
25/09/2025
Gwamnan Kebbi ya tabbatar wa Sarkin Yauri da tsaftace harkar hakar ma’adanai tare da samar da ayyukan yi ga matasa
Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Dr. Nasir Idris, Kauran Gwandu, ya sha alwashin tsaftace harkokin hakar ma’adanai a fadin jihar, inda ya jaddada cewa dole matasan jihar su kasance cikin aikin hakar ma’adanai na gargajiya ta hanya mai amfani da inganci.
Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a Yauri, lokacin da ya kai ziyarar girmamawa ga Sarkin Yauri, Dr. Zayyanu Abdullahi.
Gwamnan ya ce gwamnati ba za ta zauna lafiya ta bar ‘yan jihar su zama kamar bayi a cikin kasarsu ba, yana mai jaddada cewa dukkan zinariya da sauran ma’adanai Allah ne ya h**e su garesu.
Dr. Nasir Idris ya ce, *“Wannan ziyara ta zama dole saboda rikicin da ya faru a wurin hakar ma’adanan Marrarabar Yauri a Karamar Hukumar Ngaski karkashin shirin shugaban kasa na PAGMI (Presidential Artisanal Gold Mining Initiative).
“Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutum guda tare da lalata dukiyoyin gwamnati da na masu zaman kansu.
“Mun hanzarta shiga tsakani tare da dawo da zaman lafiya, kuma ba za mu yarda da rashin kunya daga kowa ba, musamman daga baki (’yan kasashen waje).”*
Gwamnan ya nuna damuwa cewa harkokin hakar ma’adanai suna da alaka da matsalolin tsaro, yana gargadi: *“Ba za mu yarda da shigar da mutane daga Mali, Nijar har ma da Tanzania ba.
“Waɗannan mutane daga kasashen makwabta na Yammacin Afirka da ma daga Gabashin Afirka suna gudanar da wadannan ayyuka.
“Wasu daga cikinsu suna cin moriyar arzikin da Allah ya h**e mana sosai, suna kuma tsoratar da al’ummomin da ke da hakkin mallakar wadannan arziki.”*
Dr. Nasir Idris, wanda ya bayar da umarnin dakatar da dukkan ayyukan hakar ma’adanan nan take, ya ce wannan matakin na dawo da tsari ne.
Ya bayyana cewa har sai an tantance dukkan ma’adinai na gargajiya tare da yin rijistar su yadda ya kamata kafin a bude ayyuka.
Gwamnan ya ce irin wannan binciken za a gudanar a dukkan wuraren hakar ma’adanan jihar.
Ya kara da cewa: *“Wannan zai tabbatar da cewa mun san mutanen da za mu dauki alhakin su idan aka samu wata matsala.
“Matasanmu da al’ummominsu dole su kasance cikin wadannan ayyuka na hakar ma’adanan.”*
A ziyarar girmamawa, Dr. Nasir Idris ya nuna karramawa ga Sarkin Yauri, wanda ya bayyana cewa ya taka muhimmiyar rawa wajen nasararsa a matsayin Gwamna da kuma ci gaban gwamnatinsa.
Gwamnan ya bayyana Sarkin a matsayin uba ga kowa, yana yabonsa a matsayin gogaggen malamin ilimi ga al’ummar jihar.
Ya ce: *“Mun yaba da addu’o’inka, goyon baya da hadin kai da kake ba ni da gwamnatina.
Za mu ci gaba da kasancewa masu biyayya da girmama kai da Masarautar Yauri.”*
Sarkin Yauri, a martaninsa, ya yaba da wannan ziyarar ta Dr. Idris wacce ya ce za ta kara tabbatar da zaman lafiya a fadin jihar, musamman a wajen hakar ma’adanan da abin ya shafa.
Dr. Abdullahi ya kuma jinjinawa Gwamnan bisa kokarinsa na ci gaba da daukaka jihar da inganta rayuwar al’ummar masarautarsa da jihar baki daya.
Sarkin ya yaba da dakatar da ayyukan hakar ma’adanan da Gwamnan ya yi, yana jaddada muhimmancin bin doka da oda.
Dr. Abdullahi ya nuna damuwa cewa mafi yawan ma’adinan da ke haddasa rikici a yankin ba su da lasisi, yana mai cewa: *“Amma sun zama masu karfi, suna dauke da makamai kuma basu bin doka.
“Suna samun goyon baya daga wasu jami’an tsaro da ‘yan siyasa, don haka rashin kunyar da suke yi ta wuce kima kuma dole a dauki mataki a kansu.”*
A lokacin wannan ziyara, Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Suru/Bagudo, Hon. Bello Abubakar Kaoje, ya samu sarautar gargajiya ta “ARDON YAURI” daga Sarkin Yauri.
Sa hannu:
Yahaya Sarki
Mai Bai wa Gwamnan Kebbi Shawara ta Musamman kan Harkokin Yada Labarai
25/9/2025
Rahoton: Abubakar Aliyu Shanga