Alfarma Radio and Tv

Alfarma Radio and Tv Kafar Yada Labarai Mai Zaman Kanta dake gabatar da Shirye - Shirye a Shafukan Sada Zumunta.
(1)

Yayinda ake cigaba da bikin Ranar yaki da Cutar Malaria ta Duniya wadda aka Saba a Rana mak**anciyar irin ta yau 25 Apri...
25/04/2025

Yayinda ake cigaba da bikin Ranar yaki da Cutar Malaria ta Duniya wadda aka Saba a Rana mak**anciyar irin ta yau 25 Aprilu 2025 Wace Hanya kuke bi wajen kare Mahallinku daga kamuwa da wayannan cututtuka? Sannan Wace Shawara zaku bawa gwamnati akan kare jama'arta?

Shugaban ƙaramar hukumar Gagarawa, Barista Abubakar Idris Gagarawa, ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnati da Jama'a ...
23/04/2025

Shugaban ƙaramar hukumar Gagarawa, Barista Abubakar Idris Gagarawa, ya bayyana haka ne a yayin taron Gwamnati da Jama'a da aka gudanar ranar Lahadin da ta gabata a ƙaramar hukumar da yake shugabanta.

Barista Abubakar ya ce "Abu na farko da muka fara yi shine samar da feeder ta wuta wacca zata bawa cikin garin Gagarawa wuta da sauran ƙauyukan Gagarawa wanda suke ɓangaren gabas, za ta wuce har yankuna na Maigatari da kuma yankunan ƙaramar hukumar Malam Madori".

Ya ƙara da cewa "Mai girma Gwamna saboda wannan aikin da muka yi, yanzu a ƙaramar hukumar Gagarawa mun fi wata ɗaya da wani abu tunda aka yi aikin nan ba'a taɓa ɗauke wuta ba".

Shugaban ƙaramar hukumar ya bayyana hakan a matsayin nasara da s**a yi wadda yasa masu sana'oi da dama har ma da ƴan garuruwa daban-daban suna nan suna sana'oi a ƙaramar hukumar ta Gagarawa.

Lamarin ya faru ne a Unguwar Haye dake tsakanin Tokarawa da Hotoron Arewa a cikin Karamar hukumar Nassarawa, bayan an Sh...
22/04/2025

Lamarin ya faru ne a Unguwar Haye dake tsakanin Tokarawa da Hotoron Arewa a cikin Karamar hukumar Nassarawa, bayan an Share wani fegi da niyyar shimfida titin dogo na Jirgin Kasa a wajen.

Sedai bayan share wajen keda wuya sai akayi katari da wani tsohon tabo daya bushe yai k**ar sawun kafa, cikin wani faifan Bidiyo da ya karade Shafukan sada zumunta anga yadda Mutane ke tururuwar zuwa wajen da niyyar samun tabarruki daga tabon da s**ace yana k**a da sawun kafar fiyayyen Halitta inda har wasu ke diban ruwan dake daura da Wajen da niyyar samun waraka daga cututtuka tunda suna ganin wajen a Matsayin guri mai tsarki.

Bayan hukumar Hisbah ta samu labari tuni tai durar mikiya a Unguwar tareda rushe tabon k**ar yadda Mataimakin Kwamanda Sheikh Mujahiddin ya tabbatar sannan yace sun kori Mutane daga wajen.

Wakilinmu Ahmad Bin Ali ya rawaito cewa Sheikh Mujahiddin Aminuddin yace Jahilci ne irin Wannan abu tunda masu Ilimi sunsan cewa a tarihi babu inda labari ya nuna Annabi Muhammad S.A.W ya shigo yankin Nahiyar Africa ballantana Najeriya.

A Karshe yaja hankalin Mutane akan kiyaye yada labarai na karya masu alaka da Annabi Muhammad Saboda hakan kuskure ne kuma yana tauye Imani, sannan ya bukaci mutanen da s**ace sawun kafar fiyayyen Halitta ne dasu tuba ga Allah Saboda Kuskuren da s**a aikata.

Rundunar Yan Sandan Jigawa tana Sanar da daukacin Al'ummar Jihar Musamman mazauna Birnin Kudu da Kewaye cewa zata gabata...
18/04/2025

Rundunar Yan Sandan Jigawa tana Sanar da daukacin Al'ummar Jihar Musamman mazauna Birnin Kudu da Kewaye cewa zata gabatar da atisayen koyan harbi ga Sababbin Kurata.

Cikin Sanarwar da Kakakin Rundunar Yan Sandan SP Lawan Shisu Adam ya fitar yace: Kwamishinan Yan Sandan Jigawa C.P AT Abdullahi Psc. Yana sanar da ilahirin alummar Yankin Birnin Kudu da karsu tsorata a lokacin da zasu gudanar da atisayen a kauyen tsohon Kafi.

