11/06/2023
Baba Otu: Gwanin Yanka Da Kekketa Ƴan Wasa A Filin Ƙwallon Da Ba Za A Manta Da Shi Ba
Wallafawa: Jamilu Uba Adamu
Fassarawa: Yasir Kallah
Ƴan Nijeriya da dama sun manta da jerin ƴan wasan ƙwallon ƙafar da s**a taka leda a cikin shekarun 1970s da 1980s, musamman ma matasan wannan ƙarnin, sakamakon rashin tattarawa da taskance tarihin nasarorinsu da bajintarsu a wasan ƙwallon ƙafa.
A wannan ƙaramar maƙalar, na yi niyyar tunowa da wani gawurtacce kuma ƙwararren ɗan ƙwallon ƙafa da ya yi shuhura a tarihin ƙwallon ƙafar Nijeriya da na taso ina jin labarin kwarewarsa da bajintarsa a ƙwallon ƙafa, musamman ma a ɓangaren yanka da kekketa ƴan wasa.
Wannan ɗan wasan ba wani ba ne face Baba Otu Muhammad na tsohuwar tawagar ƙwallon ƙafar Raccah Rovers ta jihar Kano.
A nahiyar Afirka, musamman Nijeriya, yana da matuƙar sauƙi a manta da ƴan wasan ƙwallon ƙafar da s**a bayar da muhimmiyar gudunmawa gurin cigaban wasan har ya cimma inda yake a yanzu.
Akwai su da yawa da s**a ɓace a cikin tarihi, ko kuma ba a ba su karramawar da s**a cancanci a basu. Wasunsu ba a ma tunowa da su yayin da ake tattaunawa a kan gogaggun ƴan wasa ko lambobin da s**a buga sakamakon rashin isasshen rubutaccen tarihi a kansu.
A nahiyar Turai da ma Arewacin Afirka, akwai filayen wasanni masu yawa da wuraren zama waɗanda aka raɗa musu sunayen wasu mashahuran ƴan wasa. Akwai ma gumaka da yawa da aka gina na ƴan wasan da s**a yi bajinta domin adana tarihinsu. Irinsu sun haɗa da Kubala na Barcelona, Alfaredo Di Stefano na Real Madrid, Beckenbeur na Bayern, har zuwa George Best na Man Utd. Dukkansu an karrama su sakamakon nasarar da s**a samu da gudunmawarsu yayin da suke kan ganiyarsu a ƙwallon ƙafa.
Lokaci mai tsawo kafin a kafa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars FC, akwai wata shahararriyar ƙungiyar ƙwallon ƙafa a Kano da ta yi fice a cikin tarihin ƙwallon ƙafar Nijeriya sakamakon salon wasanta mai matuƙar birgiewa da bayar da nishaɗi. Ana kiran tawagar da Raccah Rovers.
Da farko ana kiran Raccah Rovers da Darma United. Su ne tawaga ta biyu daga Arewacin Nijeriya da s**a ci gasar ƙasa (Nigerian League) a shekarar 1978. Bayan nan kuma s**a kai zagayen na kusa da na kusa da ƙarshe (quarter final) a Kofin Zakarun Afirka a 1979, wanda kuma yake daidai da gasar Kofin Zakarun Afirka (CAF).
Wasansu da ya fi shahara shi ne wani wasan sada zumunta da s**a yi da ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Fluminense FC ta ƙasar Brazil wanda s**a buga a 1978 a Kaduna inda aka ci su da ci biyu da ɗaya (2-1). Shahararren ɗan ƙwallon ƙafa na duniya, Pele, ya buga wasan.
Baba Otu Muhammad ne ya kasance babban ɗan wasan tawagar a wannan lokacin. Gwani ne a iya yanka da wasa da ƙwallo.
Mahaifinsa ɗan ƙaramar hukumar Bebeji ne ta jihar Kano. Kasuwancin goro ne ya kai mahaifinsa ƙasar Ghana, inda kuma ya zauna a can.
A can ƙasar Ghana aka haifi Baba Otu da sauran ƴan uwansa mata guda huɗu. A can kuma ya tashi.
Alhaji Isyaku Muhammad, Babban Daraktan kamfanin Afro International Group of Companies, ne ya gano Baba Otu yayin da yake buga wa tawagar Ghana Academicals a wani wasansu da Nijeriya.
Academicals a lokacin gasa ce tsakanin makarantun sakandare na Nijeriya da na Ghana.
A lokacin Alhaji Isyaku shi ne mai ɗaukar nauyin tawagar Mighty Jets ta Jos. Hakan ya sanya ya ɗauki Baba Otu domin ya koma buga wa Mighty Jets.
Ya kasance a tawagar na tsawon ƴan shekaru. Daga baya, sakamakon wasu rigingimu na cikin gida a tawagar, Alhaji Isyaku ya janye ɗaukar nauyin da yake yi wa Mighty Jets. Hakan ya sanya dole Baba Otu ya fara neman wata tawagar ƙwallon ƙafar da ta fi wannan.
Ana haka sai labari ya isar wa Raccah Rovers. Ba tare da ɓata lokaci ba s**a aika Marigayi Anas Muhammad da Salisu Yaro (jami'in jin daɗi da walwala na Kano Pillars a yanzu) domin su neme shi kan ya zo tawagar. Da s**a same shi bai ƙi ba.
Tawagar a wancan lokacin tana ɗauke da manyan ƴan wasan ƙwallon ƙafa kamar: Iliyasu Yashin, Abdulwahab Haruna, Ado Ebenezer, Mai Yawo, Godwin Bankole, Ayiye Muhd, Grandson Abbas, Abubakar, Abubakar Ba Ka Wasa, Anas Muhammed, Kalalah, Willie Cabis, Hussaini Alibi, Felix Owolabi, Ahmed Dangogo, Akawu Ƙofar Wanbai, da Nazifi Muhammed.
Shuwagabanni da sauran jagororin tawagar sun ƙunshi: Alhaji Ma’arruf, Alhaji Tadada, Alhaji Nasidi Boka, Alhaji Musa Kallah da Alhaji Abdulmumini.
Baba Otu Muhammad na ɗaya daga cikin tawagar Nijeriya a gasar Olympic ɗin da aka buga a Montreal, Kanada a 1976. Ya kuma buga wa tawagar Nijeriya ta Green Eagles a gasar Nation Cup a Ethiopia a 1976 da kuma Ghana a 1978, inda s**a zo na uku a gasar. An zabi Baba Otu a matsayin ɗan wasan gefen dama da ya zarce kowa a 1976.
A yanzu haka akwai wasu ƴan wasan ƙwallon ƙafa a Kano da ake musu laƙabi da sunansa.
LURA: Binciken marubucin ya dogara ga tattaunawa ta waya da mutanen da binciken ya shafa waɗanda suke raye da kuma wasu bayanai a yanar gizo. Yayan marubucin, Marigayi Salahudeen Uba Adamu ya kasance masoyin tsohon ɗan ƙwallon ƙafar.
Jamilu Uba Adamu marubucin wasannin motsa jiki ne mai zaman kansa.
[email protected]