HASKE Radio/Television

HASKE Radio/Television Jaridar haske domin fayyace gaskiya komai ɗacinta da kuma samun labaru da ɗumi ɗuminsu

06/09/2025

An tashi kwallo
NIGERIA 1
RWANDA 0
amma yan kallo since wasa bai kayatar ba meye ra'ayinka

Labari cikin hotuna yanda aka gudanar da taron zagayen maulidi kenan domin nuna murna da zagayowar watan haihuwar ANNABI...
06/09/2025

Labari cikin hotuna
yanda aka gudanar da taron zagayen maulidi kenan domin nuna murna da zagayowar watan haihuwar ANNABI SAWW a garin gombe.

kaman yanda kuke gani nan me martaba Sarkin Gombe ne ke tarbon dandazon masoya Annabi saw a kofar fadar sa

me zaku ce

06/09/2025

An tafi hutun rabin lokaci wasa tsakanin Nigeria Da Ruwanda babu ci ,
Shin kuna ganin wasan da Nigeria s**ayi ya kayatar daku ?

06/09/2025

Mun kori Abdulmumini jibrin kofa har abada inji shugaban NNPP na jihar Kano Dungurawa ME ZAKU CE ?

Menene ra'ayin ku game da abinda dan Bello ke yi na to asirin masu satar dunkiyar talakawa ?
05/09/2025

Menene ra'ayin ku game da abinda dan Bello ke yi na to asirin masu satar dunkiyar talakawa ?

Babu ranar da ta zowa da duniya alheri sama da ranar haihuwar MANZON ALLAH SAWWSharif Elmusaddiq
05/09/2025

Babu ranar da ta zowa da duniya alheri sama da ranar haihuwar MANZON ALLAH SAWW

Sharif Elmusaddiq

Wike Ya Kaddamar da Aikin Gaggawa Akan Titinan Garin KaruMinistan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya kaddamar da aik...
04/09/2025

Wike Ya Kaddamar da Aikin Gaggawa Akan Titinan Garin Karu

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya kaddamar da aikin gina titin Karu na gaggawa daga Karu Interchange zuwa Customs Clinic Junction, inda ya tabbatar da cewa saboda kishin Karu da Karamar Hukumar AMAC, ya yarda a haɗa da wasu hanyoyi kamar:

Customs Clinic Junction zuwa CBN Quarters Junction,

Customs Clinic Junction zuwa EFCC,

Hanyar NIA Quarters

Hanyar Primus Hospital

Ya kuma yi alƙawarin kammala su cikin watanni goma tare da sanya fitilun tituna. Ya ce wannan na daga cikin manufofin Shugaba Bola Tinubu na Ajandar Sabon Fata, wanda ke mai da hankali wajen kai ci gaban ababen more rayuwa zuwa yankunan dake wajen birnin Abuja

Wike, a yayin bikin kaddamarwa, ya jinjina wa shugaban Karamar Hukumar AMAC, Christopher Maiakalangu, da tsohon Sanata Philip Aduda, bisa irin rawar da s**a taka wajen ganin an haɗa hanyoyin cikin aikin.

Sayyada Batulu Shariff Rabi'u Usman Baba Kenan, 'Yar Gidan Shararren Mai Yabon Annabi S.A.W Marigayi Shariff Rabi'u Usma...
04/09/2025

Sayyada Batulu Shariff Rabi'u Usman Baba Kenan, 'Yar Gidan Shararren Mai Yabon Annabi S.A.W Marigayi Shariff Rabi'u Usman Baba

Wanne fata za ku yi mata?

Gwamna Zulum ya kai gwamnonin Arewa-Maso-Gabas ziyara ga Shugaba Tinubu don neman kammala manyan hanyoyi 17 da dawo da h...
04/09/2025

Gwamna Zulum ya kai gwamnonin Arewa-Maso-Gabas ziyara ga Shugaba Tinubu don neman kammala manyan hanyoyi 17 da dawo da hakar mai a Kolmani da Lake Chad.
Gwamnonin sun tattauna muhimmancin ci gaban yankin tare da nuna godiya ga kokarin tabbatar da zaman lafiya da shugaba Tinubu ke yi.
Shin wane bangare na wannan ganawar ne ya burge ka sosai?