Ya kara da cewa Rundunar zata shafe kwana 23 tana gudanar da horon harbin daga gobe Asabar 19 ga watan afrilu zuwa Lahadi 11 ga watan mayu.

A Karshe ya nemi hadinkai daga mazauna wajen da atisayen zai gudana da su zama masu kauracewa gurin tareda basu dukkan goyon baya har lokacin da zasu Kammala.

Tashar Talabijin Ta Yahudawa AREWA24 a Kano Ta Naɗa Celestian Umeibi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar Ba'amurken-Yahuda...
18/04/2025

Tashar Talabijin Ta Yahudawa AREWA24 a Kano Ta Naɗa Celestian Umeibi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar

Ba'amurken-Yahudawar Tashar Talabijin ta Arewa24 a Najeriya , wacce ke jagorantar gidan talabijin na nishadantarwa da salon rayuwa a harshen Hausa, da shirye-shiryenta daga gidan talabijin na Kano, ta sanar da samun gagarumin sauyi na shugabanci.

Idan za'a iya tunawa, an kafa tashar talabijin ta Arewa24 ne a shekarar 2014; kuma tana gudanar da ayyukanta a Najeriya ba tare da izinin Hukumar Kula da Tallace-tallace ta Ƙasa (NBC), da Hukumar Kula da Tallace-tallace ta Najeriya (ARCON) ba, don kasuwancin tallace-tallace a sashen Masana'antar Talla ta Najeriya.

Mataimakin Shugaban Kamfanin na yanzu, kuma Babban Jami’in Harkokin Kasuwancin ta, Celestine Umeibe, wadda ya ke kula da harkokin tallace-tallace na kamfanin a jihar Legas, zai karɓi ragamar aiki ne daga hannun wanda ya kafa kamfanin, Shugaba Jacob Arback.

An bayyana cewa Umeibe dan Kabilar Igbo zai ci gaba da sa ido kan ayyukan sadarwa da tallace-tallace na Arewa24 ba bisa ƙa'ida ba a jihar Kano.

~Tashar Yanchi

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta k**a wani matashi dan shekara 24 mai suna Shamsu Yakubu daga karamar hukumar Dawakin Kud...
18/04/2025

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta k**a wani matashi dan shekara 24 mai suna Shamsu Yakubu daga karamar hukumar Dawakin Kudu, bisa zargin lasar duburar akuya a wani bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta.

A bidiyon, an ga Yakubu yana sanya bakinsa a duburan akuyar, tare da umartar wani ya dauke shi a bidiyo domin yada shi a intanet.

Yakubu ya amsa cewa ya aikata hakan ne don neman daukaka a kafafen sada zumunta, amma ya musanta cewa ya taba jikin akuyar. Hukumar Hisbah ta bayyana lamarin a matsayin abin kunya da sabawa koyarwar Musulunci, tare da bayar da umarnin a yi masa gwaje-gwajen kwakwalwa da na miyagun ƙwayoyi.

Hukumar ta ce za a dauki matakin doka bisa sak**akon da binciken da gwaje-gwajen za su bayyana.

Tsohuwar Jamiyyar CPC ta rabu biyu bayan tsohon ministan Buhari Abubakar Malami SAN ya yiwa su faruku Adamu Aliyu dasu M...
18/04/2025

Tsohuwar Jamiyyar CPC ta rabu biyu bayan tsohon ministan Buhari Abubakar Malami SAN ya yiwa su faruku Adamu Aliyu dasu Masari martani.

A makon da muke bankwana dashi ne Wasu daga cikin Jagorori a tsohuwar Jamiyyar CPC wadda ta narke a APC s**a gabatar da taro a Abuja da niyyar tabbatar da goyon baya ga Shugaban kasa Bola Tinubu.

Wayanda s**a halarci taron sun hada da Tanko Almakura Tsohon gwamnan Nassarawa da Aminu Bello Masari tsohon gwamnan Katsina da Malan Adamu Adamu tsohon ministan Buhari da Faruku Adamu Aliyu tsohon Dan Majalissar Tarayya a Jigawa da Sauransu.

Sedai Muhammad Bello doka me magana da yawun tsohon Minista Abubakar Malami yace Jagoranchin Jamiyyar CPC ne kadai keda ikon bayyana matsaya akan goyon bayan Tinubu ko akasin haka.

A Karshe Malami ya tabbatar da cewa babu wani labari dake da alaka da komawarsu SDP ko wata Jam'iyyar Idan da bukatar hakan sedai zuwa gaba amma a yanzu jita jita kawai ake yadawa.

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya goyi bayan ayyana dokar ta-ɓaci da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi a jihar Rivers.Da ...
18/04/2025

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya goyi bayan ayyana dokar ta-ɓaci da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya yi a jihar Rivers.

