SARAUNIYA

SARAUNIYA SARAUNIYAR JARIDUN HAUSA

05/09/2025

Big shout out to my new rising fans! Muhamadu Sada

Rundunar Ƴan Sandan Kaduna Ta Aika Wa El-Rufai  Sammaci Daga Yasir Kallah Rundunar Ƴan Sandan jihar Kaduna ta gayyaci ts...
04/09/2025

Rundunar Ƴan Sandan Kaduna Ta Aika Wa El-Rufai Sammaci

Daga Yasir Kallah

Rundunar Ƴan Sandan jihar Kaduna ta gayyaci tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru El-Rufai, da kuma wasu jagororin jam'iyar ADC na jihar Kaduna.

A dangane da wata wasiƙa da Daily Trust ta yi iƙirarin gani, rundunar ta gayyace su domin amsa tambayoyi a game da zargin aikata maƙarƙashiya, tayar da zaune tsaye a cikin al'umma, ɓarna, da kuma haifar da ƙuntatawa mai muni.

Mataimakin Kwamishinan Ƴan Sanda mai kula da Sashen Binciken Laifuka (CID) na jihar, Uzairu Abdullahi ne ya sanya wa wasiƙar mai ɗauke da kwanan watan 4, ga Satumba, 2025, hannu.

Wasiƙar ta ce, "A yanzu haka wannan sashen yana bincike a kan taƙaddamar da aka ambata a sama wadda ta ƙunshi waɗannan mambobin na jam'iyyarku. Ana buƙatarka da ka taho tare da su zuwa SCID a ranar 8 ga Satumba, 2025, domin su yi bayani a kan zarge-zargen da masu ƙorafin s**a shigar a kansu.

"Mal. Nasir El-Rufa’i, Bashir Sa’idu, Jafaru Sani, Ubaidullah Mohammed, wanda ake kira da 30, Nasiru Maikano, Aminu Abita, da Ahmed Rufa’i Hussaini, mai inkiya Mikiya.”

Da jaridar ta tuntuɓi mataimakin shugaban jam'iyyar ADC na yankin Arewa Maso Yamma, Jafaru Sani, wanda shi ma sunansa yana cikin waɗanda ake neman, ya bayyana mata cewa mafi yawansu sun samu labarin gayyatar da ƴan sandan ke musu a shafukan sada zumunta.

“E, mafi yawanmu mun ga jawabin a shafukan sada zumunta," ya faɗa, inda kuma ya ƙi yin ƙara bayani a kan batun.

A satin da ya gabata ne gwamnatin jihar Kaduna da El-Rufai s**a yi musayar kalamai masu zafi a game da rikicin da ya ɓalle a lokacin wani taron jam'iyyar ADC a Kaduna.

Gwamnatin ta zargi El-Rufai da shirya makircin dagula jihar ta hanyar taƙalo rikici da furta kalaman da za su harzuƙa mutane, inda shi kuma ya musanta aikata hakan.

A wani jawabi da Kwamishinan Tsaro da Harkoki na Cikin Gida, Dakta Sulaiman Shuaibu, ya sanya wa hannu, gwamnatin ta bayyana cewa ba za ta naɗe hannu ta zuba wa El-Rufai ido ya maido da jihar cikin rikici, rarrabuwar kai, da rashin tsaro ba.

Buɗe Wa Ma'aikatan Masana'anta Wuta: Rundunar Ƴan Sanda Ta Gayyaci Shugabar Algon Daga Yasir Kallah Rundunar Ƴan Sandan ...
04/09/2025

Buɗe Wa Ma'aikatan Masana'anta Wuta: Rundunar Ƴan Sanda Ta Gayyaci Shugabar Algon

Daga Yasir Kallah

Rundunar Ƴan Sandan jihar Kano ta gayyaci shugabar ƙaramar hukumar Tudun Wada, kuma shugabar ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin jihar Kano (ALGON), Sa'adatu Salisu, kan zargin jagorantar wasu ƴan daba wajen kai farmaki a kan wasu ma'aikatan wata masana'anta da ke aiki a ƙaramar hukumar.