DA ƊUMI-ƊUMI: Duk Masu Gidaje Na Zama Da   S**a Sauya Amfanin Su Zuwa Wuraren Kasuwanci Ba Tare Da Izini Ba Zasu Biya Ta...
04/09/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Duk Masu Gidaje Na Zama Da S**a Sauya Amfanin Su Zuwa Wuraren Kasuwanci Ba Tare Da Izini Ba Zasu Biya Tarar Naira miliyan 5 A Abuja

Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya (FCTA) ta sanya tara ta Naira miliyan 5 kan duk masu gidaje na zama da s**a sauya zuwa wuraren kasuwanci ba tare da izini ba a wasu manyan tituna na Abuja, ciki har da Titin Gana, Titin Gimbiya, Titin Aminu Kano, da Titin Ademola Adetokunbo.

Wannan matakin ya fito ne daga rahoton kwamitin wucin-gadi da Ministan Abuja Nyesom Wike, ya kafa a ranar 8 ga watan Agusta, 2025 domin tantance matsalolin amfani da Gidaje da kuma canjin dalilin bayar da filaye da ake yi ba bisa ka’ida ba.

Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Daraktan Kula da Ci gaban Birni, Mukhtar Galadima, ya gano cewa mafi yawan gine-ginen da ke kan titunan Gimbiya a Garki, Gana a Maitama da kuma Ademola Adetokunbo a Wuse II an sauya su zuwa otal-otal, ofisoshi da shaguna ba tare da bin ka’idar Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja ba.

Kwamitin ya ba da shawarar cewa a sake ayyana waɗannan gine-ginen zuwa wuraren kasuwanci ta hanyar biyan kuɗaɗen da s**a haɗa da:

-Bakwai da digo biyar na kimar gidajen a matsayin kuɗin canjin sauya amfani.

-Biyan sabbin kuɗaɗen mallakar fili (Statutory Right of Occupancy) bisa sabon nau’in amfani.

-Idan aka gano filin anyi kari ko an haɗe wani wuri da wani wuri ko an raba ba bisa ka’ida ba, za'a biya karin biyu cikin dari na kimar wurin

Kwamitin ya kuma bayyana cewa duk wanda bai bi wannan doka ba za a iya:

-Rufe gine-ginen,

-Rusa gini,

-Ko kuma kwace takardar mallakar fili

Hakazalika, kwamitin ya ba da shawarar cewa a soke tsofaffin takardun mallakar ƙasa sannan a sake fitar da sababbi na shekaru 99 bisa sabon yanayin amfani da ƙasa.

An kuma umarci masu filaye da ba su riga sun gina ba a cikin kwarya birni wato Central Business District da wani yanki da ake kira Phase II Sector Centres su fara gini cikin watanni uku ko kuma su fuskanci kwacewa.

Da yake karɓar rahoton, Ministan

04/09/2025

A yau ne ake sa ran zaman MAULID da aka saba duk shekara a gidajen bayin Allah domin murna da samun Annabi saww wane fata za kuyi

Da dumi-dumin su: Al'ummar garin Bimasa da ke cikin karamar hukumar Tureta sun yi kukan kura sun bi 'yan bindiga har Dab...
03/09/2025

Da dumi-dumin su: Al'ummar garin Bimasa da ke cikin karamar hukumar Tureta sun yi kukan kura sun bi 'yan bindiga har Dabarsu sun kashe na kashewa sun kwato mutanensu da akayi garkuwa da su🔥🔥

Jinjina ga al'ummar garin Bimasa da ke karamar hukumar Tureta akan namijin kokarin da su ka yi a yau, inda su ka yi kukan kura su ka farmaki 'yan bindiga har Dabarsu su ka kashe na kashewa su ka kwato al'ummar garinsu da 'yan bindigar su ka yi garkuwa da su.

Hakazalika, al'ummar garin sun zo da kafar daya daga cikin wadannan 'yan bindiga domin murna da nasarar da su ka samu.

Address

Kano

Telephone

+2349073244225

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HASKE Radio/Television posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HASKE Radio/Television:

Share

Category