Da yake jawabi ga wasu manema labari a birnin Abuja, tsohon gwamnan na jihar Rivers ya ce so ya yi a cire gwamnan jihar Siminalayi Fubara ba dakatarwa ba.

A wani mataki da ke ci gaba da raba kan ƴan ƙasar, shugaba Tinubu ya dakatar da gwamnan Fubara tare da mataimakiyarsa, Ngozi Odu da mambobin majalisar dokokin jihar, bayan kwashe watanni ana dambarwar siyasa a jihar.

Wike ya ce matakin shugaban ƙasar ya ceto jihar daga faɗawa rikici, yana mai cewa naɗa kantoman riƙo a jihar kyakkyawan mataki ne.

~ BBC Hausa

Rashin Yadda da Kaddara shine dalilin Nasiru El-Rufa'i na fice daga APC -inji Hon. Faruku Adamu Aliyu.Fitaccen Dan Siyas...
18/04/2025

Rashin Yadda da Kaddara shine dalilin Nasiru El-Rufa'i na fice daga APC -inji Hon. Faruku Adamu Aliyu.

Fitaccen Dan Siyasa daga Jigawa kuma tsohon wakilin Birnin Kudu da Buji a Majalissar Tarayya ya bayyana haka a tattaunawar da yai da BBC hau inda yace sunan irin cin mutunchin da El-Rufa'i yayiwa dattawan Arewa harma yace babu dattijo a Arewa.

Amma kwatsam Saboda bukatar sa ta gaza biya ya fice daga APC tareda komawa SDP, dukda haka be kale APC ba yake mana bitada kulli, munsan anyimai alkawarin Minista a gwamnatin Tinubu Amma yak**ata ya gane komai daga Allah yake kuma ita siyasa haka ta gada.

Faruku Adamu ya kara da cewa koma menene ze faru sudai suna bukatar Jam'iyyar APC tayi Nasara Saboda itace Jamiyyar da suke ciki a Yanzu.

Muna tare da Tinubu dari bisa dari dukda ba'a bamu muk**ai ba -inji Hon Faruku Adamu Aliyu.Tsohon wakilin Majalissar Tar...
17/04/2025

Muna tare da Tinubu dari bisa dari dukda ba'a bamu muk**ai ba -inji Hon Faruku Adamu Aliyu.

Tsohon wakilin Majalissar Tarayya daga Jigawa ya bayyana haka yayinda yake tattauna da BBC Hausa Inda yace su Yan Asalin Jamiyyar CPC masu Biyayya ga Muhammadu Buhari babu inda zasuje koda ba'a basu mukami ba.

Yana Wannan kalamai ne a wani bayani me k**ada martani ga wasu da suke ikirarin barin APC da Sunan Yan Asalin Jamiyyar CPC.

Ya kara da cewa ko El-Rufa'i da ya fita daga CPC shikadai ya fita Jagororin CPC babu wanda ya bishi kuma k**ar yadda tsohon Shugaba Buhari yace yana APC daram to suma kafarsa kafarsu.

Bayan ankai Ruwa Rana tsakanin masu ganin Mining me Suna Paws Yan damfara ne a gobe masu Paws zasu sallami duk wayanda s...
15/04/2025

Bayan ankai Ruwa Rana tsakanin masu ganin Mining me Suna Paws Yan damfara ne a gobe masu Paws zasu sallami duk wayanda s**a bada gudunmawa wajen hako Paws.

Har yanzu Mutane da dama nada kwarin gwiwa akan Mining din Manhajar Telegram yayinda wasu ke ganin angama daga kan Notcoin da Dogs.

Sedai Wannan Mining din na Paws shine ze yi alkalanchi tsakanin wayanda s**a daina Mining da wayanda suke kan yi a Yanzu, wasu sunsha alwashin matukar Paws beyi daraja ba sun daina Mining yayinda ake Saran idan yayi daraja Mutane da dama zasuyi mi'ara koma baya su cigaba da hako Kudi a Telegram.

Menene Raayinku akan Paws???
Kuma kuna daga cikin Masu Jiran ta fashe ku kwashi Kudade ko kuma ku Yan Kallo ne???

Kwanakin Baya Yan Siyasa suna kiran Kwankwaso da Mara Jama'a (Local Champion).Meyasa Yan Siyasa ke Zawarchin Sanata Rabi...
14/04/2025

Kwanakin Baya Yan Siyasa suna kiran Kwankwaso da Mara Jama'a (Local Champion).

Meyasa Yan Siyasa ke Zawarchin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a maimakon wasu Yan Siyasar na Arewacin Nigeria dukda Suna nuna rashin Mutane da yake dashi???

Address

Sani Mainagge Along Mandawari
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alfarma Radio and Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category