Jaridar DAILY NIGERIAN ta yi rahoton cewa ma'aikatan masana'antar Tasarrufi General Enterprise ne s**a shigar wa da hedkwatar ƴan sandan jihar Kano da ke Bompai ƙarar shugabar ƙaramar hukumar kan zargin bai wa wasu ƴan daba umarnin kai musu farmaki da adduna, tare da umartar odilanta da ya buɗe musu wuta, wanda kuma hakan ya jawo mutane da yawa s**a jikkata da samun rauni.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, Abdullahi Kiyawa, ya bayyana cewa rundunar ta fara bincike a kan lamarin tare da aika gayyata ga dukkan waɗanda batun ya shafa, ciki har da shugabar ƙaramar hukumar.

Kiyawa ya kuma ce, “An shigar da ƙorafi a kan shugabar Algon ɗin. An gayyaci dukkan shaidun da kuma wadda ake zargin. An kuma yi kiranye ga odilan shugabar ALGON ɗin da ya je hedkwatar ya bayar da bayani a kan abin da ya faru."

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya Daga Yasir Kallah Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi ...
26/01/2025

SERAP Ta Maka Gwamnatin Tarayya da NCC A Kotu Kan Ƙarin Kuɗin Waya

Daga Yasir Kallah

Kungiyar SERAP, mai fafutukar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya ta maka gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya, NCC, a kotu kan ƙarin kashi 50 cikin ɗari na cajin waya, saƙon tes, da data a Nijeriya, inda ta yi zargin cewa ƙarin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙasar, da tsarin doka, kuma babu hankali da adalci a ciki.

A kwanakin nan ne hukumar NCC ta amince da ƙarin kuɗin, wanda ya ɗaga cajin minti ɗaya na waya daga ₦11 zuwa ₦16.5, farashin data 1GB daga ₦287.5 zuwa ₦431.25, sannan saƙon tes na SMS daga ₦4 zuwa ₦6.

Ƙarin kuɗin ya jawo ce-ce-ku-ce da s**a mai yawa ga hukumar NCC ɗin da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu, inda ita ma ƙungiyar SERAP ta ruga kotu domin a dakatar da ƙarin.

A ƙarar mai lamba FHC/ABJ/CS/111/2025 wadda ta shigar a gaban Babbar Kotun Tarayya, SERAP ta koka a kan ƙarin kuɗin ya keta haƙƙin al'umma na ƴancin magana da samun bayanai kamar yadda kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya s**a ƙunsa.

SERAP ɗin ta roƙi kotun da ta bayyana cewa ƙarin kuɗin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da dokokin duniya na ƴancin ɗan'adam, sannan ta dakatar da aiwatar da ƙarin tare da soke shi baki ɗaya.

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno Daga Yasir Kallah Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ...
26/01/2025

Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 18 da Kwamanda Ɗaya A Borno

Daga Yasir Kallah

Aƙalla sojoji 19, ciki har da kwamanda ɗaya, ne s**a rasa ransu a sa'ilin da mayaƙan Boko Haram s**a kai musu farmaki a sansanin sojin da ke Malam-Fatori, ƙaramar hukumar Abadam ta jihar Borno.

Malam-Fatori gari ne da ke kan iyakar Nijeriya da Nijar.

Majiyoyi masu tushe sun yi rahoton cewa maharan sun kai wa bataliyar ta 149 farmakin a ranar Juma'a, 24 ga Janairun 2025.

Majiyoyin sun tabbatar da cewa ƴan ta'addan sun isa sansanin a kan manyan motoci masu bindiga, inda s**a ƙone gine-gine da motocin sojojin a lokacin farmakin.

"Sojoji masu yawa sun samu mummunan rauni yayin da har yanzu ba a ga wasu ba," wata majiya ta bayyana wa gidan talabijin ɗin Channels.

