18/04/2025
Tashar Talabijin Ta Yahudawa AREWA24 a Kano Ta Naɗa Celestian Umeibi A Matsayin Sabon Shugaban Hukumar
Ba'amurken-Yahudawar Tashar Talabijin ta Arewa24 a Najeriya , wacce ke jagorantar gidan talabijin na nishadantarwa da salon rayuwa a harshen Hausa, da shirye-shiryenta daga gidan talabijin na Kano, ta sanar da samun gagarumin sauyi na shugabanci.
Idan za'a iya tunawa, an kafa tashar talabijin ta Arewa24 ne a shekarar 2014; kuma tana gudanar da ayyukanta a Najeriya ba tare da izinin Hukumar Kula da Tallace-tallace ta Ƙasa (NBC), da Hukumar Kula da Tallace-tallace ta Najeriya (ARCON) ba, don kasuwancin tallace-tallace a sashen Masana'antar Talla ta Najeriya.
Mataimakin Shugaban Kamfanin na yanzu, kuma Babban Jami’in Harkokin Kasuwancin ta, Celestine Umeibe, wadda ya ke kula da harkokin tallace-tallace na kamfanin a jihar Legas, zai karɓi ragamar aiki ne daga hannun wanda ya kafa kamfanin, Shugaba Jacob Arback.
An bayyana cewa Umeibe dan Kabilar Igbo zai ci gaba da sa ido kan ayyukan sadarwa da tallace-tallace na Arewa24 ba bisa ƙa'ida ba a jihar Kano.
~Tashar Yanchi