Sani Mainagge Along Mandawari
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alfarma Radio and Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category