"Kwamandan bataliyar, wanda Laftanal Kanal ne, da wasu manyan hafsoshi guda biyu, ciki har da daraktan lafiyar sansanin, na cikin waɗanda aka kashe a farmakin."

Wannan farmakin ya zo baya ƴan kwanaki kaɗan da ƙungiyar Boko Haram ɗin ta kai mummunan farmaki a kan wani sansanin sojin da ke Damboa, inda ta kashe tarin sojoji da ba a gama tantance yawansu ba.

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarc...
25/01/2025

Kotu Ta Hukunta Budurwa Da Ta Saɓa Alƙawarin Kai Wa Saurayinta Ziyara

Wata kotun majistare a Ilesa, jihar Osun, ta umarci wata budurwa mai suna Rhoda Audu da ta biya saurayinta mai suna Eru Dupe Naira 150,000 a matsayin diyya sakamakon karɓar Naira 3000 da ta yi a wajensa a matsayin kuɗin motar kai masa ziyara amma daga ƙarshe ta cinye kuɗin tare da saɓa alƙawarin zuwa.

An fara samun saɓanin a lokacin da Eru Dupe ya tura wa Rhoda kuɗin motar, inda ita kuma daga baya ta kashe wayarta tare da ƙin zuwa. Ganin cewa ta damfare shi ne ya ɓata masa rai, inda kai-tsaye ya kai ƙara ofishin ƴan sandan Ayeso, su kuma ƴan sanda ba su yi ƙasa a gwiwa ba s**a je s**a kamo Rhoda sannan s**a gurfanar da ita a kotu.

Yayin gabatar da shari'ar, Eru ya gabatar wa da kotun shaida, ciki har da shaidar tura kuɗin ta waya da kuma saƙonnin WhatsApp tsakanin shi da Rhoda.

A hukuncin da ta yanke, Mai Shari'a Okogun Oludare ta umarci Rhoda da ta biya Eru Naira dubu ukunsa da kuma ƙarin Naira 100,000 ta laifin saɓa yarjejeniya, da kuma ƙarin wata Naira 50,000 a matsayin diyyar sa shi a cikin damuwa.

Kotun ta kuma jaddada cewa ta yanke hukuncin domin ya zama izina ga masu irin wannan halin cin amanar.

– Yasir Kallah

Tsohon Ministan Abuja, Jeremiah Useni, Ya Mutu Daga Yasir Kallah Allah ya yi wa tsohon ministan Birnin Tarayya, Abuja, n...
23/01/2025

Tsohon Ministan Abuja, Jeremiah Useni, Ya Mutu

Daga Yasir Kallah

Allah ya yi wa tsohon ministan Birnin Tarayya, Abuja, na lokacin mulkin Marigayi Janar Sani Abacha, Laftanal Janar Jeremiah Timbut Useni, rasuwa.

A dangane da sanarwar iyalansa, ya rasu a yau Alhamis, 23 ga Janairun 2025, bayan fama da doguwar rashin lafiya.

Gwamnan jihar Filato, Caleb Muftwang, ma ya fitar da sanarwar mutuwar tsohon ministan ta bakin daraktan yaɗa labaransa, Gyang Bere.

Gwamnan ya bayyana mutuwar Janar Useni a matsayin babban rashi ba ma ga iya iyalansa ba, har ga rundunar sojin Nijeriya, da jihar Filato, da ma ƙasar bakiɗaya.

Za A Koma Rubuta Kowace Jarrabawa A Kan Kwamfuta A Nijeriya – Minista Daga Yasir KallahGwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙu...
23/01/2025

Za A Koma Rubuta Kowace Jarrabawa A Kan Kwamfuta A Nijeriya – Minista

Daga Yasir Kallah

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta ƙudiri aniyar kawo ƙarshen rubuta kowace jarrabawa a kan takarda, inda ta ce za ta sauya zuwa rubutawa a kan na'urar kwamfuta daga shekarar 2027.

Ministan Ilimin ƙasar, Dakta Tunji Alausa ne ya bayyana hakan yayin bikin ƙaddamar da kwamitin kyautata ingancin jarrabawa a Nijeriya, wanda aka gudanar a ranar Alhamis a Abuja.

Alausa ya ce an ɗora wa kwamitin alhakin shawo kan manyan matsalolin da ɓangaren ilimi yake fuskanta a ƙasar, tare da daidaita ayyukan jarrabawa, da kuma tabbatar da gaskiya da inganci.

Ministan ya kuma jaddada ƙoƙarin gwamantin wajen magance satar amsa da ta yi yawa da kuma ƙarfafa ingancin jarrabawar ƙasar baki ɗaya.

A dangane da jawabinsa, magance satar amsa yana buƙatar mataki mai tsauri domin ba ɗalibai ba ne kawai suke aikata laifin satar amsar ba.

Ministan ya ce iyaye ma suna bayar da gudunmawarsu ta hanyar goya wa yaransu baya su yi satar amsar.

Ya kuma ce malaman makaranta, da shugabannin makaranta, da ma masu kula da jarrabawar suna da hannu a cikin yaɗuwar satar amsa a ƙasar.

Zanga-Zangar Unguwar Kurna: Yadda Ɗan Sanda Ya Harbe Salisu Player Daga Isyaku Kabir Rio "Jiya a can Ƙasan Layi faɗa ya ...
29/11/2023

Zanga-Zangar Unguwar Kurna: Yadda Ɗan Sanda Ya Harbe Salisu Player

Daga Isyaku Kabir Rio

"Jiya a can Ƙasan Layi faɗa ya rincaɓe tsakanin wasu yara har aka karya wa mutum biyu a hannu. Ana cikin rikicin ne wani yaro ya mari wata yarinya. Ganin hakan ne ya sanya yayan yarinyar ya ce Wallahi ba za su yarda ba, sai sun ɗau fansa. Shi ne ya je bakin titin Ƴan Doma Motors ya ɗauko ƴan daba domin su zo su ɗaukar wa ƙanwarsa fansa.

"Shi ne cikin daren nan ƴan daban s**a shigo domin ɗaukar wa ƙanwar abokinsu fansar marin da aka yi mata. To a dalilin haka ne aka sanar wa ƴan sanda s**a shigon cikin unguwar s**a kora yaran. To sai yaran s**a fito saman unguwar suna zage-zage, suna barazana ga mutane, suna saka mutane gudu, masu shaguna suna rufewa.

"To a daidai lokacin ne matasan unguwarmu, nan kan gadar gidan mai unguwa waɗanda suke bai wa unguwarmu tsaro s**a yi shiri domin hana waɗannan 'yan Dldaban shigowa cikin unguwar tamu su yi sata ko su ji wa mutane ciwo. A daidai lokacin matasan unguwarmu s**a tanadi duwatsu domin su ba su da makami irin na ƴan daba.

"Can muna tsaye sai muka hango mutane sun taho ana ta gudu. A daidai lokacin ne shi marigayi SALISU PLAYER ya ce min, "RIO ga su nan fa. Mu gudu, ƴan daba ne." Sai na ce masa 'wallahi ba inda za ni. Su zo mu gan su. Cikinsu babu wanda ba mu sani ba.' Ni ma na riƙe dutse a hannuna. Muna tsaye tare da ni akwai Deeni Amana. Shi kuma SALISU PLAYER sai ya gudu. Ashe bai tsira ba daga harbin tsinannen Ɗan Sanda😭😭

"Muna tsaye ayarin ya zo ya same mu. Waɗansu matasa ne da masu manyan kaya a jikinsu suna ihu ɗauke da makamai irin su katako, adda, barandami. Suna tafe suna ɗuɗɗura ashariya. Ganin haka sai su kuma waɗannan matasan masu kula da unguwa s**a sa musu jifa da duwatsun nan suna cewa ƙarya ne. Kawai a take a wurin sai na ji harbin bindiga daga cikin ƴan daban. Ashe wai ƴan sanda ne a cikinsu suna tare.

"Wallahi billahillazi ba mu ankara ba sai gani na yi a gabana an harbi ɗan uwana USMAN IG. Harsashin ya gogi hannunsa ya wuce cinyar SARKI ZILADAINI. Saii ya kara harba bindigar, shi ne ya kashe SALISU PLAYER 😭"

Falana Ya Koka A Kan Hukuncin Shari'ar Kano, Ya Ce Alƙalai Na Hukunta Masu Zaɓe A Kan Kura-Kuran Da INEC Take Yi Fassara...
03/11/2023

Falana Ya Koka A Kan Hukuncin Shari'ar Kano, Ya Ce Alƙalai Na Hukunta Masu Zaɓe A Kan Kura-Kuran Da INEC Take Yi

Fassarawa: Yasir Kallah

Babban lauyan nan mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam na Nijeriya, Femi Falana, SAN, ya koka a kan hukuncin shari'ar kotun sauraren ƙararrakin zaɓen kujerar gwamna ta jihar Kano wadda ta soke nasarar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.

Idan ba a manta ba, Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Nijeriya, INEC, ta bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaɓen kujerar gwamna ta jihar Kano da aka kaɗa a ranar 18 ga watan Maris, 2023.

Da yake jawabi a wani shiri na gidan talabijin ɗin Channels, Falana ya ce: "Bai kamata ka hukunta masu zaɓe a kan kura-kuran da INEC ta yi ba. Hakan ne abin da ya faru ba da jimawa ba a Kano, inda aka ce jami'an INEC ba su maka ƙuri'u dubu 65 ba."

Ya ƙara da faɗin cewa: "Muna kira ga alƙalai da su rungumi adalci, adalci na haƙiƙa, ta hanyar da ba za ka iya hukunta masu zaɓe a kan kura-kuran da INEC ta tafka ba."

A dangane da tsari na doka, matuƙar an ƙirga ƙuri'un sannan an bayyana wanda ya samu nasara, "Ba za ka iya ƙalubalantar ingancin takardun zaɓen ba".

"Saboda haka, ina ganin waɗannan ne wuraren da alƙalanmu ya kamata su koma baya su gyara," inji Falana.

Guguwar Juyin Mulki: Tsoro ya sa shugaban ƙasar Ruwanda ya kori manyan sojojin ƙasar A ranar Laraba, Paul Kagame, shugab...
31/08/2023

Guguwar Juyin Mulki: Tsoro ya sa shugaban ƙasar Ruwanda ya kori manyan sojojin ƙasar

A ranar Laraba, Paul Kagame, shugaban ƙasar Ruwanda, ya bayar da umarnin yi wa wasu sojojin ƙasar ritaya. Sojojin da ritayar ta shafa sun ƙunshi janar guda 95 da ƙananan sojoji 930.

Na gaba-gaba a cikin jerin sunayen sojojin shi ne Janar James Kabarebe, tsohon ministan tsaro, kuma tsohon babban hafsan tsaron ƙasar.

An wallafa sunayen sojojin da aka yi wa ritayar a kan sahihin shafin yanar gizon jami'an tsaron ƙasar a ranar Laraba.

Sanarwar ta fito bayan juyin mulkin da aka ƙaddamar a ƙasashen Niger da Gabon.

Kafin a yi masa ritaya, Janar Kabarebe ya kasance mai bai wa shugaban ƙasar shawara na musamman a kan tsaro.

Wasu kafofin yaɗa labarai na ƙasar sun bayyana cewa wasu daga cikin sojojin sun cimma shekarunsu 65 na ritaya yayin da wasunsu kuma aka zarge su a kan aikata wasu laifuka.

Address

M 31 Farin Bene, Yan Awaki Road, Unguwa Uku, Tarauni LGA
Kano
234

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when SARAUNIYA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to SARAUNIYA:

Share